Amatulmalik Chapter 5

Amatulmaleek Chapter 4

This entry is part 4 of 6 in the series Amatulmalik na Mamuhgee

4

Duk fada da masifar daya daga cikin  ma’aikatan tashar yayi mata akan zuwan nata duk da baisan dalili ba bare Kuma alaqarta da Gidan ASH TALBA din datazo gurinsu Amma dai yasan Hakan datai na zuwan Kai tsaye nada hadari.

Kallanta yayi Kai tsaye yace ta Fadi sunanta ya rubuta Sako ya tura mata ga numbern,

Jiki a mace cikin sanyi ta fada masa tareda Dana ‘yayanta wainda yayiwa Wani kallan qyama da takaicin yanda ta kwasosu kaman wasu almajirai sunzo garinda basusan koinaba ko tsoro bataji.

Kai tsaye sunanta Dana yayan nata ya rubuta a cikin sakon da cewan a taimaka a dauki wayar gasunan Tasha a zube harda mara lafiya.

Tafiyar sakon ya sakashi kallanta yace ta zauna ta jira idan ankira to shikenan idan Kuma baa kiraba motar asubar safe su koma inda suka fito.

Gyada masa Kai tayi cikin sanyi da nutsuwa tareda Bude Baki ahankali tayi masa godiya ta juya ta koma inda su Amatun ta zauna tana kallansu har zuciyarta bataji komai ba na haushi ko jin zafin rashin daukan wayar harma da fadan da ma’aikacin tashar yayi mata Dan kuwa Babu lefi a cikinsu saima uzuri datakewa kowa Wanda shine abin dayafi bawa mutane Daman cutatar da ita ko acan kauye sbd komai kayi mata a rayuwa tanai Maka uzuri Bata fushi Komai girman cutar da zakai mata.

Zaune suke cikin duhu da rashin mafita hakanan ta miqe tayi alwala a gurin tayi sallah har lokacin AmatulMaleek a kwance take jikinta yafara tsanani sosai Abdulhameed ma tini Shima yafara kamuwa da zazzabin sbd wahalar yunwa.

Har Akai ishai Babu Wani bayanin biyo sakon da suka tura da kira Dan haka ta Yanke komawarta da bin motar asuba Kila Wani uzurin ya Hana Abeeda ganin sakon Dan haka bazasu cigaba da damunta da Kiran ba akwai takurawa ga Hakan ta sani.

Ruwa kawai ta ringa bawa Abdulhameed da AmatulMaleek har kusan asuba anan suka kwana cikin sanyi a sararin iska ga sauri da duhu harma da qwari kala kala Dan haka asuba nayi sallah kawai tayi suka miqe Dan shiga layin bin motar komawa.

Koda gari ya fara haske AmatulMaleek kaman bazata tashi ba hakama Abdulhameed Dan haka sai hankalinta ya rabu biyu ga tafiyar sbd bazasu iya bin doguwar hanya a Hakan Amma Kuma Babu zabi na yanda zatayi Dan haka tayi shiru a cikin sanyin jiki Dana zuciya idanuwanta sunyi jajir da damuwar Dake riqe da zuciyarta.

Isowar ma’aikacin tashar na jiya ne gurinta Yana qwala kiranta ya Sakata dagowa ahankali cikin sanyi ta Dan kallesa tareda sauke Kai tana gaidasa da girmamawa.

Da farin cikin dayake tareda takaici ya kalleta Yana cewa tayi Maza tazo ana son magana da ita anbiyo sakon da kira yanzu.

Numfashi ta sauke me dumi kafin ta fito layin a sanyaye ta biyosa zuwa inda ba hayaniya ya miqa mata wayar wadda daidai lokacin aka sake kira.

Cikin nutsuwa ta Bude Baki tayi sallama nauyin zuciyarta na raguwa Jin amsa sallamar Abeeda cikin Wani irin nutsuwa ta wainda suke cikin duk wata ni’imar rayuwar duniya.

Jin muryar Asmau ya Saka Madame abeeda sauke ajiyar zuciya a hankali tareda sake Bude Baki tace

“Asmau kece??

“Meyesa Baki kirani da wayarki ba?

Yaushe kikazo?

Sai yanzu nake duba sakon sbd Banda time na duba wayar rasuwar da Akai ya Saka Sam bana samun Hutu yanda ya kamata.

Shiru sukai dukkaninsu sbd kowannensu da Wani girmamman quncin dayake mamaye cikin ransa Amma baisan tayaya zai tinkari Dan uwansa ba sbd Nisan daya shiga cikin kusancinsu da tsananin kaunarsu

Numfashi mara sauti maamah ta sake saukewa ahankali kafin ta Dan saki murmushi me sanyi tace

“Eh nice,jiya nazo sbd labarin rasuwar ta alhaji babba danaji daga bakin Dan gidan kawu bello dayake Dan shiga birni shine yazo ya sanar mun,

Allah yaji qansa yayi masa Rahama,

Munata damunki da kira ga fama da jamaa Anata zuwa gaisuwa.”

Numfashi Madame abeeda ta sauke kafin tace

“Ba komai yanzu ku Jira ga driver Nan zan Aiko yazo ya dauko ku keda yaran ai gwara da bakiyi saurin juyawaba Ina buqatan ki Asmau,

Ina tsananin buqatan nawa a kusa Dani”

Shiru suka sake yi jikin Maamah na sanyi ita Kuma acan nata bangaren wasu zafafan hawayen da babu Wanda ya taba ganinta dasu ne suka taru a cikin idanuwanta Amma Bata bari sun taba saukowa kan fuskartaba bare yau din Dan haka ta sake hadiyesu cikin dauriya da karfin zuciya kafin ta kashe wayar ta ajiye gefenta sbd Asmau kamar rauninta ce sbd Bata iya boye mata komai duk dauriya da jarumtarta.

Ita kanta Asmau sanyi jarumtarta ke Neman yi Dan haka ta daure batareda ta dago ba tasake yi masa godiya tana koma gurin yaranta da suka koma kamar mahaukatan almajirai.

Zaunawa tayi tareda zuba musu idanuwanta da suke boye duk Wani abinda yake cin Rai da zuciyarta tana musu fatan hayewa matakin nasara a duk inda suke rayuwarsu.

Zaman jigum tayi tana sauke kanta qasa da jiran tsammanin Kuma Ina rayuwa da kaddara zatai dasu itada yayanta a gaba.

Zaman jiran awa kusan Daya da Rabi tayi zuwa biyu kafin Daya daga cikin Mahaukatan motocin gidan ASH TALBA ta iso tashar daukanta.

Da farko numbern da aka bawa drivern yazo daukanta ya kira shine ma’aikacin tashar ya kawosa har inda Maamah take zaune kaman almajira ita da yaranta yace “gatanan”

Kallanta drivern yayi dakyau kafin ya dawo da kallansa kan mutumin Dake nuna masa ita Yana wasi wasin idan wannan din ce akace ya dauka yakai gidan ASH TALBA sbd ko masu aikin gidan bazasu dauki wannan aikin gidajensu ba bare gidan ASH din da kansa.

Lura da fahimtar tinanin dayake gudana a zuciyar drivern yasaka Dan tashar sake basa tabbacin ita din dai ce,daga kauye ta fito shiyasa.

Kasa cewa komai driver yayi sai kawai ya dauki jakar kayanta ya Bude bayan black range Rover Din dayaxo da ita yana sake kallansu maamah din cikin danne mamakinsa da Dan shakkar idan ba kuskuren daukansu zaiyiba.

Maamah dasu AmatulMaleek ma da basusan inda kansu yake ba rakubewa sukai tareda dunqulewa guri Daya bayan motar Babu me iya motsawa sukai shiru Maamah din najin zuciyarta na Dan sake sanyi da taimakon gaggawar dasu AmatulMaleek din zasu samu Dan kuwa data koma dasu a wannan halin ba lallai ta samu Isa gida da duka yayanta biyu ba Kila ta rasa ran Daya a hanya kafin su Isa,sai gashi Allah ya dubi maraicinsu ya kawo sassauci a lamarinsu ta samun Kiran Abeeda.

Tafiya me Dan tsayi sukai kafin suka Isa,

Koda suka Isa tini sanyin ac yakusan sankarar dasu Abdulhameed Duk da sun Saba da sanyin Allah Amma wannan din yayi musu karfi da yawa sosai.

Babban makeken luxury gate din  gidan ASH TALBA aka wangalewa motar gidan dasuke cikinta suka shige harabar gidan datake da Wani irin girma da tsari irin na gidajen turai da Kuma masu abin duniyar qasa da qasa,

Motacin Dake harabar sunkai takwas koma fiye,

Motoci ne wainda babu me karamin kudin da zaka iya lissafawa bare manyan,

Dukkaninsu baqaqe ne sai farare guda biyu aciki sai Ash Daya.

Parking yayi daga gefen da ake ajiye duka motacin gidan Dana mutan gidan Banda na ASH dake gefensu daban sbd ta inda yake fitowa daga sashensa da Babu Wanda yake bin kofar idan ba shi ba Dan haka ta Nan yake fitowa ya shige motacinsa yabar gidan batareda ma kana gidanba bare kasan fitarsa.

Tinda Sharif driver yayi parking ya fito yake Dan Jin zuciyarsa na sake shiga shakku idan baiyi kuskuren dauko Wanda Basu aka aikesa daukowaba.

Bude musu motar yayi Yana kallansu yace maamah tafara fitowa tukuna idan ya tabbatarda sune aka sakasa daukowa saisu shiga.

Wayarsa ya fitar cikin nutsuwa ya Nemo numbern Madame din ya Saka kira.

Saida yayi mata kira biyu kafin ta daga Kai tsaye ya sake gaisheta Yana cewa

“Hajiya ga baqin na dauko Amma bansaniba ko na samu kuskuren daukowa wainda Basu ba….

Katsesa Abeeda tayi da cewa

“Bata wayar naji”

Da sauri ya miqawa Maamah wayar Yana cewa “yi magana taji”

Karban wayar maamah tayi tana sallama Abeeda ta kashe wayar tareda miqewa daga zaunen datake ciki lafiyayyan bedroom dinta sanyeda jallabiya ash da mayafi me Dan girma na sallanta ta ajiye wayarta tana nufar kofar barin bedroom din sanyeda slippers masu tsananin laushi da tsadan kudinsu zasu ciyar da maamah din da yayanta na sati uku koma fiye.

Tinda ta tinkaro babban palonta ta nufo kofa ma’aikatan Dake gyaran palon suka ringa gaisheta cikin tsananin girmamawa sun Dan sauke Kai sbd Koma me zai fitarda Madame din harabar gidan a daidai wannan time din me tsananin mahimmanci ne.

Sharif dayaji madame ta kashe wayarta Babu amsar komai Shan jinin jikinsa yayi sbd ta tabbata kenan yayi kuskuren dauko wainnan kauyawan dajin.

Kallan maamah yayi cikin sauri Yana cewa

“Kinga maza shiga na mayar daku inda na daukoku kafin na Rasa aikina”

Juyawa mota maamah tayi tana kokarin komawa batareda tace masa komaiba Dan itama batasan dalilin kashe wayar Abeedan ba.

Cikin fada da daga murya yaci gaba da yi mata sauri sauri Yana cewa

“Wai bazakiyi sauri ba muje?

Kema kinyi gangancin biyoni bayan kinsan Babu ta inda kukeda arzikin Azo daukanku da mota irin wannan Amma haka kawai kika biyoni gashi Kuma Kinga irin gidan da akazo bazaki Bude Baki kice bakuda Hadi da irin wanna guraren”

Shiga motar Maamah ke kokarin saiga fitowar Abeeda harabar gidan tini ta dagakata daga shiga motar tana tsayuwa a inda take gabobin jikinta na Neman saki idanuwanta dasukai Dan ja suna tsayuwa a kan Abeeda wadda itama nata idanuwan akan Maamah din suke tana kallan Wani irin mugun mummunan yanayin da Asmaunta ke ciki kamar wadda Tayo gudun hijira.

Suturar jikinta ta kalla taji hankalinta na mummunan tashi kafin ta tsayar da idanuwanta akan fuskar Asmaun da sauran kadan takoma skeleton sbd rama da bushewa.

Maamah kasa kurar da nata kallan tayi kan Asmau sbd alkunya da muzantar dataji tanayi agaban Abeedan sbd yanayin datazo gidan dashi kamar almajirar data debo tafiyar qafa.

Qasa tayi da kanta lokacinda Abeeda ta tinkarota Kai tsaye jiki a tsananin mace da baqin cikin ganinta ahakan tana isowa hannunta take kokarin kamowa tana ambatar sunanta muryarta na rawa sosai.

Kasa bari maamah tayi Abeeda din ta a kamata sbd jikinta Babu inda yake da tsafta ita kuwa tamkar wata tauraruwar datafi taurari take komai nata na musamman ne sbd Jin dadi,Hutu da daular da Allah yayisu acikinta.

Sharif na ganin Hakan yasan ba kuskuren ne dai aka samu ba Dan haka a Jere ya Sako ajiyar zuciya Yana Bude mota da sauri yahau kokarin kamo Abdulhameed sbd AmatulMaleek bazata dauku garesa ba tinda ta fara zama yar budurwa.

Yanda Sharif ya dauko Abdulhameed kamar matacce ya Saka gaban Abeeda mummunan faduwa tana kallan Motar cikin tashin hankali tace

“Meya samesa?

Ina AmatulMaleek?

Meya samesu?”

Jiki na rawa murya na sauri sharif yace

“Ahaka aka daukosu daga Tasha inaga basuda lafiya sosai sunyi Nisa musamman ita macen ko numfashi ma batayi…””

Bai qarasaba Abeeda ta katsesa da cewa

“What??

Kallan maamah tayi tana Isa motar jikinta na rawa takai hannunta kan AmatulMaleek Dake kwance ba Rai ta janyota kafin tayi Wani yunkuri tini sharif ya kira masu aikin gidan mata su biyu suka iso gurin Dan daukan AmatulMaleek Dan baiyi tinanin Madame din tasu zata iya taba mutanenba.

AMATULMALEEK

Mamuhgee

#ZafafaBiyar

Series Navigation<< Amatulmaleek Chapter 3Amatulmaleek Chapter 6 >>
Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *