Huriyya Hausa Novles

Huriyya Chapter 2

𝗣𝗮𝗴𝗲 2️⃣

Ta aje plate din hannunta da sauri ta zari tissue ta goge bakinta.

“Amma na tafi kar na yi latti”

Amma dake kokarin jefa tawul a ruwa ta ce

“Kya ji da shi, kullum ke ce uwar yan latti sai an jiraki, ga kokari ga buga latti”

Hurriya ta dauki jakarta ta makaranta da sauri ta goya tare da daukar lunch box dinta ta fice daga falon da gudu, kamar zata fadi haka ta isa bangaren Appanta sai haki take kamar wadda aka yi yakin duniya tare da ita. Hannu ta mika jikin window falon kamar yadda sauran yan mata sa’aninta da wandanda suka girmeta suke mika na su hannu suna karbar karamin hollandia da chocolate da yake raba musu, tana son karba yan’uwanta na tureta tana yin baya har sai da suka gama karba sannan ta samu karba daga gurin mahaifinta, kyautar wani abun ci da ko abun sha a kowace safiyar week days wani abu ne da ya sabawa yaransa da shi tun suna kanana.

“Na gode Appana”

Ta fada tana murmushi jindadi, shi ma murmushin yayi yana kallon kyakkyawar yarsa, mai yawan yi masa godiya da nuna masa jindadinta a duk lokacin da yayi musu kyauta komai kankantar kyautar domin haka mahaifiyarta Amma ta koyar da ita, kusan ita ce karama a cikin yayansa mata a cikin maza kuma kanenta Hamad ne karami ƴaƴansa na jini amman ya fi sauran yayansa godiya da yabawa idan yayi musu abu.

“Allah ya miki albarka Hurriya, ga ladabi ga basira”

Ta yi yar siririyar dariya mai sauti.

“Appa haka Uncle dinmu yake cewa, har da cewa yayi wai akwai wata gasar da zan sake shiga”

“Da kyau ni ma ya fada min haka, kuma yace wannan gasar ma mai tsoka ce, suna kyautata zaton idan kika yi ta daya za su dauki nauyin karatunki domin haka suke yi ma duk wadda yayi na daya, ni kuma na kara musu da cewa ko da ba su fitar da ke ba, zarar kin kallama makarantar da kike yanzu zan fitar da ke waje ki yi karatu mai kyau, duk kuwa da bana sha’awar fitar da ƴaƴa mata waje yin karatu amman ke zan fara akanki”

Ba shiri Hurriya ta bude baki tana mamakin jin furucin mahaifinta.

“Appa da gaske?”

“Da girmana zan yi karya?”

Ta saki chocolate din da hollandia ta rufe baki tana zaro ido kamar zai fado. Sai kuma ta daka tsalle ta dire.

“Appa i love you i can’t wait”

“Ki dage da karatu Allah ya taimaka ina alfahari da ke, Allah ya miki albarka”

Ya fada yana murmushi yana nuna mata alamar lokaci a hannunsa da babu agogo, sai ta duka ta dauki abun da ta zubar ta.

“Ameen ina sonka Appana, na tafi sai na dawo”

“Allah ya kiyaye,”

Ta amsa da Ameen already ta sauka entrance din tana hadawa da gudu domin yan’uwanta sun kusa isa gurin bus din dake kaisu makaranta ta maido su. Tana daf da isa ta ji an fisge chocolate din dake hannunta kamin ta juyo aka fisge madarar hollandia din dake dayan hannunta. Suna hada ido ta bata fuska ta buga kafa kasa, shi kuma ya saka dariya yana kokarin bude ledar chocolate din.

“Yaya Yassar dan Allah ka ba ni”

“Wallahi ba zan baki ba”

Ya fada kai tsaye yana mata dariyar keta, juyawa ta yi cikin yanayin damuwa ta koma bangaren Appanta wannan karon bata tsaya gurin windows din ba ta murda kofar falonsa ta shiga, sanin talkamin makaranta ne daure a kafarta sai ta fadi kasa tana rarrafe dan kar ta taka masa carpet.

“Appa Appa Appa”

Alhaji Haruna ya fito daga dakinsa da sauri jin yarsa na kiransa.

“Hurriya baki wuce ba?”

“Appa YaYa Yassar ya kwace min abun da ka ba ni, na kowa yana nan ni ya karbe nawa”

Appa yayi murmushi ya juya ya koma ciki, be dade ba ya fito rike da wani chocolate din da hollandia ya mika mata.

“Appa dan Allah ka kora Yaya Yassar daga gidanka ka ce ya tafi ya bar maka gidanka, Wallahi takura min yake yi da yawa”

Tana fada tana saka hannu biyu ta karba.

“Idan kin hadu da shi a yanzu ki fada masa na ce ya hada kayansa ya bar min gidana, saboda ya cika takuraki ke da gidan Appanki”

“Appana na gode, zan fada masa haka a yanzu kuwa”

Cikin shagwaba da jindadi ta fadi haka sannan ta mike tsaye shi kuma ya kai hannu ya shafa kanta dake cikin hijab domin ya fahimci a bakin gaskiyarta take fadar Yassar ya bar gidan. Tana kokarin juyawa Amma ta shigo falon dauke da tray, bata yi mamakin ganin Hurriya a sitting room din mijinta ba, daman ta fi kowa yin latti zuwa makaranta ko fita unguwa. Musamman idan mahaifinta yana gari, a dole sai ta ganshi sannan zata fita, idan kuma bata zuwa ko’ina to tana zaune tare da shi a bangarensa babu ruwanta da ranar girkin Amma ne ko na Hajiya Kaltume ko Momy, ko da bata shiga har inda yake ba indai ta san yana nan zata zauna a part dinsa ne, hakan ya haifar da shakuwa sosai a tsakaninsu.

“Daman ai duk wanda yayi shiririta a garin Gusau a bayanki yake, ke kam Allah ya shiryar da ke Hurriya”

Dariya kawai ta yi ta fice tana fadin.

“Appa ka fada mata abun da Yaya Yassar yayi min. . .”

Daga mahaifiyarta har mahaifinta binta suka yi da kallo jindadi da farinciki har ta fice, sannan Amma ta girgiza kai ta maida dubanta ga Appa.

“Bismillah Appan Hurriyya muje ka karya”

Kamar wanda aka jefo a wata duniyar haka yanayin fuskarsa ya sauya daga murmushi da jindadi zuwa bakinciki da bacin rai da be san dalilinsa ba, ba dan komai ba sai dan jin muryar Amma a bayansa.

“Zan shigo”

Ya amsa ba tare da ya jiyo ba, domin baya son kallonta a yanzu, fuskar dake masa kyau da kwarjini, mace da yake gani yana jin kamar shi da ita sa’anin juna ne, a yau ita yake kyamar gani, muryar da ta fi kowace murya yi masa dadi a duniya yau muryar ce yake jin kamar tana sanar masa mutuwa. Cikin hikima da kokarin danne damuwa ta sauke ajiyar zuciya domin ta san shekaru da aka fito da watanni mijinta ba haka yake ba, a da idan ta kawo masa abinci jiki na rawa yake tarbarta ya fara zuba santi tun kamin ya ci, ba zai ma bari ta fara isa bedroom dinsa ita kadai ba sai ya rika mata tray ko ya dauki wani abun yana zolayarta, amman a yan kwanakin da idan aka a hada su aka kirga zai bada wata daya ya sauya mata gaba daya.

Sai da ya tabbatar ta shige sannan ya juyo ya kalli kofar dakin, hannu ya saka a kirjinsa ya danne tashin hankalin da yake jin yana kusantoshi. Cikin wani yanayi mai kama da nauyin jiki da na zuciya ya cira kafarsa ya fara takawa tare da maida hannayensa baya ya rumgume yana tafiya a hankali. Yana shigowa cikin dakin Amma ta juyo ta kalleshi da damuwar da ta gagara boyuwa a fuskarta.

“Ranka ya dede waya canja Bedsheet din nan?”

Tsaye yayi yana kallonta kamar mai tunanin kalar amsar da zai bata, kana kallon idinsa zaka karanci damuwar dake tare da shi. Can kuma ya kawar da fuskarsa ya dawo da hannayensa dake rumgume a bayansa ya zuba su cikin aljihu.

“Kaltume ce ta canja”

Da matukar mamaki Amma take kallonsa, domin al’adarsu ce duk wanda ke da girki ita zata gyara bangaren mijinta kuma zata tafi da Bedsheets dinta ta shimfida, idan wata zata karbi girki sai ta kwashe kayanta wadda ta karba ta shimfida nata ta kula da bangaren, hakan ya saka ko wace mace da kalar kamshin turaren dake fita a part dinsa idan girkinsu ya zo.

“Ban gane ta canja ba? Jiya na shimfida shi fa, kuma jiya da yau girkina ne, ai ta jira har sai girkinta ya zagayo tukuna ta canja”

“Ni na saka ta canja kuma na karya zaki iya dauke abincinki”

Kamar an watsa mata ruwa sanyi a jiki haka ta ji duk wata kusurwa da logo dake jikinta ya saki, lakkar jikinta ta yi kasa.

“Gaba daya na daina gane maka a yanzu Appan Hurriyya ka canja min”

Ta matsa inda yake tsaye ta risina kasan guiwowiyinta ta hade hannayenta kamar mai rokon gafara.

“Wannan shi ne karo na biyar da zan sake rokonka idan wani laifi na yi maka ka fada min na nemi yafiyarka, ka dubi girman Allah ka yafe min, ka daina hukunta ni da wasu dabi’u da halayya da ban sanka da su ba, kuma baka saba yi min ba”

“Baki min laifin komai ba Iyami, Wallahi ban rike ki da wani abu ba a zuciyata ba”

Ta daga kai ya kalleshi.

“Toh me yasa kake min haka? Akan wani dalili zaka saka Hajiya ta canja zanen gado kuma ta kawo maka abun karyawa bayan ni ce da girki?”

“Saboda zata karbi girki a yau”

Kamar an tsinke wutar cikin jikinta haka ta ji, sai ta mike tsaye tana kallonsa ta kasa sake furta komai.

 Hannayensa ya cire aljihu zuba ya nufi kusa da inda ta aje masa tray ya zauna gefen gadonsa sannan yayi mata alama da ta zo ta zauna.

Ta kalli gurin da ya nuna mata amman ta kasa cira kafata ta isa gurin.

“Zo ki zauna Iyami”

Sai a lokacin ta ji kuzari ta cira kafarta ta taka har ta isa gurin ta zauna jiki a sanyeye tana kallonsa. Ajiyar zuciya ya sauke kusan sai uku sannan ya kai hannunsa ya bude bedside drawer ya dauko wata yar karamar jaka ya bude ya dauko wasu takardu ya mika mata.

“Wannan takardun gidana ne da yake a Samaru, na saka lawyer na ya canja komai daga sunana zuwa naki, na kafa shaida da lawyer na kuma ta bangarenki na yi magana da Bappa shi ma ne shaida domin a gabansa aka yi komai, sai dai na bukaci kar ya fada miki saboda ina son ya zama ni zan fara sanar da ke, saboda haka yanzu gidana dake Samaru mallakinki ne halak malak…”

Ta mika hannu biyu ta karba cikin yanayin mamaki da faduwar gaba, ta kasa godiya haka kuma ta kasa jin farinciki ko kishiyarsa. Wata karamar Envelop ya dauko a cikin jakar ya mika mata.

“Wannan Cheque ne na Naira miliyan Ashiri, ina son ki yi amfani da kudin ta hanyar da ya dace ki yi kasuwanci ki rike kanka dan Allah”

Ta karba idonta na cika da hawaye.

“Wannan duk na minene?”

Yayi shiru ya kasa ce mata komai, sai ya sake saka hannunsa ya dauko wani envelop din ya mika mata.

“Ki yi hakuri Iyami, ina jin rashin natsuwa da faduwar gaba da tashin hankali a duk lokacin da girkinki ya zagayo, idan na tuna kina a cikin gidana karkashin kulawata sai na ji kamar zan mutu, na yi ta daurewa ina ganin kamar abun nan zai wuce amman ban ga alamar haka ba, a kullum sai kara yin gaba abun yake, akan hakan na yanke hukuncin yin abun da zai zame mana mafita gudun kar na cutar da ke, domin idan muka daure a haka ban san a gaba yadda zama zai kasance ba”

Kasa mika hannu ta yi ta karba kuma ta kasa ta kasa cewa komai, ta kasa dauke idonta daga barin kallonsa, hawaye kuma suka ce  mata ga rabarsu. Ganin haka ya saka ya aje mata takardar a saman takardun da ya mika mata.

“Bana son ki bar min komai duk wani abun da na siya miki tun daga kayan daki har tufafi da duk wani abun more rayuwa, mallakinki ne zan saka a kawo miki har gida, amman dan Allah ki bar min Yayana a hannuna ban yarda ki tafi da ko daya ba, cikin dake jikinki ma idan kin haihu zan dawo da abu na a gidana”

Sai a lokacin ta samu kuzarin bude bakin da yayi mata nauyi ta yi magana.

“Babu uwar da zata so wasu yayan kamar nata, kuma babu yayan da za su jidadin wata uwar kamar ta su, musamman a gida irinka”

“Kin fi kowa sanin yadda nake son ƴaƴana, da uwa ko babu uwa za su jidaɗin zama a gidan mahaifinsu, zan kula da su”

Ta haɗe wani abun da ya tsaya mata ta miƙe tsaye da tunani kala kala, ta bude takardar ta duba me ke ciki saki ne ko akasin haka? Idan sakin ne saki nawa ne? Ko kuma dai ta faɗi a ƙasa ta yi masa kuka ta roƙi ya maida ita bayan ya faɗa mata baya jin natsuwa da kwanciyar hankalin a zamansa da ita yanzu?

“Allah yasa hakan shi ne alheri, kuma ya baka ikon kula da su Hurriya da Hamad”

Ita kanta sautin murya mai kama da tata take jin tana fita a bakinta, domin bata da tabbacin tana da kuzarin furta masa wani abu a yanzu. Tana jan ƙofar ɗakin nasa ta ji ƙafafuwanta sun yi nauyi, mararta ta murɗa wani irin tashin hankalin da bata taɓa samun kanta a ciki ba ya baibayeta. Da gaske Appan Hurriya sakinta yayi? Anya zata iya tafiya ta bar ƴaƴanta? Ko dai wasa yake mata wata ƙila kuma wunin yau gaba ɗaya be faru ba. Tana tafiya jini na mata zuba amman bata sani ba zafin zaton sakin da bata tabbatar ba ya manta da ita zafin mararta dake murɗawa, ya hana hankalinta kusanto jikinta ya juya tunaninta a gurin abun da bata taɓa mafarkin faruwarsa ba.

Arzikinta ɗaya, ko wane part an yi masa corridor da zai sada ɓangaren da ɓangaren Alhaji Haruna ba sai ta gaban gidan ba. Kuma zaka iya fita ko shiga ba tareda sanin kowa ba, har sai idan mutum ya isa part ɗin. Kamar wadda ta sha giya haka ta isa ɓangarenta ta zarce bedroom ɗinta ta zauna a kan gadonta.

“Innalillahi Wa’inna Ilaihiraji’un”

Ta furta daker tana kokarin dawowa hayyacinta.

“Haka ake ji? Haka saki yake? Ko dan ina da kurciya ne? Ko kuma saboda ban saka tsammanin zuwan sakin ba ne gaba daya a zaman rayuwata? Ko kuma saboda ina tsoron barin ƴaƴana ne? Allah ka sassauta min, ka saka min natsuwa da kwanciyar hankali, ka hallata aure ka hallata saki, Allah ka yaye min wannan damuwar da zata rufe ni, Ubangiji ka tsaya min”

Rahamar Allah ga bayinsa, da kuma dace ya ƴan amin a kusa, tana gama addu’ar ta ji natsuwa ta sauko mata, numfashin da take jin kamar zai danne mata kirji ya daga mata, mararta ta sake murdawa har sai da ta lumshe ido ta kai hannunta ta taba cikin dake jikinta na wata shida.

Kamar wadda aka yi ma allurar kuzari haka ta tashi ta aje takardun hannunta ta shiga bandaki ta gyara kanta ta fito ta gyara dakin inda ta ɓata ta cire Bedsheet din ta bar gadon a haka, ta dauki ruwa da tsumma ta bi tana goge jinin da bata san ya zuba ba sai a lokacin. Kamar mai shirin yin sata haka ta shiga ɓangaren ta goge jinin sannan ta juyo gabanta na tsananta faɗuwa ta fito daga ɓangaren. Ganin jinin yaƙi tsaya mata ya saka ta sake tsabtace jikinta ta saka pant da pad ta tare sannan ta kwanta saman gadon tana sauraren zuciyarta da ke bugawa da karfi, mararta kuma na cigaba da murdawa.

“Me na yi ma Appan Hurriya?”

Shi ne abun da take ta tambayar kanta, tambayar da bata da amsarta, mulmulawa ta yi saman gadon tana karewa katon dakinta kallo kamin ta tashi zaune ta fashe da kuka mai karfi, a rayuwarta bata taba fuskarta wani abu na tashin hankali irin yau ba. Cikin kuka da bakinciki ta dauko akwatunanta ta fara zuba kayanta ba tare da ta tsaya shiryasu ba, wani abun ma sai dai ta gwamatsa shi cikin wani talkaminta da atamfa ta saka su a kwati daya, sai da ta gama ta rufe ta kaisu gurin kofa ta aje ta dawo cikin dakin ta zauna kasa ta rasa me ya rage mata ta yi, kuma ta kasa fita daga dakin.

Misalin Karfe biyu da mintuna Bus dake dauko yaran makaranta ta shigo gidan, a harabar da aka tanada domin aje motoci direban ya faka motar. Sai da manyan suka fara fita sannan Hurriya ta fito, Hamad kan cikin manyan yayyunsu ya kutsa ya fita, daman shi yana daga cikin sarakunan kiriniya da rashin kunya na gidan, babu kalar dukan da basa masa ko hantara amman kowa yace masa kule zai ce chasss, Amma ta yi fada har ta gaji, Appa ma har baya son a kai masa kararsa domin ko ya masa fada ba zai hana gobe ya sake ba, Hamad irin yaran nan ne da ko kallonsu ka yi a karkace sai sun rama.

Hurriya na shiga part dinsu ta jefar da jakarta a kan kujera ta nufi bedroom din mahaifiyarta, a hankali ta tura kofar dakin ta shiga tsaye ta yi bakin kofar tana kallon kanenta Hamad dake ta fadawa Amma abun da ta yi masa a makaranta.

“Amma karya yake, karfe 1:30pm aka tashe mu shi ne na ce nasa yaje yayi sallah saboda bus din mu sai 2pm take zuwa ai, shi ne ya taso min fa masifa har zai yi dambe da ni gaban yan makaranta har da yan ajinsu fa”

Hamad ya juyo ya kalleta a fusace.

“Toh ina ruwanki da ni da zaki ce na tashi na yi sallah, kafiri ne ni ko bana sallah aka ce miki? Salon friends dina su fara tsokana ta suna cewa bana son sallah”

“Na ji ba zan sake maka magana ba, amman ni ma karka sake zuwa class dinmu ka ce na ara maka wani abu, ba ruwana da kai karka sake taba min komai kuma safata da ka saka yau ban yafe ba karka sake min taba min komai”

Amma ta mike tsaye tana kallonsu kowane zuciyarsa ta kawo kamar abokan gaba.

“Wannan fadan duk na minene wai? Ku kullum baku zaman lafiya? Kai kake binta amman kai da ita babu zaman lafiya, abinci ma ba zaku ci a plate daya ba, magana mai dadi babu tsakaninku kullum sai fada?”

Hamad ya ce.

“Ita ce bata ba ni respect ai”

“How? Kai ne babba or ni? Ni ce babba ai kai ya kamata ka ba ni respect”

“Ni ba zan taba baki respect ba i hate you kuma kika sake min wata maganar banza sai na ballaki”

Hamad na kaiwa nan ya juya ya fice rike da jakarsa har yana bankade Hurriya.

“Amma kin ga ko? Imagine”

Amma ta dafe kanta ta zauna bakin gadon tana fashewa da kuka.

“Innalillahi Wa’inna Ilaihiraji’un”

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *