GUDUN KADDARA 2

GUDUN KADDARA NA HUGUMA BOOK 2

GUDUN KADDARA NA HUGUMA BOOK 2

           “………….ya fada soyayya?,yana nufin kenan aure yake da buqatar yi?,bama fadawa soyayyar ba,wadda ya fada soyayyar da ita, yarinyar dake da gatan da ya kerewa nasa,suke da dukiya da tarin gatan da ya yiwa hankali nisan tazara,kai koda ma ace ya kammala karatunsa ya kama aiki ina yaga kudin auren hamdiyya abdu me kano?,ko yana da kudin aurenta dinmma sakayyar da zai yiwa bibi da mohmoud dake tsaye a kansa ba dare ba rana?,ya tattara ‘yan kudinsa yayi aure ba tare da sun mori komai daga gareshi na wahalar da suka sha dashi ba?. Kansa ya girgiza yana bawa kansa amsa da A’AH,ya zama dole ya sake nisanta kansa da zuciyarsa daga soyayyar hamdiyya,hatta da mohmoud sai yanzun yaga an fara tada zancan aurenshi,idan bai manta ba wancan satin yaga ya fara shigo da akwati guda uku bibi na mata wajen ajiya,ta yaya shi da yaie sanya ran zai zamesu musu sanyin idaniya ya buge da wannan zancan?. Dama bai bari ko kadan zancan hamdiyya ya fasu cikin gidansu ba saboda gudun tashin hankalin bibi da kullum tsaronta akansu ne,sai kawai ya yanke shawarar fara janye jiki daga gareta da kuma dukkan al’amuranta.

               Hakan bai haifar da komai ba saima sake dagula al’amarin da yayi,ta zube dukkan wautar dan fari da shagwabarta,kwatsam sai kawai gashi ta dauko mahaifinta tun daga Nigeria yayo tattaki ya iskeshi har cikin makaranta wai yazo sasantashi da hamdiyya,tace batasan laifin data yiwa yayanta hamidou ba yake gudunta. A ranar hankalinsa yayi matuqar tashi,ganin babban mutum me girman daraja wai yazo gareshi ban haquri?.

              Kame kame ya dinga yiwa abban don baisan ma me zaice masa ba. Daga qarshe kawao abban ya saki murmushi yana dubansu

1 Comment

  1. Gsky mun gode da gudun qaddara Allah yasaka da khairan Amma book two din bai kai qarshe ataimaka aduba Mana sauran Dan Allah

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *