Ameenatou Hausa Novel Part 2

Ameenatou Part 2

This entry is part 2 of 4 in the series Ameenatou na Mamuhgee

AMEENATOU
Mamuhgee

ZafafaBiyar

blackMoneyLove

2
Kaman yanda suka Saba duk zasu shiga Rami a tare suke shiga basa yadda su shiga ba tareda Dan haka Basu taba shigar ba tareda junansu su biyar din ba.

Gyara tsayuwa mamman yayi Yana Dan gyarawa daurin jakar kayansa a qugunsa Yana kallan omer da kusan shine koyaushe me zama karshen Shiga Dan ya yaddarwa kansa idan kullum suna shiga su fito wataran yasan idan suka shiga bazasu fito din ba.

Shiga sukai da karfin gwiwansu tareda qarfin zuciya Dan kuwa ginar zinari Se me taurin zuciya da rashin tsoro,

Rami ake ginawa me zurfin gasken da idan ka shiga zafinsa da duhunsa kadai zai iya kashe me qaramin karfin jini ko me tsoro,
Da fitila ake shiga tareda batiran fitila da ruwan Sha duk a jikinka daure sbd idan ka shiga bawai Kai tsaye kake fitowaba wasu sai suyi kwana Daya a ciki wasu fiyeda kwana Dayan da kwanaki ma duk sunayi a ciki sbd ba wai Rami ne da zaka ringa shiga Kai tsaye kana fitowa ba,
Idan wainda suke ciki suna ciki to ko magana zaayi musu Saida loudspeaker sbd sunyi Nisa a cikin qasar da ba zasuji magana Kai tsaye ba.

Aduk lokacinda zaa samu zinari ko ginosa to tabbas jinin rayukan mutane da dama zasu salwanta sbd hadarin Dake ciki tareda wani irin son zuciya me qarfin gaske,
Rijiyar Gino zinari bawai Rami ne na qasa ba zaa ringa ginawo Rami ne dazaa ringa ginawa a cikin qasar tareda dutsina masu karfin gaske Wanda shiyasa hadarinsa yakeda yawan gaske sbd wani dutsin kana bugosa a cikin ramin zai rufeka gaba Daya ya zubo ya danneka ba iya Kai Daya ba zai iya zubowa ta koina yayi sanadin Rai fiyeda adadi Wanda da yawa ana ji ana Gani za’a samu Ciro wasu wasu kuwa qasa ta ciny shikenan sbd bazaa iya cirosu ba alokacin,
Idan zaa haqo rijiyoyin zinari a gurinda ake da tinanin akwaisa ana haqo akalla rijiyoyin da fadinsu da zurfinsu bamai misaltuwa bane a gurin akalla daga rijiya goma Sha biyar zuwa sama har dari biyu Wanda jiri ma zai iya Kamaka idan ka tsayu a gurin.
Zinari nada wani Sirri Wanda shine a duk lokacinda jinin wani ya zuba to takan qara yaduwa ne tamkar Shukan da ake bawa ruwa.

Su mamman tin iyayensu na raye suke yawon nahiyoyi daban daban dan Gino zinari Wanda idan suka bar gida akalla sukan shafe watanni da yawa basu dawo ba sunacan cikin daji da Sahara da yawon kauyuka masu Nisa da hatsarin gaske Dan Neman zinari Amma har Allah yayi musu rasuwa Daya bayan Daya duk a harkar Basu samu komaiba bare Tarawa Dan haka yayansu suka dauki Niya da damara tareda alkawarin ko da dadi ko ba dadi,Koda jinin wasu ne saisun samu bazasu qare a wahalce kaman yanda iyayensu suka qare a daji da nahiyoyin nesa Dan Neman zinari ba.

Mamman a cikinsu shine Wanda yafi kowa karfin hali da rashin yadda Koda wasa a tauyi haqqinsu Dan haka suke Dan samun na abinci a harkar duk da Suma har lokacin Allah Bai Basu tasu nasarar ba Amma Basu cire Rai ba Dan yanzu suke matasansu.

Omar a cikinsu Kuma shine Wanda yafi kowa sonsu,
Yana tsananin kaunarsu fiyeda kansa sbd shi Kuma duk abinda ya samu su yake miqa Se yanda Akai dashi duk da Suma sauran suna tsananin kaunar junansu.

Dukkaninsu dai marayu ne tinda Babu me Uba a cikinsa hakama iyayensu mata biyu rasu, mahaifiyar Omar da mahaifiyar mamman,
Tinda suka fara Dan tasawa Suma idan suka bar gida suka kutsa nema saisu share watanni fiyema da yanda iyayensu ke dadewa batareda sun dawo ba sedai duk inda dayansu ya Saka kafa suna nan a tare kaman kashin awaki a manne da juna shiyasa kusan ake da saurin saninsu a duk inda suka yada zango sbd Yan biyar seelahs da ake kiransu.

Shekaransu bazasu wuce Sha takwas zuwa ashirin ba a lokacinda Allah ya bayyanar musu da babbar sa’ar rayuwarsu Kuma babbar musibar rayuwarsu ba.

A babban dajin kauyen ashalawa Dake wani yankin Daya raba shiga nijar da Nigeria suka yada zango kusan shekara Daya har sun zama Yan gari Yan gida Dan kuwa duk kusan da yawan jamaa sun Sansu Kuma suna Jin dadin aiki dasu Dan kuwa sunada karfin halin gaske da taurin zuciyan neman arziki ido rufe Dan kuwa sun dauki alwashi sun duqufa bazasu koma gida ba batareda arziki ba Wanda kusan zuciyar kowannensu ta sauya kudin arzikin zinariya kawai kota yaya.

A ashalawa wata babbar duniyar Neman zinari ce sbd asalinta ba gari bace bare kauye,
Tarin matafiya da Yan kwadago da Yan cin kasuwar gari gari tareda asalin buzaye masu harkar danyar zinari da Yan Nigeria Suma masu harkar rijiya da Kuma danyar zinari ne suka taru suka Maida asalin dajin da aka Gano tarin arzikin zinariya acikinsa gari guda,
Sun Maida dajin ya koma kusan babbar garinda kasuwar duniya kawai akeci a cikinsa,
Ashalawa baida dare baida Rana bare asuba,
Kowanne lokaci su a gurinsa lokacin harka ne Dan haka Koda yaushe a hargitse yake kowa na abinda yake gabansa,
Babu Mai auren da zaka samesa da iyalinsa a ashalawa sbd gurine da babi yiyuwar kawo iyali Dan kuwa Babu kalar kaddararrun mutanen da babu masu rayuwa daban daban,

Tarin karuwai masu aji da masu saukin kudi Babu kalar wadda babu a ashalawa,
Idan Maza kake so kayi muamala dasu akwaisu,
Akwai matasa akwai manya,
Hakama ta bangaren yare da kabila kusan Babu kalar Wanda Babu,

Babu wasu gine gine a ashalawa sai runfuna da tinti da kusan sune suke cikewa ashalawa sunfi dari biyu zuwa dari hudu ma,
Gine ginen Dake ciki ko dozin bazasu kaiba Suma na wainda suka riqa ne suka samu zinariya sosai suka Gina suka zuba karuwansu da suka koma tamkar matayensu Dan kuwa duk Wanda ya jiqa a ashalawa bazai rasa akalla karuwan kansa kusan guda shida zuwa sama ba,
Marasa karfi sosai sune suke da karuwai bibbiyu haka ko Daya zuwa uku Amma dai sauran har me goma akwai.

Masu siyar da abincin ashalawa dukkaninsu Suma kaman mata Maza suke wasu kuwa karuwan ne Dan kuwa idan baka bazaka iya kashewa ko illatawa ko zama busashiyar zuciya bazaka taba iya zama a ashalawa ba.

A garin ashalawa Babu ranar da zinariya Bata kisa hakama Babu ranar da wani Baya illata wani ko kashewa,
Idan baka zuciyarka bata bushe qamas ba Kokuma Daman Tim farko Kai din me busashiyar zuciya ce zaka iya komai Dan ka tsira to bazaka rufa sati Daya a ashalawa ba batareda ka Isa kofar barzahu ba Dan kuwa rayuwa ce akeyi ta ko ka kashe ko akasheka Dan haka zinariyar ashalawa take sake habbaka da yaduwa koyaushe sbd jininda babu ranar da Baya zuba Kuma jini irin Wanda takeso wato me zafi na fitar rashin Imani maana jinin kisar gilla.

Tafiya me tsayi ta kwanaki da satika harma da wata ce ta kawo su mamman Ashalawa inda sukaga duniyar da Basu taba Gani ba Dan kuwa ashalawa wata duniyar ce ta daban me zaman kanta.

Da farko sunsha wuya sosai daqyar suka tsira suka Kai lokacinda suka fara gane kan rayuwar tsira ko mutuwa akeyi a Ashalawa Dan haka mamman ne ya fara tsayuwa ya jefar da tausayinsa gefe ya dauki rashin imaninsu da rashin tausayinsu ya tsayawa Yan uwansa suka fada harkar haqar rijiyoyin zinariyar ashalawa wainda akalla akwai rijiyoyin da aka Tona a gurin sunfi dari uku Kuma Babu wadda idan ka tsaya gefenta zafin ciki kawai idan ya huro Maka zaka iya Yanke jiki ka Fadi sbd tsananin zufinda zaka share fiyeda awanni masu yawa baka Isa kasanta ba.

Duk bulayin yawon shekaru masu yawa da iyayensu sukai harma dasu wanda sukai sai da suka iso Ashalawa suka San sun iso inda ya kamata ace sun samu isowa tin lokacin iyayensu Dan haka gabaki dayansu su biyar din Babu Wanda baisan a yanzu duniyar dasuke buqata ce suke.

Tinda suke a rayuwarsu tin daga lokacinda suka fara takawa da kafafunsu Basu taba zuwa koina ba batareda juna ba har suka girma wanka ne kawai yake rabasu Shima ba koyaushe ba sbd a ruwan gulbi suke wanka a tare sai Kuma su share kwanaki kafin su sake samun wata damar wankan sai zuwansu Ashalawa suka fara abubuwa ba tareda Shima shiga rijiya ne kawai sukeyi Hakan Wanda idan sun shiga sukan kwana Basu fitoba Dan haka kowa ya dage Dan kuwa yanzu kowa arzikinsa na hannunsa idan ya dage musamman Omar Dake da burin bawa kansa ilimin boko sosai da tasa dukiyar sabanin sauran da babu me dogon alkhairi a ransa.

Shekaransu Daya a Ashalawa sun goge sun zama gaba gaba acikin matasan da ake ji dasu a harkar,
Ba wasa ko tausayi aharkarsu,
Mamman kaf ashalawa bayan Yan uwansa seelahs babu Wanda bazai iya zubarda jininsa a qasar Ashalawa.

Kaman yanda kowa arzikin da Allah yayi masa daban haka Allah ya fara bayyanarda arzikin Dake tattareda kowannensu sbd sun fara Tara abin kansu suna samun zinariya sosai Dan yanzu zubar jinin a ashalawa yawa yake sake yi Kuma kullum samun baqin da Suma imanin Bai ishesu ba akeyi suna zama Yan gari Suma.

Turawa da labawa dakuma wakilansu sosai suke shigowa ashalawa wasu ma da helicopter ake kawosu suyi huldan su hau helicopter din su koma.
A taqaice ashalawa headquarter ce me zaman kanta ta huldar danyar zinariya wadda ake hadawa da gudanarwa cikin rashin gaskia Dan haka turawa da labarawa sosai suke Hulda da Yan Ashalawa Kuma Suma Yan ashalawa sunfi Hulda dasu sosai Dan baka iya fita Ashalawa da danyar zinari idanma ka hada sbd ta kowanne dajin da zaka fita masu jiran ka fito su kasheka su karbe suna Nan suna Jira.

MAMUH

BEST LOVE

BLACKMONEYLOVE

ZAFIN KAI

ROMANCE

JAMAAL JEEY SEELAH

TOOTOOHOT

ZAFAFABIYAR

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

Join our WhatsApp group here

AMEENATOUH
Mamuhgee

ZafafaBiyar

3
Da yamma ne sosai suka fito daga rijiyar zinarin bayan kwanaki da share a ciki,
Lameenu ne yafara fitowa da kyakkyawar sa’arsa ya samo zinariya me Dan yawa,

Murnarsa kasa biyuwa tayi duk da jikinsa Dake rawa sosai na tsananin wuya da wahalar Daya debo a ciki.

Mamman ne yafito na biyu Sedai shi Kam Bai samo wani abin arziki,
Jamilu da Omar da kasim ne suka fito karshe Wanda abinda suka samo Saida ya girgiza kusan mutane da yawa Dan kuwa sun samo abinda aka Dade babu Wanda ya samo irinsu.

Hayaniya Ashalawa ta dauka sosai Wanda tini aka fara kokarin nuna musu fin karfi sedai mamman Kara rayuwarsa yayi akan Babu Wanda ya Isa duk da akwai wainda suka fisa karfi da girma Amma zuciyarsa kusan zata iya fin tasu qarfi da soyewa idan har rashin imanin sukeji.

Turawa Dake Ashalawa da larabawa masu siyan danyar zinari tini suka firfito suka kama zasu siye da tsabar kudin dollar ko naira duk Wanda akeso Kokuma ta banki.

Wanke qasar da tacewa aka hau yi Dan fidda zinari daga cikinta aikuwa nan ashalawa ta sake rikicewa da tsananin mamaki Dan kuwa zuciyoyi da dama sun shiga tinani kala kala akansu Omar da kasim da jamilu.

Su kansu manyan Ashalawa a tsaye suke ana aikin wankin zinariyar Dan kuwa kowa ya kasa tafiya Dan yawanta ya tabbatar musu da sai an rasa rayuka akanta Dan Hakan suka tsaya.

Kasimu Dake murna da nasa da Allah ya azurtasa dashi Wanda zai ishesa Gina rayuwarsa cikin rufin asiri da wadata tareda rayuwa me kyau Jin yayi gaba Daya jikinsa ya mutu murnarsa ta koma ciki sbd abinda yake kalla a abinda su Omar suka samu shine har yayansu da jikokinsu Inshallah bazasuyi talauci ba,
Wani zufa da sanyin jiki yaji ya rufewa a lokaci Daya ya juyo a hankali ya Kalli mamman wanda yayi Nisa Shima a nasa tinanin.

Dan goge zufansa yayi da hannuwansa Dake cikeda qasa da ruwan qasar sbd daga qasansu har samansu koyaushe a cikin qasa suke sbd yanayin rayuwar da akeyi a Ashalawa din.

Matsowa yayi gefen mamman ya tsaya Yana Dan sake kallan mamman Wanda har lokacin mamman Bai juyo ya Kalli lameenu dinba idanuwansa da suka Dan sauya suna kansu Omar da kasim da jamilu Daketa farin ciki suna rungume juna Dan kuwa taskar arzikinsu dasukaita yawo tsawon shekaru suna nema Allah ya hadasu da ita.

Numfashi mata sauti mamman ya sauke ahankali Yana dauke idanuwansa akansu ya Maida kan zinariyar da aketa wankewa cikin ruwanta da ake wanketa dasu.

Wani numfashin ya Kuma saukewa Yana kallan tarin daruruwan Jamaar Dake gurin anata ihun zinarin,
A kaf ashalawa duk wani Mai Rai a cikinta idan ya samu dama yanada niya ko kudirin danne su Omar ya karbe zinariyarsu ko a ta sauki ko ata daukan Rai.

Daga yanxu dasu Omar suka samu wannan taskar arzikin rayuwarsu tana Bakin bodar mutuwa da rayuwa Dan kuwa Allah ne kadai ya Isa ya fiddasu ashalawa a raye matiqar ba sune zasu zama masu kashewar ba Dan tsira da arzikinsu Daman cikin Dayan biyun ne ko ka kashe din ko a kasheka.

Tinaninsa tsayawa yayi cak Dan kuwa duk yanda yake tsananin son seelahs dinsa baisan tayaya zai Basu kariyarda sukai alkawarin bawa juna ba har mutuwa.

Shima juyowa yayi ahankali ya Kalli lameenu Wanda daidai lokacin Shima juyowa yayi ya kallesa kowannensu da abinda yake ransa daban,
Kallan juna sukai tsawon mintina Babu Wanda ya furta komai bayan zuciyoyinsu da kowace da abinda take tattauna.

Mamman ne ya fara dauke Kai Yana sake Maida kallansa kansu Omar yayi musu kallan daqiqu kafin ya daga kafafunsu Yana washe bakinsa ya nufesu Yana bayyanarda farin ciki da murnarsa sosai,
Shima lameenu takowa yayi ya taho Yana bayyanarda tasa murnar suka rungume juna suna wani irin ihu da farin ciki Mai tsananin gaske.

Suna gama murna kan harkar tace zinarin suka koma sai alokacin su mamman ke sake tantance tsananin yawan arzikin dasu kasim din suka samu.

Ahankali yaji wani abu me nauyi na tasowa daga cikinsa zuwa kirjinsa Yana dannewa.
Dago idanuwansa yayi ya Kalli kasim dake sake shiga farin ciki Yana rungume Omar hadda sumbatarsa a gefen fuskarta yana cewa

“Ahhh Omar ahhhhh Omar burinmu na ratsa ilimi me kyau zai tabbata,
Zamuyi Tarayya da ilimi a cikin wadatar Ubangiji da rufin asirinsa.”

Wani farin ciki me sanyi dayake fitowa daga qasan Rai yake bayyana a kan fuskar Omar din Yana sake rungume kasim da mamman Wanda yake washe Bakin dole Shima.

Jamilu kuwa gaba Daya hankalinsa baa kwance yake ba idan ba ganin yayi dukiyar zinariyar ya shiga hannuwansu ba sunbar Ashalawa zuwa rayuwar arzikin Dake jiransu a duniyar wajen Ashalawa Dan kuwa Ashalawa kamar duniyar kafiran da ko sunan Imani ba Basu sani bane,
Ashalawa kamar wata qabilace me zaman kanta da Babu kalar zunubin da baa aikatawa a bayyane cikin izgilanci Dan haka shi a matse yake da barinta a yanzu Daya samu Arzikin da zai wadatar da duk zuriar da zai Tara har tsawon lokacinda Bai saniba.

Lameenu duk yanda yakejin murnar nasa samun a farko gabaki Daya ya dakushe Baya murna ko yar kankanuwa,
Daci da nauyi yakeji a zuciyarsa fiyeda yanda yayi tsammani Dan Bai taba dauka zaiji qyashin samun Daya daga cikin seelahs dinsa ba.

Har dare har safe suna aikin cire arzikin zinariyarsu ba har kusan wata yamma kafin suka samu aka gama cireta gaba Daya aka narka aka ajiye a jere wanda nauyinsu ya sake girgiza Ashalawa.

Sai a Daren su kasim suka samu kansu suka dawo rumfarsu bayan sunyi magana da masu Siya,
Na Omar wani bature ne zai Siya,
Na kasim da jamilu kuwa balarabe ne zai Siya Dan haka Basu baro tent na turawan Dake gefen manyan Ashalawa ba dayake da masu tsaron gaske na samudawan Ashalawa.

Karfe Daya da Rabi da wani abu suka shigo rumfarsu inda mamman da lameenu ke kwance suna bacci Dan haka Basu tayar dasu ba suna cikin tsananin farin cikinsu Daya dadu Dan kuwa wannan Daren shine darensu na karshe a Ashalawa washe gari zasu bi turawan zuwa sabuwar rayuwar Dake jiransu Kuma zasu tafi ne da Yan uwansa lameenu da mamman Dan kuwa dukiyarsu ta seelahs ce gaba dayansu.

Jamilu kaf rayuwarsa Bai taba samun kansa a cikin asalin farin ciki ba irin Daren Dan kuwa mahaifansu mata zasu samu rayuwar kulawa da tattalin da mahaifansu Maza Basu samu damar Basu ba suna gurin yawon nema har suka rasu.,
Zai Tara Iyalin kansa su taso cikin Hutu da wadata ba irin tasa rayuwar Daya taso tin qanqani a yawon duniya ba.

Omar da kasim ma kwantawa sukai kusa da juna suna kallan juna kowannensu zuciyarsa kaman zata zage sbd farin ciki da murnan samun rayuwar nutsuwa da Kwanciyar hankali da ilimi da suka Dade suna buqata da fatan samu.

Omar ne me tsananin burin son rayuwar nutsuwa da ilimin dayake tattare da Kwanciyar hankali da rashin damuwa,
Ahankali raayin Hakan da tsananin so da burin Hakan ya shiga kasim sbd tsananin kaunarsa da Omar Wanda sunfi kusanci sosai sbd kasim din Dake matiqar son Omar tin suna qananun kaunar Omar daban take a zuciyar kasim duk da suna son junansu duka su biyar din Amma Omar ya samu qarin matsayin da babu wanda ya samu a Aransa.

Tsakiyar dare guraren karfe uku bayansu da zagayensu yayi tsit Babu motsin komai da kowa sbd runfarsu tana daga baya Baya sosai inda dagasu sai daji.

Dukkaninsu sunyi Nisa a bacci me karfi sbd wahalar dasuka Sha ta shafe kwanaki acikin tsananin zafin Rami da duhu da wahala shiyasa idan ka fito kake bacci sosai sbd wuyar da gangar jiki Tasha.

Ahankali mamman da idanuwansa biyu bacci ba yaji motsi na kusanto runfarsu Wanda motsin yake cikin sanda.

Bude idanuwansa yayi ahankali daga kwancen dayake batareda ya motsa ba Yana sake saurarawa.

Tabbas motsin tahowa ne gurinsu
Tashi zaune yayi ahankali cikin qaramin hasken dayake gurin na farin wata Yana kallan inda lameenu yake kwance Shima idonsa biyu baiyi bacci ba yanajin motsin mamman din.

Wajen rumfar ya juya ya kalla daidai da isowar mutum uku Bai iya ganin fuskokinsu ba sbd ba haske sosai
Sharbebiyar wuqar Dake hannun Daya daga cikinsu idanuwan mamman suka sauka wadda yasan kaifinta Bata fitowa cikin mutum idan an soka batareda ta yanko kayan cikin mutum ba.

Da sauri mamman din ya miqe Yana Ciro tasa wuqar Dake karkashin pilon Kwanciyar sedai kafin yayi yunkurin Isa gurinsu lameenu yayi saurin riqesa daga kwancen dayake Yana kallansa cikin wani irin kallan Daya Saka mamman din kallansa Shima duk da duhu ne.

Zuciyoyinsu bugawa sukeyi sosai da sosai kaman zasu faso kirjinsu daidai lokacinda mutanen sukayi kansu Omar Dake kwance sedai kafin su afka musu kasim ne yafara tashi yayi saurin tarewa Yana ambar sunan Omar da karfi.

A rikice Omar da jamilu suka tashi lokaci Daya suna miqewa tsaye kowannensu na lalabo wuqarsa da wasu irin gora masu qarfin gaske.

Kokawa me qarfi ce ta kaure tsakaninsu suna ambatar sunayen su mamman da Basu ga tashinsu ba Amma Sam Babu motsin su,

Kokarin kashesu mutanen keyi sosai cikin rashin Imani ko kalilan hakama ga duhu basa ganin juna Amma sunqi yadda Dan haka fadan yafara Muni sbd jini ne ke zuba Tako ina a tsakaninsu sbd kaifin makaman hannuwansu bana wasa bane.

Ba qaramar yanka jikin kasim Dana Omar yasha Amma Sam sun qi yadda a kashe su,
Jamilu yanada karfi sosai Dan haka shi Bai jiqata kaman su ba sedai Shima yasha yankan har a fuska.

Mamman da zuciyarsa ke wani irin rawa da jijjiga daga inda yake yasan ko baa fada ba kashe su Omar zaayi to Amma meye amfanin lafewansu Dan akashe Yan uwansu su gaje zinariyar bayan idanma an kashesu din wainda suka kashesun zasu kashesa su tafi dashi su anbarsu a biyu babu an kashe musu Yan uwa Kuma an tafi da zinariyar.

Idan har Yan uwansu zasu mutu to gwara su mutu a hannunsu su su gaji zinariyar Dan kosu da zasu mutu sunfi son su Yan uwansu su mallaketa.

Abinda yake cikin ransa shine yake yawo acikin zuciyar lameenu Dan haka juna suka kalla a lokacinda suke Jin kasim na ambatar sunansu cikin rauni sbd tinanin ko an Riga an kashesu ne basa motsi.

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

AMEENATOU
Mamuhgee

ZafafaBiyar

4
Hankalin Omar tashi yayi mummunan yi rashin Jin motsin mamman da lameenu Dan haka ya fara sarewa Dan kuwa idan har an kashe mamman da lameenu anyi musu mummunan raunin da seelahs zasu bace gaba Daya Dan Suma ba tsira zasuyiba.

Jamilu da Shima yafara gabalaita bazai iya taresu ba ya juyo inda su mamman din suke zai ambaci sunan lameenu kawai lameenun ya daga wuqarsa Dake wani irin daukan ido a duhun ya kutsata gabaki Daya a cikin jamilun take jamilun ya dago jajayen idanuwansa da sukai jajir ya Kalli fuskar lameenu,

Shima lameenu jamilun ya kalla tareda zaro wuqar ta sake kutsata a gefen cikinsa tareda cirowa jinin jamilun na gangara a hannunsa har qafafunsa,
Jajir idanuwansa sukayi wasu irin hawaye masu tsananin zafi suna cika a cikinsu dukkanin jikinsa rawa yakeyi hakama.

Mamman ma tasa wuqar ya Ciro ya daga sama tareda warawa da qarfi zai kutsata gefen cikin Omar kasim da acikin duhun idanuwansa suka sauka akan abinda yake Shirin faruwa yayi saurin karawa da niyar ture mamman din sedai tini wuqar ta kutsa gefen cikinsa ta shige gaba Daya.

Kafin ya zare wuqarsa acikin matune ukun wani ya sake sokawa kasim wuqar daga bayansa take mamman yayi saurin cire tasa wuqar Yana ja da Baya sbd juyowar Omar Yana ambatar sunan kasim da karfi.

Ihun Omar da sunan kasim dayake kira ya Saka aka juyo hayaniyarsu kafin su lameenu suyi kan Omar tini mutane suka yo runfar kowa suka juya kan fadansu kan wainda suka kawo musu farmakin suka illata su sosai Dan haka Koda aka taho da fitilu masu yawa ana duba mummunan lamarin dayayi Munin da Babu me iya kalla Dan kuwa jini ne na kowa da kowa da aka zubar Amma na kasim da jamilu da suka mutu a take shine yake gangara kwance a qasa hakama Omar yaji rauni sosai.

Su kansu mamman yajiwa kansa rauni sosai sbd fita daga zargi duk da a duniyarsu duk Wanda yasan seelahs yasan bazasu taba illata junansuba koda kalmomin bakinsu ba kuwa bare irin wannan mummunan kisan Gillan rashin tausayi da Imani tareda tashin hankali.

Acikin wainda suka kawo musu farmakin Daya Shima take ya rasu sbd raunikan Daya samu dagasu mamman da lameenu sauran biyun ma sunji raunin sosai Dayan har idonsa Daya ta tsiyaye.

Duk tsananin halinda Omar ke ciki kuka yakeyi sosai kaman ransa zai fita da ganin gawar kasim a gabansa da jamilu,
Su kansu mamman da lameenu kuka sukeyi suna ambatar sunan Yan uwansu cikin tashin hankali da dacin zuciya.

Fada ne ya sake kaurewa akan gawawwakin uku sbd zinariyar dasuka bari take aka fara kokawa ana fidda makamai ana ihu batareda ko gawar an dauke daga gurin ba.

Hankalin lameenu Dan mamman tashi yayi suka Kalli juna Dan kuwa bazasu yarda ba bayan uban sukan bayan da akwai aminansu Yan uwansu na alkawarin har mutuwa duk akan wannan zinariyar Kuma suxo su rasata.

Omar gabaki Daya ya fita hayyacinsa sbd tsananin tashin hankali da girgizan wannan balain Dayake shedawa na mutuwar Rabin jikinsu biyu a lokaci Daya Kuma kisan rashin Imani.

Dayasan samun zinari zaiyi sanadin ran yan uwansu daya raki Allah ya hanasu samunta har karshen rayuwarsu.

Fada sosai kaman yaqi ya kaure a take gurin inda har an sake illata wasu mutum biyu an cinnawa rumfar wuta.

Omar da sauri duk rauninsa ya miqe ya dauki jakar zinariyarsu da shi kadai yasa inda suka ajiyeta ya daure a jikinsa tareda Jan gawar kasim ya fara fitarwa su mamman suka kamo ta jamilu suka fito da ita har lokacin kuka Omar keyi sosai Yana kallan gawarsu Yana juya ta yanda zaiyi rayuwa ba kasim hakama yanda zaije ya sanar da mahaifiyar kasim din kasim ya rasu ya barta hakama mahaifiyar jamilu.

Irin kukan dayake yi ne sosai ya Saka da yawa dakatawa daga tashin hankalin manyan Ashalawa din suka iso gurin ana haskawa da fitilu ana ganin Munin lamarin.

Akan gawar su kasim aka tsaya tareda wainda suka mutu duk akan fadan.

Gefe Akai dasu aka rufe Saida safe zaa musu sallah a rufe.

Omar kuwa dole dashi suka tafi Dan basa kariya idan ba Hakan ba Shima kafin safiyar ba samunsa zaayi ba Dan haka Suma su mamman duk tashin hankalin da suke ciki na yanda komai zai kasance Bai hanasu bawa Omar din kulawa ba daga raunikansa ba.

A rayuwar Omar bai taba tinanin zasu samu kansu a irin wannan mummunan yanayin ba duk yawonsu da hadarukan da suka Saba shiga,
Sun dauka zasu samu kyakkyawar rayuwar da iyayensu Basu samu ba Ashe zasuyi mutuwar kaskanci ne wadda iyayensu su Kam basuyiba sunyita ta rufin asiri daidai gwargwado sbd su a cikin rijiyar zinarin suke mutuwa.

Zazzabi ne take me karfin gaske ya rufesa Babu inda Baya kakkarwa a jikinsa gashi jikinsa har lokacin jini na zubar masa.

Mamman ne ya Kalli lameenu
Shima lameenun shi ya kalla kafin suka fara kokarin cigaba da tattalinsa suna basa kulawa da share masa jinin fuskarsa suna kukan rashinsu jamilu.

Duk da antaho dasu Omar din bangaren manya kafin safe fadan Ashalawa din be kwanta ba saima qara girma yakeyi Daman lokuta da dama karamin fada ko fada kadan sai a tayarda fadan da fitinarsa zatai babbar illa ga kowa sai anyi rashin rayukan da dama shiyasa koyaushe zinariyarsu Bata karewa habbaka takeyi.

Fatinar Bata lafaba ko kadan take ta zama babba Ashalawa ta dauki hayaniya,
Koda asuba tayi sallah kawai Akai turawan sukace tafiya zasuyi sbd tashin hankalin dayaketa sake rikicewa.

Tini sukai waya helicopter zai taho ya daukesu ya fidda su dajin.

Babban tashin hankalin Daya Saka mamman da lameenu kusan Yanke jiki a gaban manyan Ashalawa da turawan da zasu siye danyar zinarin shine Sanar dasu gabaki Daya tarin danyar zinarin kasim ya bawa Omar tin a daren jiyan da Akai rubuce rubuce komai sunan Omar aka Sanya sbd Omar shine zai riqe musu dukiyarsu dashi dashi din Dan haka gaba dayanta ta Omar ce gashi kaf acikinsu ukun da suka samu me yawan gasken ta kasim din tafi ta kowa yawa hakama ta Omar din Dan haka lissafinta ma da aka hada din hankali bazai taba daukaba.

Wani mummunan hayaqin tashin hankali ne mamman yaji Yana fita kunnuwansa Yana gurbata numfashinsa dake fita da daqyar.

Lameenu kuwa manyan idanuwansa ya fiddo waje suna sauyawa zuwa jajir hannuwansa na daukan rawar tashin hankali yayi saurin qanqame hannuwan Yana kasa boye firgicinsa duk yanda yaso.

Juyawa yayi ya Kalli inda mamman yake zuciyarsa na dauka wani irin radadin zafi da ‘dacin baqin cikin da Bai taba sanin da akwaisa ba.

Akan Omar dukkaninsu suka mayar da kallansu lokaci Daya zuciyoyinsu naci da wata irin wutan tafasar zuci.

Me kenan?
Omar sukaiwa kisan su kasim din kenan tinda shine yafi kowa arziki a Ashalawa kenan yanzu ko me?
Me Hakan ke nufi da cewan kasim ya bawa Omar taskar arzikinsa gaba Daya?

Lameenu a tasa zuciyar kuwa abu Daya ya sani shine tinda suka riga suka kawar dasu kasim akan zinariyar to kowama yayi musu shamaki da ita inda suka aika su jamilu can zasu aika koma waye,
Sun Riga sun fara aikinda Babu tsayawa sai sun mallaketa,
Omar bazai taba hanasu mallakarta ba Dan zai musu zarran da bazasu taba kamosa ba har abada Kila,
Tayaya zasu kallesa a samansu su suna qasansa bayan sune sukai dirty work din Daya basa Arzikin dukiyar.

Sake kallan juna sukai shida mamman har lokacin Babu Wanda zuciyarsa ba tafasa takeyi cikin tashin hankali da tsoron tabbatuwar abinda aka fada din ba.

Omar kuwa har lokacin Yana cikin halin rashin lfy Daya rufesa da kukan rashinsu kasim Daya kasa dawo dashi daidai.

Zinariyar kuwa baa tsaya komaiba aka ware ta Omar da kasim aka ware masa abarsa shine zai kula da mahaifiyar kasim Daman tamkar itace ta haifesa yake.

Ta jamilu kuwa batareda tinanin komai ba ko bin tsarin Daya kamata ba haka aka Kara rabe musu su uku,mamman da lameenu Da Omar din Wanda yace ya yafe musu aka barmusu su biyun.

Kason da suka samu ba qaramin kaso bane da zai ishesu Gina rayuwarsu cikin wadata sosai da Kwanciyar hankali tareda samarwa Kai suna da wani matsayin ma Amma duk wannan Bai saukar da mummunan nauyin Daya Riga ya danne zuciyarsu ba data rikide a dare Daya Takoma wata sabuwa daban da kadan Baya isarta.

Gabaki Daya baqin cikin duniya ba basusan dandanonsa ba shine dabaibaiye da zuciyoyinsu akan mahaukaciyar arzikin da suke kallan Omar dashi Wanda basajin zai taba sauka matiqar ba sune suka kasance mallakinta ba Kokuma rabinta ma.

Tafiya zaayi da Omar sbd baturen dayayi musu alkawarin Basu irin rayuwar da suke so shi da kasim kafin rasuwar kasim din Dan haka ana rufe su kasim tashin hankalin Omar ya qaru sbd Kai tsaye su mamman sukace ba zasu bisu ba su zasu zauna anan su sake samun zinariya kafin su biyosa.

Su biyar din basu taba rabuwaba tinda suke a rayuwarsu sai wannan ranar da biyunsu suka bar duniya gaba Daya sai Kuma yanzu da zaa tafi da Omar abarsu Badan sunso ba sai Dan ana son nuna musu fin karfi.

Mr Jaden da tin farko Allah ya Saka masa kasim arai sosai fiyeda kowa a Ashalawa sbd ladabinsa da nutsuwarsa data fita daban haka kawai yaji bazai iya barin Omar ba a Nan bayan rasuwar kasim Dan yariga yayi musu alkawari hakama zuciyarsa Bata yardar masa barin Omar a tsakanin mamman da lameenu ba Dan haka baiyi tsaiko a tafiyar tasu ba duk yanda Omar ke cikin tsananin tashin hankalin rabuwa dasu mamman Amma Shima yanason cika burinsu shi da kasim na rayuwar Kwanciyar hankali da nutsuwa tareda wadatar ilimi Dan haka yabi Mr Jaden din tinda su mamman din zasu biyo Daga Baya.

Mamman da lameenu tamkar tsokar jininsu ce ake yanka ana rabasu da ita sukeji a lokacinda suke kallo Omar zai tafi da tarin arzikin da suke ganin sunada cikakkiyar haqqi akanta tinda sune sukai aikin kawar da me ita din Dan haka kukansu da baqin cikinsu na tafiyar akan Hakan ne sedai zuciyoyinsu ne kadai ke kika Banda idanuwansu da suka bushe Babu komai Dake cikinsu bayan radadin Jan bacin Rai suna kallo har Mr Jaden Dake riqe da hannun Omar ya jasa suka nufi filin da helicopter din dazai daukesu yazo ya daukesu suka bar dajin Ashalawa.

MAMUH

TOOTOOHOT

JAMAAL JEEY SEELAH

AMEENATOU SEELAH

ZAFIN KAI

LOVE

DEEP

ROM

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

Join our WhatsApp group here

AMEENATOU
Mamuhgee

ZafafaBiyar

5
Lagos suka Isa da Omar Wanda tini zazzabi da ciwo me karfin gaske ya rufesa Wanda idan suka so a lokacin Mr Jaden zai iya karasa illatasa ya gudu da dibbin dukiyar Amma Sam har cikin ransa bayajin zai iya Hakan Dan take kaunar Omar din ta cikesa musamman da a bayyane mutuwar Rabin jikinsa ta tabasa wadda ba zai taba mantawa har abada ba,Dan ko Babu kauna irin shaquwa da rashin rabuwarsu tin haihuwa dole kowannensu ya rabu ciki kuwa harda su mamman duk da babu Wanda yasan sune sukai kisan.

Mr Jaden na da gidan kansa Daya mallaka a cikin garin Lagos me girman gaske Dan haka ba asibiti ya nufa dashi Kai tsaye ba gidansa dayayi kama da Akira mansion suka nufo bayan yasa ankira likitan da zaizo ya duba Omar cikin gaggawa.

Isarsu Babu Bata lokaci aka shige da Omar har Daya daga cikin dakunansa Dake sama har cikin toilet take manyan yaransa biyu Ahmed da Aron suka gyare Omar din tsaf suka tsaftace sa daga datti da jinin jikinsa da duk ya bushe.

Kusan Omar din Baya hayyacinsa Dan haka suna gama gyarasa kusan gajeran wando sabo kadai suka Saka masa sai aka kwantar dashi a lafiyayyar gadon Dake dakin tareda ragewa AC karfi suka fice daidai isowar likita da nurse namiji Daya sai Mr Jaden.

Bude musu dakin Ahmed yayi Yana matsawa gefe suka shiga.

Kallansa Dr yayi ya raunikan jikinsa sai Kuma zazzabin gaske me qarfi dayake Saka jikinsa wani irin jijjiga.

Babu Bata lokaci ya fara dubasa cikin sauri sbd ganin Yana buqatan taimakon gaggawa.

Da farko akwai inda yake buqatan dinkuna sosai a jikinsa sbd deep yanka Daya samu sosai Dan haka su aka fara duk da an masa allura Amma Yana cikin azaba sosai sedai ko motsi Baya iyawa har aka dauki tsawon lokaci sosai aka gama.

Ruwa da wasu alluran akai masa tareda rubuta maganin da zai buqata Sha suka fito akan zaa daukarwa Omar din nurse me kulawa dashi.

Bayan tafiyar su Dr sai alokacin Mr Jaden ya samu kansa Shima yaje yayi wanka yaci lafiyayyar abincin da aka jere masa su a dining ya koshi ya kunna wayoyinsa ya ringa wayoyi tsawon lokaci kafin ya shige yayi Kwanciyarsa yafara baccin Hutu.

Omar Bai farfado ba sai bayan kwana Daya da wuni Wanda har hankalin Mr Jaden yafara tashi sai gashi ya farka Kuma lafiya kalau Babu zazzabi ko wani ciwon sai raunikansa da Suma zasu warke a hankali.

Kulawa dashi sosai nurse dasu Ahmed sukai harya samu damar yin wanka da kansa yayo alwala yazo Ahmed dayake musulmi Dan uwansa ya nuna masa gabas yayi ramakon sallolin dasuke kansa duk da ba wani ilimi ko sani akan Addini suke dashi sosai ba Amma dai sunsan sallah Kuma basa tsallaketa.

Ko kafin ya gama sallolinsa tini aka shigo da abinci aka jere masa su lafiyayyu masu Kara lafiya da drinks masu sanyi kadan.

Aron ne ya shigo Shima da wasu sabbin kayan sakawar bayan wainda aka kawo masa kafin ya fito wanka.

Yana idar da sallan abincin ya kalla tareda juya idanuwansa Yana sake kallan dakin dayake ciki din Wanda Basu taba sanin akwai tsari irinsa ba duk yanda suke hararo rayuwar kudi da Jin dadi Basu dauka haka abin yake ba a zahiri.

Tamkar mace haka yaji idanuwansa sun ciko da wani irin Hawaye masu tsananin zafi da radadin rashin su kasim a duniya daidai lokacinda ya kamata su ji dadi,
Bai taba sanin samuwar arzikinsu zai tafi da jini da rayuwar Yan uwansu Rabin jikinsu ba da tini ya Dena rokarwa kansa arzikin.

Su kasim sun bar duniya basa tareda shi hakama su mamman dasuke raye a yanzu basa tareda juna,tayaya zai fara rayuwa Babu su,Suma su mamman din tayaya zasuyi rayuwa Babu shi din.

Share hawayensa yayi yana daga hannuwansa yayiwa iyayensu dasu kasim adduar dacewa da Rahama Suma su mamman yayi musu adduar Allah ya Basu abinda sukai burin samu acan Ashalawa din kafin su baro.

Miqewa yayi daidai shigowar Ahmed Wanda kaman shine Mr Jaden ya bawa Ragamar kulawa da Omar yanda ya kamata tinda sune suke Addini Daya da juna.

Kallansa Ahmed keyi Yana Dan sake fuska cikin kulawa ya sanar dashi ya taso yaci abinci sbd lokacin Shan maganinsa yayi.
Ba musu Omar din ya taso sbd su Ahmed din sun girmesa sosai Dan alama Dan zasuyi shekaru talatin su zuwa sama shikuwa a lokacin ne suke shekarunsu na ashirin zuwa da Daya.

Abincin kudi Kai tsaye zai kira abinda yake kalla a gabansa da sunan abincin,
Brown basmati rice ce da aka dafa da abubuwan da bama zai iya gane me dame bane a ciki Se brown chicken breast a jere cikin wata glass bowl daban.

Ahmed ne ya basa kwari gwiwan fara cin abincin Wanda Yana fara Kai spoon na farko bakinsa idanuwansa suka ciko da Hawaye zuciyarsa na karyewa da tino Yan uwansa su mamman ko sun samu sunci abincin Daren kuwa kokuwa ma kila suna can cikin azabar duhu da zafin ramin gurin Gina.

Ahmed Dake kallansa Yana tinanin Allah me bawa Wanda yaso,
Gasunan dai sunata Fadi tashin nema Amma ga yaro qanqani kaman Omar Allah ya basa Arzikinda zasu lalace a karkashinsa gurin bauta masa kaman bayi.

Harya ci abincin ya gama Hawaye ne ke tsiyaya daga idanuwansa da sukai jajir Babu farin ciki ko kadan a ransa Dan kuwa rayuwar da zai fuskanta Babu seelahs ko Daya a cikinta bazai taba farin ciki ba duk Jin dadin dazai samu acikinta.

Bayan gamawarsa Ahmed da kansa ya kwashe kayan ya fice dasu tareda dawowa sukai sallahn ishai a tare dakin tukuna ya fito ya sauko ya barosa ya sake samun hutawa kaman yanda Mr Jaden yace abarsa ya huta sosai ya dawo daidai tukuna.

Zaune yake shiru har kusan dare sosai kafin ya kwanta bacci ya daukesa Bai farka ba sai asuba.

Bayan sallan asuba da baisan time ba yasan dai lokaci yayi
Yana idarwa sake kwantawa yayi sbd maganinsa akwai masu Saka bacci sosai Dan Mr Jaden ya sanarwa Dr Omar din kaf rayuwarsa Baya samun baccin Daya kamata musamman a wannan lokacin shiyasa aka rubuta hadda maganin bacci.

Washe gari ma haka ya sake wuni daga cin abinci sai sallah Se bacci,
Daga Ahmed Se Aron ne kadai suke Dan shigowa Dan su Dan debe masa kewa Amma Sam Babu walwala ko farin ciki a tattareda shi.

Mr Jaden baya zama kwata kwata sbd komawa da zaiyi qasarsa Poland Kuma duk yanda yaso tafiya da Omar abin bazai yiyuba a yanzu Dan haka dole zai barsa yaje ya dawo kafin can anyiwa Omar din komai da komai na id cards da sauransu.

Kafin tafiyar Mr Jaden cikin kwana biyu yayi kokarin ganin Omar yafara sakewa sosai Dan yanason inganta rayuwarsa fiyeda yanda ake tinani,
Yanason mayarda rayuwar Omar abar alfahari ga Yan uwansa Da Kuma duk Wanda zaiyi muamala dashi,
Yanason Omar ya samu ingantacciyar rayuwar da har abada bazai taba tinani ko shaawan komawa Ashalawa Koda kuwa ziyara ne bare Dan wani abin daban Dan haka Babu Bata lokaci ya nema lawyernsa na Nan Nigeria me zaman kansa qwararre Akai rubuce rubuce akan zallan tsananin dukiyar Omar wadda kusan yawanta takusa ta dukiyar Mr Jaden din Dan haka a rubuce Mr Jaden da Omar abokanan kasuwanci ne da dukiyarsu ta Hadu tareda adadin ta kowa.

Omar ya amince da Mr Jaden dari Nisa dari sbd kasim ya yarda dashi sosai da sosai kafin ya rasu Dan haka Shima ya miqa dukkanin yardarsa ga Mr Jaden batareda Jin komaiba aka basa takardu duka ya Saka thumbprint nasa aka sealing.

Kafin tafiyar Mr Jaden duk wata sutura tin daga kan underwears da singlet da qananun kaya da manya har turaruka da mayukan da Omar zaiyi amfani dasu da takarman da zai Saka da duk wani abin buqata na rayuwa Saida aka siyosu tsadaddu masu kyau da tsari aka zuba a dakinsa Wanda yake sama babba da toilet dinsa.

Abu na farko daya bari shine zasu fara da basa ilimin Daya kamata Dan haka babban Dan amanansa Ahmed da Aron sune yabarwa komai a hannunsa Dan haka bayan tafiyarsa Id cards aka fara yi masa da passport da banki da komai sai da Akai masa kafin aka tanada malamai biyu masu kyau aka daukar masa Dan karatun da aka fara Babu kama hannun yaro.

Tin tinanin Yan uwansa na dauke masa hankali Yana rabuwa gida biyu har su Ahmed suka Bude masa wuta sosai akan karatun Wanda yakejin kaman bazai iya ba sbd Bai fara ba tin Yana kankani harya zo yafara Maida hankali sosai da sosai Baji ba Gani Dan kuwa Aron Sam Baya masa da sauki akan karatun Dan Mr Jaden ya Basu tabbacin akan karatun karsu masa da sauki ko kadan sosai yake buqatan Omar ya San kansa ya tsayu da kansa.

A bangaren Addininsa ma sosai Ahmed ke taimaka masa Dan haka ya sake zaucewa akan karatun ba wasa ko kadan.

Ahankali ahankali ya fara Bude kansa sosai komai na shiya yanda ya kamata Dan kuwa tamkar hannun sojojin koyan aikin soja aka miqasa a hannunsu Aron Babu wasa ko kadan akan lamarin nasa.

Babu ranar da Baya kewansu mamman da lameenu dasu yake kwana yake tashi a ransa sedai Babu yanda zaiyi tinda baimasan ta yanda zai ji daga garesu ba bare ganinsu dole sai ranarda Mr Jaden ya dawo shine kadai yasan Wanda zai kira a ashalawa a hadasa dasu a waya suji junansu hakama shi kadai ne Wanda yasan yanda zaiyi yakaisa ashalawa din idanma ganinsu yakeson yi gashi Mr Jaden kullum sukai waya basa tabbacin bazai dawo daukansa ba sai yafara fahimtar karatu ya iya turanci Dan haka ya sake Maida hankali sosai akan karatun.

Bayan kusan watanni masu Dan yawa rayuwarsa ta sauya cikin kankanin lokacinda baiyi tsammani ba shi kansa,
Ya sauya sosai ya samu Kwanciyar hankali da nutsuwar rayuwa duk da akwai kadaici a tattareda shi sbd daga shi sai su Aron da masu aikin gidan ne suke rayuwa,
Baya muamala da mutane sbd koyaushe Yana gida sai Kuma idan sun fita yawon Shan iska ko siyayya ko kallan ball da sauransu Wanda sosai ake kokarin yin duk abinda zai sakashi Jin walwala ko makamanciyarta.

MAMUH

AMEENATOU

DEEP

JAMAAL JEEY SEELAH

BLACK MONEY

LOVE

CRAZY

LAHOT

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

Join our WhatsApp group here

AMEENATOU
Mamuhgee

ZafafaBiyar

6


Babban abinda yafara sauyawa sosai a rayuwar Omar shine harshen yare,
Daga Aron har Ahmed dayake musulmi basa Jin Hausa Daman tin farko da dubaru suke magana dashi Dan haka da karfi da yaji yaren turanci ya fara kama bakinsa Dan kuwa ko Ahmed dayakewa kallan nasa ba bahaushe bane yaren igala ne da aka haifesa a Lagos ya tashi a Lagos Dan haka tini Omar ya sake ya fada yaren turanci Shima Yana cabawa.

Sabo da shakuwa dole ya shiga tsakaninsu duk da Yana girmamasu a matsayin wainda suka girmesa su Kuma suna kulawa dashi kaman jininsu Dan kuwa Babu abinda bazasu iyawa Mr Jaden ba ko Yana kasar ko bayanan Dan shine gata da rufin asirinsu da iyalansu.
Mutum ne shi Daya inganta rayuwarsu sosai yanada alheri baida rowa Sam shiyasa suka zama Yan amanansa Dan ya dade a Nigeria shekaru sosai anan yake huldodinsa da yawansu.

****Lokaci yaja Omar tini ya kwana biyu da shiga makarantar da ake kira yaqi da jahilci wadda kusan acan kansa ya qarasa budewa yanzu ba laifi Yana iya abubuwa wa kansa da da sama wainda su Ahmed suka koyar dashi da Kuma iliminsa Daya fara basa,
Shine yake zuwa da kansa yaje ya dawo da mota batareda ankaisa ba hakama Kuma Yana zuwa banki ya cire kudi da kansa batareda wani ya raka sa ba hakama siyayyar abubuwan buqatansa,

A rayuwarsa yanzu abu biyune ya rasa masu damun zuciyarsa kowanne dare shine rashinsu mamman da lameenu a tareda shi sai Kuma rashin Mr Jaden da kusan zuwansa biyu Yana komawa batareda shi ba Amma yanzu Kam da komai nasa na tafiya ya kammala haka yayi bankwana dasu Aron ya tafi yanajin kaman ya rabu da Dan uwansa na jini
Amma Ahmed dashi suka tafi sbd shi har lokacin baiyi aure ba Bai da iyali sabanin Aron yanada family Dan haka shi aka barsa da kulawa da gidan suka koma Poland kwata kwata.

Da farko yaso ganawa dasu mamman kafin tafiyarsu Amma ba lokaci Dan haka dole Mr Jaden yayi masa alkawarin zaa kawo su Suma Nan Lagos su samu Dan ilimin shigowa mutane kafin akawosu Poland inda yake su hade suyi karatu kamansa.

Wannan alkawarin ne ya kwantawar da Omar hankali Wanda har sai dayayi magana dasu mamman da waya daga can Ashalawa suka basa tabbacin suna Nan tafe Suma sun shirya tsaf.

Farin ciki da nutsuwan zuciyar Daya samu da Jin Hakan ya Sanyashi kwantar da hankalinsa daga Dan tsoron Daya shiga na samun kansa a wata qasar wata duniyar da baisan da ita ba Dan haka gaba Daya yanzu ya kwantar da hankalinsa ya Maida akan karatunsa dayake Dan cimma buri ya samu dawowa yaje dubo mahaifiyar Kasimunsa da mahaifiyar jamilu.

A bangarensu mamman kuwa wata sabuwar duniyar rayuwar Baji ba Gani suka Bude a Ashalawa Dan kuwa gasu da kananun shekaru Amma Kuma suna cikin yan lamba Daya na rashin imanin Ashalawa da bushewan zuciya.
Duk abinda suke son samu sunata samunsa da nasu da Wanda na karfin hali ne duk sun hada sun mallaka Dan haka suka Tara wata irin danyar dukiya da Suma basusan ya zasu sarrafata ba,
Jini da rayukan da suka tafi Dan Saka hannunsu sunada Dan yawa a ashalawa Dan haka sunansu ya sake habbaka duk da Babu sauran Amma sunan seelahs Kam a Ashalawa yasake samun daguwa.

Basuda niyar barin Ashalawa sbd so suke ahankali ahankali sai sunkai sune manyan Ashalawa da zasu kwantar da Wanda sukeson kwantarwa su take su kashe.,suna son sukai sune manyan da acikin Ashalawa ko digon zinari bazata fita ba batareda izininsu ba da Kuma kasonsu.

Zuciyar mamman da lameenu ta rikide daga seelahs ta koma wata abar daban da babu Wanda ke iya gane Menene a cikinta ba sai su kadai da yanzu sunfi kowa sanin zuciyoyin junansu.

Dukiyar hannun Omar Bata taba fita daga zuciyarsu ba Kona sekan Daya Dan kuwa itace har yanzu a qasan zuciyoyinsu da basajin har abada idan ba mallakarta sukai ba zasu ji abinda yake kirjinsu ya fada.

Duk wani mataki da sukeson takawa a rayuwarsu Dan mallakar dukiyar ne wadda duk yanda suke daukan Rai baa bakin komaiba yanzu suna mallakar zinariya haryanxu Basu samu abinda yayi Koda Rabin na Omar din bane Dan haka suke sake nutso a duhun zuciya.

A ranar da sukai waya da Omar ya sanar dasu kyakkyawar rayuwar dayake gudanarwa tareda nutsuwa da tarin wadata Jin sukai gabaki Daya hankalinsu ya tashi daga Ashalawa ya koma akan samarwa kansu ilimin da zai Basu ikon mallakar abubuwa da dama daga Omar din Dan haka take suka amince da tahowa inda yake din.

Abinda Basu sani ba shine Omar yariga yabar qasar Mr Jaden ya tafi dashi Poland Dan haka bayan isowarsu sunji ciwon Hakan sosai Amma dai sunsan koman Daren dadewa zasu hade dashi Kuma abinda suke son kota halin yayane sai sun mallaka Koda abubuwa da dama zasu faru.

Aron ne mutum na farko daya fara banbance halinsu Dana Omar Dan kuwa su Babu sauki ko kadan a kulawa dasu kamanshi,
Tinda suka zo yaketa iya kokarin kulawa dasu da karatunsu sedai kwata kwata Babu sauki.

Saida suka shafe watanni suna cin banza a mansion din akai musu komai kaman yanda akaiwa Omar tin daga Id cards da passport da acct suka fara wayewa da harkar kafin Mr Jaden ya hadasu da abokan huldansa da lauyoyi na daban suka fidda dukiyarsu me yawan gaske ta danyar zinariyar Akai huldarta anan ne suka Hadu da Mr Owolowo bayaraben da shima ya goge a harkar danyar zinari ta gurbatacciyar hanya Dan haka tini ya janyesu daga Mr Jaden suka koma gurinsa acan suka fara gogewa da karatu da harkar zinari ta hanyar ilimi da wayewa tini suka bar qasar suka gaba Daya suka bisa Angola acan suka fara karatunsu sosai Kuma suna kasuwancin zinarin sosai tareda wasu huldodin na kasuwancin Daya kamata sabaninsa.

Ahankali ahankali Suma dukiyarsu tafara habbaka kaman yanda iliminsu da wayewarsu ke habbaka tareda sunayensu.

Kaman yanda rayuwa ke tafiyar musu daidai haka rayuwa ke tafiyarwa Omar daidai Wanda nasa ilimin yafi nasu zurfi sosai hakama gaba Daya shi tasa rayuwar tamkar Dan gata yake gudanar da ita Dan kuwa Mr Jaden ya zama tamkar uban Daya haifesa sbd tini ya qara masa da sunansa akan nasa Dan ya zama asalin Dan qasar Kuma kaman yanda da yawa basu San Mr Jaden ya taba haihuwa ba sai suke dauka Omar din dansa ne Daya Haifa a Nigeria sbd zaman da yayi acan sosai.

Matar Mr Jaden da farko ta qyamaci Omar Amma da shekaru suka fara ja ya goge ya koma tamkar baturen Shima hakama nutsuwa da tsananin son dayake wa mr Jaden kamar asalin Dad dinsa ya Sakata itama amincewa dashi a matsayin ‘da.

Dukiyarsu Babu Haram Babu cuta ba cutatarwa kasuwanci akeyi da ita sosai tini ta qara haukacewa da habbaka ta bangare Daya Omar ya fara tsayuwa sosai a business ga bangare Daya ya musuluntar da iyayen nasa Mr and mrs Jaden Dan haka suka sake samun nutsatsiyar rayuwa.

**Bangaren su mamman rayuwa tayi musu yanda suke so Tako ina daukaka suke sake samu da qananun shekarunsu Dan haka suna cikin matasan Dake tashen arziki me yawa,

An wayi gari abokin huldansu Mr Owolowo ya mutu sanadiyar bugawar zuciya ake tinani sbd jinin da aka samu ta hancinsa Yana fita da kunnuwansa Amma dai baa tsaya wani dogon bincike ba aka rufesa aka bar maganar daga Nan suka tattara suka bar Angola suka dawo Nigeria suka Gina kansu Amma dai basa wani zama suna gurin Omar Wanda gabaki Daya idanuwansu da zuciyoyinsu sake shiga tashin hankali sukeyi idan suka ga rayuwar dayake ciki da irin mugun tashin da arzikinsa keyi.

Shekarar da Omar yayi graduating daga karatunsa tareda su Akai biki na burgewa da Mr Jaden ya hada masa Wanda ya Tara manyan abokan huldansu da families nasu.

Su kansu su Omar din cikin farin ciki suke sosai sbd burinsa ya cika ayau ya samu kansa cikin ilimi me yalwa da Kwanciyar hankali tareda wayewa tamkar bashine me yawon kauyuka da daji ba.

Su kansu mamman sauyinsu a bayyane yake Dan ma sunfisa budewan ido sbd sunfisa yawon qasashe yanzu tinda kusan su dasu ake yawon duk business dinsu musamman yanzu da Babu Mr Owolowo sune akan dukiyarsu da tasa da suke cinye fiyeda Rabi.

A gurin dinner din mamman ya kalla idanuwansa akan baturiyar qasar data dauki hankalinsa Badan komaiba sai Dan sanin mahaifinta akan sunan dayayi akan harkar zinarin kasar Amma ya tsufa sosai yanzu hakama ko gida baa fitowa dashi mahaifiyarta ce Akai itama mahaifiyar tata ta tsufa.

Da farko lamari ne da bazai taba yiyuwa garesa ya samu baturiyar Amma Kuma duba da Shima kudin ne dashi sosai ba laifi hakama yanada iliminsa da wayewarsa tareda kayansa Dake Jan raayin mata da yawa sosai akansa yasa Hakan zata iya yiyuwa.

Babban abinda yabawa kowa mamakin bayan kwana biyu da dinner din shine soyayyar mamman da Aleena wadda Mr Jaden da mahaifiyar Aleena din da Omar sukai alkawarin hadasu aure Amma Omar na ganin yanda mamman ya mutu akanta take ya Hana Mr Jaden sake tada maganar aurensa da Aleena sbd yayiwa Dan uwansa mamman farin cikin samun mace kaman Aleena duk da ba musulma bace Amma zuciyarta nada kyau musuluntar da ita bayan auren abune mara wuya.

Lameenu dayafi kowa sanin zuciyar mamman Baiyi mamakin farin ciki da tsananin son da mamman din kewa Aleena ba da yanda ya ringa sakin dukiyarsa kaman baisan zafinta ba wadda bawai damuwa Aleena tayi da dukiyar ba sbd shi takeso Kuma duk abinda mamman yakedashi tanada abinda yafisa fiyeda a kirga.

MAMUH

JAMAAL JEEY SEELAH

AMEENATOU

DEEP

ROM

TOO HOT

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

AMEENATOU
Mamuhgee

ZafafaBiyar

7


Iyayen Aleena sunada wani irin qyanqyami da kabilanci ga Wanda basu sani ba Sam duk da suna kallan su mamman din a matsayin family na Mr Jaden sedai Sam Sam Basu aminta da mamman ba duk da Shima fari ne sosai kaman Omar Kuma kyakkyawa daya kusa ma yafi Omar din kyau amma dai hankalinsu yafi Kwanciya dari bisa dari akan Omar dasuke ganin kaman a taredasu ya taso duk da basusan yarinyartasa ba Amma ai a tinaninsu a hannun Mr Jaden ya taso Kuma dansa ne Daya haifa acan.

Aleena a zuciyarta mam kaman yanda yanzu ake kiransa ya kwanta mata dari bisa dari sbd yakai duk mataki da tsarin datakeson namiji yakai mata,
Yanada kyau sosai da wayewan da baya shakka ko tsoron kowa,
Hakama yanada class Wanda taku ne Daya iya abinsa tinda ya samu kansa sabuwar duniyar datafi wadda suka fito,.yanada ilimi da dukiyar kansa da bazai taba damuwa da tata dukiyar ba hakama ya Bata tabbacin shine zai tattaro ya dawo qasar da zama bazai taba daukanta zuwa koina ba Dan haka taji Hakan ya mata.

Omar Bai taba tinanin akwai Kokuma wata manufa zata shigo cikin maganar auren mamman da Aleena ba dan haka yafi kowa farin ciki
Su kansa su mum dinsa sunyi farin ciki daga baya Daya nuna musu Yanason su nuna farin cikinsu da Hakan.

Ansha fitina da damuwa sosai akan iyayen Aleena su amince Amma suka qi musamman mahaifinta Sam Sam Bai amince ba.

Har Aleena ta cire Rai sai kwatsam Dad din nata aka wayi gari ya mutu a dakinsa kwance Yana Yana bacci.

Sun shiga tashin hankali sosai sbd Aleena na tsananin son Dad dinta fiyeda mum din shiyasa ma ta hakura da maganar auren mamman bawai Dan shekarunta basu Kai tayi abinda ranta yakeso ba sai dan Dad din kawai.

Jadens family sun shiga tashin hankali da firgicin mutuwar Mr Harris sbd kusancinsu da zamtowansu family friends tin tsawon lokaci me tsayin gaske.

Omar dasu mamman sun shiga damuwa sosai sosai Dan haka Omar ma yaji Yana sake son auren Aleena da mamman Dan ta samu musulunta ita da mum dinta kafin Suma su rasa wannan damar kaman Mr Harris.

Shi kansa mamman yasan yanzu Kam Babu wata shamaki da zata shiga tsakaninsa da auren Aleena musamman yanzu da nauyin komai na kamfanin Dad dinta da uban dukiyarsa zasu dawo kanta.

Mutuwar Mr Harris ya taba Aleena da mum dinta sosai musamman mum din da Bata sake lafiya ba
Ba Bata lokaci Aleena ta sake amincewa mamman sbd tsananin kulawansa da tattalin dayake nuna musu ita da mum dinta.

Sunyi register na aurensu da komai hakama auren musilunci suka fara yi wedding dinner Daya sukai bayan daurin auren da kwana Daya anan
Duniya ta sake sheda auren nasu Wanda da yawa manyan mutane da respected families Dake tareda su kusa da nesa duk sun samu halartowa.

Babban sa’ar da mamman yasake tsintar rayuwarsa a ciki shine gabatar dashi da Mum din Aleena tayi ga abokanan huldansu na business da sauransu,
Da yawa ta gabatar dashi take ya nutsu ya fara samarwa kansa matsayin da suna a cikin manya ta hanyar nuna nutsuwa da tinani tareda sanin ya kamata harma da bayyanarda tsananin kauna da son dayakewa Aleena da mahaifiyarta da yanzu shine zai tsaya musu.

Da yawan mutane sun yaba dashi Dan take take aka ringa recognizing nasa shida lameenu Wanda yake gabatarwa a matsayin Dan uwansa Kuma abokin tasa huldar.

Omar Baya buqatan gabatancin kowa sbd shi din sananne ne a cikinsu tini Kuma duk yanda suka yaba dasu mamman Omar ne a ransu da idanuwansu fiyedasu.

***Bayan auren mamman da Aleena ya nutsu ya duba ya karanta da kyau yaga duk inda yake tinanin dukiyar Aleena abin ya wuce Nan Dan haka ya sake iya takunsa Dan kuwa son dayake nuna mata tini ya qarasa gamawa da ita da mum dinta take suka Dorasu akan dukiyarsu sbd ita Aleena batada time sbd karatunta na likitanci da saura kadan ta kammala.

Lameenu ya koma Nigeria sbd gudanar musu da ayyukansu na can Kuma Shima Yana komawa Babu Bata lokaci yayi aure Wanda daga mamman har Omar sun halarta angama sun dawo.

Bayan dawowarsu ba jimawa Aleena ta fara aiki a Special Care hospital din data Gina me tsarin Daya dauki kudi masu yawan gaske da hankalin mutane tareda zuba qwararrin doctors da qwararrin nurses da ma’aikata.

Fara aikinta yayi daidai da bayyanar ciki a tareda ita Wanda ya Saka mahaifiyarta da ita murna sosai kamar me
Sedai duk murnarsu basukai ko Rabin ta mamman ba da Daman haihuwar yake Jira dukiya ta tabbata tasa Dan kuwa abinda zata Haifa shine zai gaje dukiyar to Kuma ai shine uban abinda zai Haifa din.

Omar yabar Poland Yana UK gurin qaro ilimi akan harkar business sosai Wanda Shima acan ya Hadu da tasa matar yar asalin kasar Jamaica tin Yana can suka Kai karshe sedai shikam a Jamaica din sukaje Akai aurensu Kuma kowa ya samu halarta hadda Aleena da mum dinta duk da auren musulmai ne sun halarta.

Bayan auren daga Omar din har Nur dinsa a UK suke sbd itama karatun takeyi Amma ita yanzu ne ma ta fara a matakin farko take.

Lameenu na Nigeria,
Mamman na Poland
Omar na UK,
Haka kowannensu yake gudanar da rayuwarsa bisa tsari da yanda yake Sonta Dan kuwa kowa takai masa iya iyakar yanda yakeson.

Haihuwar Aleena ce ta sake hadasu guri Daya sbd farin ciki Mai tsananin gasken da suka samu rayuwarsu a ciki da karuwar seelahs,

Duk wani Wanda yake Hulda ko yasan seelahs Saida ya sheda farin ciki me tsananin gaske da sukeyi da samun haihuwar farko a cikinsu Kuma Allah a Karan farko Saiya albarkace su da samun ‘yan biyu duka Maza.

Mam Bai taba dauka ma zaiji irin farin ciki da tsananin kaunar yayan fiyeda komaiba Saida aka haifosu ya rungumesu jajaye dasu kaman wasu taurari.

Mum din Aleena har hawayen farin ciki ta ringa yi tsabar murna kusan tata dukiyar mallaka musu ita tayi a matsayin will dinta idan ta mutu a Basu 60% na dukiyarta sauran 30 a bawa Aleena din.

Wannan will din ba qaramin dadi yayiwa mam ba Dan haka soyayyar ‘yayansa ta ninku a ransa Dan kuwa ya tabbatarda sune mukullin arzikinsa mara adadin dabai samu riqewaba sai yanzu,
Sune sa’arsa Daya Dade Yana jira ta shiga hannunsa,
A yanzu Daya samesu yasan dukiyar Aleena tasa ce itama tinda ta mahaifiyarta ta zama tasa burinsa Daya ne ya rage a rayuwarsa shine mallakar dukiyar Omar wadda duk abinda zai mallaka idan ba ita suka mallaka ba bayajin zai iya numfashi me dadi.

MAMUH

AMEENATOU

LIFE

ROM

JJS

THE SEELAHS

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

Join our WhatsApp group here

AMEENATOU
Mamuhgee

ZafafaBiyar

8


Bayan haihuwar Aleena Omar yasake yiwa mam magana sosai akan musuluntarta Amma Sam mam Baya wani takurawa ko damuwa da maganar sbd ganin yakeyi duk lokacinda taso zata iya musuluntar tinda dai shi yasan yayansa musulmai zasu tashi a hannunsa.

MUHAMMAD HAROON HASSAN SEELAH da MUHAMMAD JAMAAL HUSAIN SEELAH shine sunan da ‘yayan sukaci Wanda daga Aleena har mum dinta Babu Wanda ya musawa sunan kawai dai suna kiransu da Haroon and Jamaal wani lokacin Kuma little seelahs.

Jamaal da Haroon identical twins ne da ko farcensu baka iya banbancewa bare wani abu nasu,
Kamanninsu sunyi mummunan yawan da dole ake banbance musu kalan tufafin sakawansu Dan gane waye Jamaal waye Haroon.
sun taso cikin tsananin kulawa da gata tareda asalin rayuwar da ake kira luxurious life,
Sun taso a cikakkun halfcase Dan kuwa kana kallansu zakasan baturiya da baqar fata ne suka Hadu suka haifesu sedai Allah yayi musu arzikin tserewa dauko gashi irin na mahaifiyarsu hakama hasken Basu wani dauko nata ba na Dad dinsu ne sedai sun fisa haske sosai duk da mam seelah ya Dade da komawa tamkar baturen a harkar rayuwarsa gabaki Daya.

Omar ya dawo Poland inda yake riqe da komai yanxu na nasu dukiyar da kamfanin sbd Dad dinsa ya huta Dan haka yanzu kwata kwata Mr Jaden ya aje aiki sbd manyanci hutawa kawai yakeyi a gida shida mum din Omar ne akan komai Kuma kaman yanda kowa yasani yake Gani Omar Jaden seelah ya wuce ajin su mam ta bangaren ratsawan ilimi da qwarewa a aiki ga class din ma ba Daya ba.

Sun tashi daga inda suke sbd dawowansa kwata kwata da matarsa Dan haka sun koma wani Sabon mansion din daban da suke rayuwa a ciki shida iyayen nasa da matarsa wadda har lokacin Allah Bai Basu haihuwa ba.

Jamaal suna cika 17 years a duniya kakarsu Dake tsananin sonsu fiyeda komai da kowa ta rasu bayan ta musulunta a hannun jamaal wanda shine yafi kusanci da ita sosai fiyeda kowa a gidan nasu Kuma itace tafi ganesu fiyeda kowa a family duk da halayensu sosai suketa banbanta Dana juna tin suna fara tasowa,
Raayoyinsu suna Dan banbanta Amma dai halayensu shine abinda Kai tsaye ya banbance Jamaal daban Haroon daban.

Rasuwar Granny ya Saka Dr Aleena shida damuwa sosai harta koma koyaushe tana gida sbd a bayan Sam batada time na gidanta da ‘yayanta mum dince ke kulawa dasu tana nuna musu kauna kaman ta hadiyesu.

Rasuwarta duk wani hali na mam ya fara fitowa Wanda yafara bawa Dr Aleena mamaki me tsananin gaske Dan kuwa Kai tsaye ya nuna mata Nigeria zasu tattara su koma gabaki dayansu.

Da farko ta dauka ba da gaske yake ba Amma daga baya ya rufe idonsa da Babu Imani ko Daya a ciki ya Bata zabi ko ta bisu ko ya dauke yayansa ya tafi dasu yabarta.

Bata taba Shiga tsoro da tashin hankali ba rayuwarta irin wannan sai a wannan lokacin.

Omar tafara nema ta sanar masa komai yayiwa mam din magana Amma Sam mam Bai yadda ba daga karshe ma rashin fahimtar akansu yaso qarewa Dan haka ya fita a zancen.

Su jamaal Basu San meyake faruwa ba sbd karatu sukeyi sosai basa wani zama gida musamman jamaal da shine yake karatun medicine kaman mum dinsu Haroon ma yaso medicine din Amma Yana Shan wuyar karatu ba kaman Jamaal ba sai mum dinsa ta sakashi karantar law.

Duk yanda Dr Aleena taso riqe yayanta abin gagara Yayi gashi batason tayi kararsa sbd tana tsananin son mijinta Dan haka ta Yanke shawarar binsa Amma ba zaman can dindin ba zata dawo Poland tanayi tana Dan Kai masa ziyara itada yayanta.

Da zasu koma kwata kwata Nigeria din dukiyar su Jamaal ta Dade da shiga hannunsa Dan haka tata dinma da yawanta sun kwashe sun taho da ita kusan 70% sun baro 30% a Poland din.

A Lagos suka Bude sabon Babin rayuwar masu hannu da Mai a makeken mansion gidansa Dake manne Dana lameenu hakama na Omar na manne da nasa Shikuma sbd tin suna can suka Aiko da kudaden da aka zube masu tarin yawa aka Gina musu shi a anguwar security dinta kadai zai baka nutsuwa da Kwanciyar hankalin da duke me kudi yake buqata.

Matar lameenu ta haihu yayanta har so biyu duk mata ta Haifa Fadeela seelah da Aysha seelah.

Daga anguwar har cikin mansion din da suke rayuwa a cikinsa Babu abinda ya banbanta Dana rayuwar luxury da suka baro a Poland Dan haka su Jamaal Basu wani samu damuwa ba hakama mum dinsu ba laifi taji she’s ok sedai hidimominta na can data baro tanajin damuwarsu musamman asibitinta Data karbu tana cikin manyan asibitocin Poland din.

Anan din ma lafiyayyar tsadaddiyar asibiti Alh mam seelah ya budewa Dr Aleena me tsadan gaske aka zuba doctors da kwararrin ma’aikata tafara aiki ahankali ahankali harta fara sabawa tafara sakewa.

Su Jamaal kuwa Basu wani jimaba suka koma Poland makaranta Amma Basu wani jima ba Haroon yafara shiga damuwa da hadda su ciwo sbd baitaba rayuwa Babu iyayensu ba
Kai tsaye Dad dinsu ya dawo dashi Nigeria karatun sbd Daman yafisonsu a kusa dashi.

Jamaal tin farko shine Wanda yafi Jin mahaifiyarsu a ransa fiyeda Dad dinsu sbd tausayin datake basa sosai kan rashin hutun datake samu ga tinda granny dinsu ta rasu mum din ta sake shiga damuwa gashi Dad yakaita Nigeria bataso sbd Bata sababa Dan haka koyaushe mum dinsa itace a gaba cikin ransa kafin dad.

Tinda Haroon ya dawo Nigeria hankalinsa ya kwanta sbd Yana tareda iyayensa,.ita Kuma mum dinsu bataso Hakan ba ko kadan Dan haka ta sake shiga damuwa sosai sosai Dan har gobe batada shiri ko niyar zaman tabbata a Nigeria musamman data fara fahimtar dukiyar Alh Mam din sake babbaka takeyi sosai fiyeda tinani sbd mummunan business din dasuke gudanarwa a bayan fagen business din gasken da akasan sunayi Dan kuwa suna cikin wainda sunansu yafara yaduwa Yana karadewa sbd kudinsu Dake magana.

A nata tsarin data yankewa kanta dukiyar ma bar masa zatayi gaba Daya ta tattara ta komawarta kasarta ta riqe ‘danta Daya tinda shi Haroon sosai yanzu yaketa samun shaquwa da Dad dinsa fiyeda Jamaal Wanda shikuma acan wata irin kauna Mai karfi da shaquwa ce take shiga tsakaninsa da Dad Omar Wanda haryanxu Bai samu haihuwa ba.

***Shekaru sun Dan Kara ja Dan kusan Haroon Dake Nigeria karatunsa yafara Nisa Wanda Dad dinsa ke tsananin alfahari dashi Dan kuwa kusan a matakin dayake Kai yafara sanin huldodin Dad dinsa da Dad lameenu Wanda duk da basa Ashalawa a yanzu Amma suna cikin masu fada a cikinta Dan kuwa Babu huldar da zaa kulla a gama a Ashalawa batareda saninsu ba ko kasonsu,
A matsayi da matakin da suka Kai jini da rayukan da suka kawosu matsayin bazasu kirgu ba Dan haka Allah yake sake musu talalan yanda sukeso suke samu Dan a jere da layin masu kudin gaske idan zaa ambata Seelahs na Daya daga Yan farko farko.

Sunada money and power fiyeda yanda ake zato,
Sunada tarin girma da mutunci a idanuwan mutane sbd suna cikin masu bugun gaba su Bada tallafi da taimako duk lokacinda zaa buqaci Hakan sbd son sake samun matsayi da mutunci a idanuwan mutane talakawa da manyan mutane.

Duk tarin daruruwan arzikin da Allah yayi musu haryanxu Omar ne a gabansu Dan kuwa takowanne bangaren haryanxu shine a gaba kafin su,
Baya Nigeria Amma yanada tarin dukiya da kadarori da suna a Nigeria musamman haryanxu dayake tareda Aron da Ahmed Yan amanar da suka zama tamkar wasu Yan uwansa na jinin musamman Shima nasa dangin suka koma sirkin Muslims da ahlulkitabi Dan zuriar mr Jaden gaba dayansu sun Dade da amsarsa a matsayin nasu kaman yanda Shima Jamaal nasu familyn yake a sirke.

MAMUH

JAMAAL JEEY SEELAH

DEEP

HAROON SEELAH

LOVE

CRAZINESS

ZAFIN KAI

AMEENATOU

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!

AMEENATOU
Mamuhgee

ZafafaBiyar

9


Kwatsam labarin rasuwar Mum din Dad Omar ta riski familyn seelahs Dake Nigeria dole suka tattara suka tafi gaisuwa da Alh Lameenu seelah da matarsa harma da yayansa sai Alh Mam da Dr Aleena wadda batada niyar dawowa matiqar ta tafin.

Haroon seelah Bai samu Daman binsu ba sbd tarin karatun Dake gabansa,
Duk yanda mum dinsu taso ya aje karatun ya bisu su tafi tare ya qarasa acan Sam Bai aminta da Hakan ba Dan a rayuwarsa Babu wanda yakeson burgewa da son sakawa farin ciki irin mahaifinsa hakam shi kansa Dad Yana son dansa ya riqa sosai ya qware a harkar sharia Dan tsayawa ga duk abinda ya shafi ahalinsu.

Dr Aleena tin kafin ta tafi Kai tsaye ta sanar da Mam idan ta tafi bazata dawo ba Kai tsaye Shima ya Bata zabin idan ta tafi zai rabu da ita
Ba musu ta aminta da Hakan tinda tasan ‘danta Daya Yana acan tareda ita Dan haka ta amince a ranar da zasu tafi ya saketa suna Isa can kasar ma suka shigar da divorce dinsu take Akai komai aka gama batareda yayansu sun sani ba hakama Kai tsaye Bata buqaci komai na sakin da ake bayarwa ba a kasarsu ta yafe masa
Dukiyarta datake hannunsa tabar masa akan ya kulawa yayanta sbd bataga alaman zai Bata ba Dan kwata kwata Babu sunanta akan komai na dukiyar duka ya cire ya mallake.

Jamaal ne kadai yasan iyayen nasa sun rabu Haroon Bai saniba Dan haka Jamaal sosai yaji tausayin mahaifiyarsa yaci gaba da Bata kulawa Dan tashiga damuwa sosai batada kowa sai shi din a yanzu sai Omar Daya zama tamkar yayanta.

Har sukai kwanakinsu suka gama suka tafi Dad din Baya wani samun Daman ganin Jamaal sbd Jamaal din dayaji Baya buqatan ganinsa sbd abinda yayiwa mum din,
Shi Dan Kai tsaye ne zai iya Jin tsanar Dad din Dan haka ya zabi nesanta kansa dashi a Dan lokacin kafin ya sauko.

Bayan rasuwar mamma kaman yanda Omar ke Kiran Mrs Jaden sosai yake kulawa da Dad dinsa shida matarsa Nur sbd tsufa da manyanci Daya rufesa sosai,
Ko shekara baa rufaba da rasuwar mamma Dad din Shima ya rasu bayan sun mallakawa Omar komai nasu ya gaji wata irin sabuwar dukiya me yawan gaske shi kadai take hankalinsu mamman yayi mummunan tashi abinda suke jima suna dannewa ya taso Dan haka gaba Daya idanuwansu da zuciyoyinsu suka koma kan OMAR JEEDEN SEELAH Wanda shi a nasa bangaren Akoda yaushe yanzu cikin baqin ciki da kuncin rashin MASOYAnsa na asalin gaske yakeyi kasim seelah da iyayen riqonsa da suka daukesa tamkar Dan cikinsu da suka Haifa.

****Bayan abubuwa sun lafa komai ya zama daidai,kowa ya fuskanci rayuwarsa ciki kuwa harda Dr Aleena wadda hasken idaniyarta,Rabin ranta datake jinsa tsakiyar zuciyarta fiyeda komai da kowa ‘danta JAMAAL MAM SEELAH ya tsaya cak a kan rayuwarta Bai bari damuwa ko wani qunci ya lalata rayuwarta ba Saida ya tabbatarda da koma asalin Dr Aleena seelah dinta ta dawo rayuwarta ta da mace me qwazo da aji da wayewa tareda sanin ya kamata da burgewa harma da kokari akan aikinta ta bangare Daya Kuma ga sauran dukiyarta datake kulawa sosai da ita tana sake fadada business dinta dukiyarta na qaruwa sbd tanada connections da dama sosai.

Jamaal shine karfin gwiwanta Kuma kuzarin datake karfafa kanta tana komawa babbar macen Daya kamata sbd Sam Bai yarda yaga rauni a tareda ita ba,
Dan shi din kwata kwata ba mutum ne Mai yadda Wani ya takaka ba Koda kuwa Yana sama dakai ne Dan Yana girmama sanin darajar Kai fiyeda komai.

Jamaal shine ya Dora mahaifiyarsa a turban hasken musiluncin da mahaifansu ya kasa dorata duk tsawon shekaru zaman auren da sukai har sai da yayanta sukai wayo Jamaal ya musuluntar da ita itada mahaifiyarta da Shikenan mahaifiyarta zata mutu ahlulkitabinta.

Tana son danta Haroon sosai kaman yanda takeson Jamaal Amma matsayin Jamaal daban yake Dana kowa aranta Kuma daga Dad din har Haroon sun San da Hakan sedai Shima Dad din yafi qawa zucin Jamaal sbd tsananin zafin kansa Dan Yana kaunarsa akan Hakan fiyeda komai,
Jamaal dinsa Baya daukan reni ko kadan sabanin Haroon da karatun sheriar da yakeyi duk ya Sanyaya zuciyarsa ya koma Yana kallan komai akan tsari na sharia Dan tsoron aikatawa Dan gudun sabawa sharia.

Duk Dad keson Jamaal kusa dashi Hakan Baya samuwa sedai ya kawo musu ziyara a ya Dan yi watanni ya koma Amma Sam Baya iya rabuwa da mahaifiyarsa Dan itace abinda yafi komai so a duniya fiyeda koma da kowa Dan haka itama mum din Bata fargaban zuwansa Dan tasan zai dawo mata.

**Dad Omar Jaden seelah ya dawo Nigeria da zama a karo na farko tin bayan barinta sedai yazo yayi ziyara yayi Hutu ko wani lalurar ya koma Amma wannan Karan ya dawo ne sbd nacin Yan uwansu su mamma da lameenu Da suka matsu su hade guri Daya da Dan uwansu Rabin jikinsu,

Dawowansa Nigeria ya Sakasu samun wata irin nutsuwa da Kwanciyar hankalin da Basu taba samuba tinda suka rabu dashi se yanzu Daya dawo gasu gashi ahali Daya zuria Daya.

Duniyar duk Wanda yasan seelahs gabaki Daya da iyalinsu Basu taba sanin su ukun ba uwa Daya Uba Daya suke ba sbd tare aka Sansu tare ake jinsu hakama suna Daya da suke amfani dashi hakama dukkaninsu Babu Wanda ya taba fadawa wani ko Yan jarida masu fira dasu abu Daya suke fada musu su din Yan uwane da jini Daya yake yawo a jikinsu.

Kaman mansions dinsu suke a jere haka securities dinsu kusan duk Daya ne Kuma dawowan Alh Omar Jaden seelah ya Saka aka sake samun securities na gidansa daban shi Amma na gidan lameenu da Mam Daya ne.

Tareda Jamaal ya dawo Nigeria Dan haka Jamaal din a gidansa yake zaune tareda shi sbd Mom Nur Bata biyaosa ba tana can itama aikinta datakeyi acan Bata saki ba shi Kuma Bai takurata ba.

Alh Mam ya sake aure tini ya auri matar wani abokin huldansu Daya rasu anan Lagos wadda suke kira da Mum Atee asalin sunanta Atika.

***Tinda Alh Omar ya dawo Nigeria kullum busy yake daga shi har su Ahmed da Aron da yanzu bawai masu aikinsa bane Suma sun zama kaman abokanan aikinsa Dan ya Basu matsayi me kyau Dan haka Sam basa zama sai sunga sun gama daidaita komai nasa anan Nigeria din yafara huldodinsa kaman kowa.

Da farko su Alh Lameenu sun masa tayin su hade dukiyarsu kaman yanda ta Mam da lameenu din take Amma sbd akwai dukiyar dayake son warewa mahaifiyar kasim da haryanxu tana Raye sai yace su datakata tukuna.

Hakan da yayi ba qaramin kular dasu yayi musamman lameenu
Dan haka ko sati biyu baa rufa ba da maganar aka bugawa Alh Omar din waya cewan innar kasimu ta rasu gidanta datake ciki Wanda Omar din ya Gina mata a kauyen na alfarma da Kwanciyar hankali kawai cikin dare akaga ya kama da wuta Dan haka gawarta ma kurmus aka samu.

Ya shiga tashin hankali da mamaki sosai da Jin wannan mummunan labarin sbd baifi sati ba da yayi magana da ita a waya duk da ta tsufa sosai.

A ranar ya shirya suka bi jirgin shi da JAMAAL da Baba Ahmed zuwa gombe.

Sai dare suka Isa
Suna sauka motocin da aka tanada suna jiransa da securities suka kama hanyar kauyen da sai sunyi kusan kwana da wuni Basu Isa ba Dan gaba Daya yayi Nisan da kaman ma baa Nigeria suke ba can asalin asalinsu Wanda ake Kiran kauyen da suna Kartako.

Tafiya sosai sukai tareda jigata Amma dai dole sai je yayi jana’izan inna Dan kuwa itace uwar Data rage masa a duniya Kuma ta tafi tabarsa kaman yanda kasim ya tafi ya barta.

Koda suka Isa Jamaal duk karfin halinda amai ya ringa yi sbd Bai taba wannan wahalan ba duk da ga AC ga komai a mota Amma dai ya gaji matiqar gaske baima taba zuwa irin wainnan gurarenba ko a waya kuwa Bai taba ganinsu ba bare Dan dayasan hakane da Bazai ce zai taho tareda Dad Omar din ba.

Isowarsa ya Saka mutane taruwa anata tururuwar gaidashi kaman zasu masa sujjada sbd girmamawa Dan kaf kauyen Babu Wanda baisan Omar seelah ba,
Seelah Daya kwalli Daya daya rage Mai tinawa da asalinsa tareda taimkawa kowa Dake kauyen,
Shi kadai seelah din Daya rage musu tin daga kan iyayensu har sauran da tini suka mance da kauyen.

A taqaice ma dai shi kadai suka sani a yanzu.

Anyi jana’izan tin kafin isowarsa Dan haka addua kawai akayi ya zauna ya tattauna da manyan kauyen sosai wainda duk suke a bushe kaman Kara,
Kowa ka kalla a kauyen kaman kazo karkarar aljanu haka suke duk sun bushe duk da Yana tallafawa sosai Dan kaman shine yake ciyar da kauyen gabaki Daya.

Inna duka rayuwarta Yaya biyu ta Haifa,
Kasim da indo wadda take aure a kauyen kusa dasu harda ‘yayanta biyu Maza sai kanwar mijinta AMEENAH datake riqo Dan haka ya buqaci ganinsu.

Koda aka aika Kiranta tazo tana ganinsa ta fashe da kuka Dan shine Dan uwanta itama Daya daya rage mata.

MAMUH

JAMAAL JEEY SEELAH

DEEP

HAROON SEELAH

LOVE

CRAZINESS

ZAFIN KAI

AMEENATOU

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

AMEENATOU
Mamuhgee

ZafafaBiyar

10


Zuciyar Omar sosai ta sosu ganin rayuwar da Ayshatu Indo take ciki Dan haka take ya Yanke shawarar mayar dasu cikin gombe sbd rayuwar ‘yayanta ta inganta hakama mijinta Wanda take ya amince Dan Daman Yana fita binni yan kasuwancinsa na siyarda dabbobi.

Lamarin masu abin duniya Babu Bata lokaci a ranar suka juyo suka baro sai washe gari da asuba suka iso gombe.

Lafiyayyar tsadaddiyar hotel din Daya sauka anan aka saukar dasu Ayshatu da yayanta da mijinta Jamaal kuwa acan sama ya sauka dakinsa daban sbd rashin lfy sosai ya rufesa.

Amina ma kanwar mijin Ayshatu sosai take ta amai da zazzabi me karfi Daya Saka dole aka sanar da Omar yasa aka kaisu asibiti take aka Bata gado.

Lamarin kaman wasa saiga Jamaal ya kwanta ciwo Shima Dan haka a ranar yabi jirgi ya shida Aron suka koma Lagos.

Suma su Ayshatu jinya sosai sukai asibiti ta Amina wadda taji jiki sosai sbd Bata taba fitowa binni ba.

Koda aka sallamosu asibiti anriga an samu gidan ansiya lafiyayye daidai su an Saka musu furnitures daidai misalin masu rufin asiri sbd bayason ya sakar musu kudi sosai yanason sufara sanin rayuwar garin idan zasu iya tukuna.

Duk wannan abin da akeyi Jamaal da idonsa baiga mutanen da Dad Omar yaje Gani a kauyen ba bare wainda yazo dasu.

Abinka da mutanen kauye da karamci da son mayarda alkhairi Kai tsaye Babba yayiwa Omar kyautar Kanwarsa dayake so fiyeda komai a duniya wadda yafisonta akan ‘yayansa Daya haifa da cikinsa.

Ita kanta Ayshatu Jin tayi tayi Naam da Hakan Dan haka ta roki Omar akan ya amince.

Shiru yayi tareda kallan budurwar yarinyar da akace an basa din tana zaune a tsakar gidan tana alwala cikin nutsuwa da sanyin jiki.

Fara ce sol kamanta da Yayanta Wanda yake kaman ubanta Dan ya Isa haihuwan nata kaman an tsaga Kara,
Ba qazama bace tanada tsafta sosai shiyasa haskenta yake fresh a Koda yaushe duk da tana kauye kwata kwata Bata aikin wahala sbd idan akwai abinda Babbah ya tsani Gani a rayuwarsa shine ganinta tana wahala shiyasa baiyi wata wata ba yayi kyautarta inda zataje tayi rayuwar Kwanciyar hankali.

Kawu Nuhu Wanda matarsa da yayansa harma da Amina da Yan kauyensu da yawa suke Kiransa Babbah Ya taso a baida kowa a rayuwarsa sai Kanwarsa da mahaifiyarsa ta bar masa bayan ta rasu gurin haihuwarta,
Amina sunan mahaifiyarsu ne data rasu ya mayarwa Kanwar tasa,

Masifaffe ne shi Kuma mafadacin da baida sauki hakama baisan kowa ba sai kansa,
Babu abinda yake girmamawa da ganin mutuncinsu idan ba kudi ba,
Yana girmama kudi,
Yana Basu girmansu,
Yana ganin kimarsu fiyeda kowa Dan kowa zindir yake kallansa idan har baida kudi,
Masu kudi kawai yake saukewa hula ya mutunta,
Duk duniyarsa Amina ce kadai abinda yafi so fiyeda kudi,
Itakadaice abinda take sakasu rissinawa idan ya kafe akan Abu,
Ko Mai garin kauyensu shakkar rashin arzikin babba yakeyi sbd Baya shakkar kowa hakama kauyensu da zagayen ansan Amina ce kadai abinda yake Saka zuciyar babba girgiza Amma ko Barayin dabbobi na shiga gidan kowa a kauyen Amma basa shiga gidan babba Dan Shima kiris ne ya rage masa ya zama Dan ta’addan idan har zaiyi kudin Dan haka Daman dama Kawai yake Jira ta barin kauye sai gata Allah ya kawo.

Kafin Ayshatu yayi aure so biyu suna rabuwa sbd suna kuntatawa Amina sai da ya auri Ayshatu ya Bata matsayi me girma a ransa sbd tsananin son da takewa Amina na tsakani da Allah tin daga zuciyarta Kuma ta riqeta tamkar yarta data Haifa har itama ta haifi nata yayan biyu duka Maza daga Nan haihuwar ta tsaya har suka fara girma.

Duk yanda babba ke tsananin son Amina nata son datake masa yafi Hakan Dan ita sbd shi ta zabi zama kimtsatsiya muka kamilar yarinyar datafi kowa nutsuwa a kauyen tareda mutunci Dan kuwa Bata fita ko kofar gida ko ganinta sai dace ake ganinta Dan kwata kwata Bata fita koyaushe tana cikin gida killace.

Tana tsananin son Dadah da Babba kaman sune suka haifeta Dan haka ko yanzu da suka Bada aurenta ga Wanda Bata taba ganiba bare sani Bata musu ba kaman yanda Shima Omar din kawai ya karbeta bayan ya karanceta cikin qanqanin lokaci.

Bai buqaci komai daga garesu bayan matar kaman yadda suka basa ita Dan haka Kai tsaye ba wani biki ko wata hidima auren kawai aka dauka bayan wata Daya da dawowansu gombe kenan Dan haka Kai tsaye ya tafi da ita Amma Saida babba ya rakota har gidanta yaga duniyar da suke ciki ya koma Yana hawayen rabuwa da Amina.

Ansaka yayan Ayshatu makaranta hakama babba an basa jari kasuwanci yakeyi ba laifi Kuma Yana more rayuwarsa a binni Dan idan ya fara yawo ko gajiya bayayi ita Kuma Ayshatu kasuwancin cikin gida takeyi itama na Yan kulle kulle.

Matar Omar Bata daga hankalinta akan aurensa ba sbd Jin wacece matar daga kauye ta fito,
Hakama su mamman mamakin auren kawai sukayi ta yanda mutum kamarsa da duniya ake respecting da shaawa ace ya auro yar kauye yarinya Kuma,
Shi Alh lameenu hankalinsa tashi yayi da auren sosai Wanda gaba Daya zuciyarsa yaji tana kasa samun nutsuwa ya Kalli Alh mam a lokacinda yake sake Jin damuwar auren yace,

“Mamman me kake Gani zai iya biyo bayan wannan auren na Omar?
Yaushe ne burin shekara da shekaru zai cika?
Wannan burin daf yake da zama tarihi idan har Omar zai fara aure aure.”

Wayar sake hannu Alh mam ya ajiye gefen tsadaddiyar Turkish Royal sofa din Dake palon dasuke Yana dagowa ya Kalli Alh lameenun yace,

“Kana tinanin wannan burin ko shi Omar din zai iya hanasa cika?
Idan ban mallaki dukiyar Omar ba har abada bana kallona Mai arziki Duk kuwa abinda zan Tara din….

Katsesa Alh lameenu yayi da cewa

“Hankalinmu na kwance ne duk shekarun Nan sbd Omar Bai taba samun haihuwa ba,hakama acan Baya mun Jira ne mr and Mrs Jaden su mutu dukiyarsu ta taru ta zama ta Omar din kafin mu dauko mataki
Yanzu dukiyar ta zama tasa Kuma gashi a kusa damu yanda muke so Amma Kuma yanzu yaqara aure
Baka Tinanin zai iya samun haihuwa idan har yaci gaba da auren Nan??

Shiru Alh mam yayi zuciyarta na daukan nauyi ahankali Dan kuwa basajin zasu iya tsayawa jiran Omar samu haihuwa,idan ma ya fara samun haihuwar to idan yayan dari zai Haifa sai sun kawar dasu gefe sbd Babu wani Rai da bazasu iya janyewaba akan buri da kudirinsu dayafi shekara da shekaru tin suna matasansu.

Tinani suka shiga dukansu musamman lameenu da hankalinsa gaba Daya shi ya tashi akan auren shi tin kafin wani abu ya shigo gabansu yaji Yana buqatan a cire matar da Omar din ya auro daga lissafi.

Rayuwar Amina a gidan mijin data kasa sabawa da shi sbd rayuwarsu akwai banbanci tazarar sama da kasa Amma Kuma sbd masu aikin da aka zuba mata da Mai kulawa da ita da koya mata abubuwa da yawa sai tafara Dan sakewa tana koyan abubuwan da dama Wanda Bata dauki lokaci ba mijinta kuwa ya amsheta amatsayin matarsa.

Zamansu Daya ya Saka soyayyarta da tausayinta masu karfi shigar Omar
Ita kuwa Daman tini ta kamu da sonsa kawai tana kama kanta ne sbd ganin kaman yafi karfinta.

Sabuwar rayuwa sosai suka Bude ta sabbin ma’auratan da suke cikin sabuwar soyayyar juna,
Gogewa tafara yi ta zama matar gidan mijinta Dan kuwa sosai take kokarin kulawa da mijinta kaman wadda tayi boko ta waye sosai.

Shi kuwa sanyinta da nutsuwarta tareda tsananin nutsuwan dayake samu da ita ya saka zuciyarsa kamuwa da Sonta fiyeda yanda yayi tinani gashi ita din yarinya ce sosai take narke masa tana sakashi Jin kansa tamkar sabon saurayi duk ta gama kame gangar jiki da zuciyarsa.

Jamaal ma yaji dadin zama da ita sosai fiyeda yanda yayi tinani duk da batajin turanci shikuma ba sosai yakejin hausar ba Baya ma iya doguwar Hausa duk kame Kame ne,

Jamaal ya koma gidan Dad dinsa sedai Bai wani jima ba ya koma sbd hutunta Daya qare na makaranta.

*Kaman yanda ake cewa kaddara ta rigayi fata kwatsam sai ga ciki a jikin Amina Wanda ya girgiza duniyar Alh Omar Jaden seelah,
Ya girgiza sosai sbd Bai taba Saka ran zai haihu din ba,
Yanada ciwo a zuciyarsa na shekaru akan rashin haihuwa Kuma ya Riga ya cirewa haihuwar Rai shiyasa bayyanar cikin ya girgizasa matikar gaske.

Ita kanta Amina Bata Saka ran samun haihuwa ba sbd ta Riga ta yaddarwa kanta zata zauna dashi ahakan ba haihuwa so itama samun cikin ya Sakata mamaki me tsananin gaske da farin cikin gaske duk a lokaci Daya.

Tinda ta samu cikin ya daukesa suka bar kasar kusan watanninsu uku kafin suka dawo lokacin cikin yakai wata shida Babu Wanda yasan dashi bayan shi da ita sai masu aikinta da suka Saba da ita sosai suke mata biyayya.

MAMUH

JAMAAL JEEY SEELAH

DEEP

HAROON SEELAH

LOVE

CRAZINESS

ZAFIN KAI

AMEENATOU

AFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!

AMEENATOU
Mamuhgee

ZafafaBiyar


Ko Nur datake matar Dad Omar din kaman an rufe masa Baki Bai fada mata cikin Amina ba sbd tausayinta Dayaji ya rufesa akan Hakan Dan haka yakejin bayason daga mata hankali ko Sakata damuwa ta hanyar fada mata sai kawai ya share,

Aminansa Yan uwansa su Alh mam na Bai fada musu ba sbd sun Riga sun fara manyanta wane maganar ciki zaije Yana fada musu kawai fatan haihuwan aminan lafiya yakeyi idan Kuma yaga abin zaiyi yawa zai dauketa ne yakaita Poland ta haihu acan sbd bayason ko irinsu bikin sunan Nan yafi son komai nasa quite ba hayaniya hankali kwance yayi naming babynsa batareda wani biki biki sai iya su family da friends kadan suci suci su Sha suyiwa Allah Godia Dan haka yake tsananin kulawa da tattalin aminarsa Dan ta samu babban matsayi a zuciya da rayuwarsa na musamman gashi Kuma zata zama uwar yayansa,macen da zata fara haifar masa jinin kansa.

Su Babbah ma basusan da cikin ba sbd kunya bazata iya barin Amina fadawa dadah tanada ciki ba bare Babba Dan haka tayi shiru batareda ta iya fada din ba har ciki yanata Kara kusantar cike watannin haihuwarsa.

***Mummunan tashin hankalin farko Daya fara ziyartar rayuwar Alh Omar jeden seelah itace wayuwar gari da Akai da mutuwar secretary dinsa Daya kwana Yana aiki a office,

Kisa ce ta tsafta wadda seda Akai aka Gano ba Alh Omar din bane Dan kuwa a office dinsa yake Yana aikin dasuke buqatan miqawa da gaggawa a washe gari.

Da farko baa dauka kisa bace sai da aka bincika abinda ya kashesa aka Gano allura Akai masa wadda ta tsayar da bugun zuciyarsa take tareda tsiyayo jini ta hancinsa da kinnensa Amma sun goge sedai anga sauran jinin.

Duk iya bincike baa iya Gano komai gameda Wanda suka kashesa ba Kuma duk tsananin securities Dake office din suna Nan Amma sun Bada tabbacin Babu wani baqo ko wani Daya shigo a Daren.

Hakanan case din Alh mam seelah ya kashesa tareda sallamar duka securities din ma’aikata ya zuba wasu sabbi sbd bawa Dan uwansu tsaro.

Hankalin Omar Bai tashi ba sbd Bai dauka shi aka kawowa harin ba Amma dai baiji dadiba sosai shiyasa ma ya Saka familyn secretary din nasa cikin wainda nauyinsu yake kansa Dan tallafa musu.

Alh Mam da lameenu ransu yafara tsananta Baci tareda tashi tsaye ga lamarin Dan kuwa basa son wankin hula yakaisu dare har a samu matsala a abinda sukeso Dan haka suka sauya taku tareda Yanke shawarar Kai tsaye gama komai ba Jira.

A hanyar omar jeden ta zuwa airport da daddare zaiyi tafiya suka samu accident na Kai tsaye da yayi sanadin rayuwar drivernsa da raunin Aron sosai shi kansa ya Dan samu rauni kadan Amma dai Allah ya Hana komai samunsa.

Asibiti Akai dasu aka dubasa gawar drivern Kuma aka miqawa Yan uwansa bayan an gama komai hakama Aron an dubasa sosai tareda Omar din suka dawo gida.

Hankalin Omar da Aron da Ahmed tashi yafara yi sbd wannan shine karon farko da suka samu accident a Yan kwanakin ba Wanda Babu ranar da basa duba lafiyar duk motan da Omar zai hau ba.

Basu sake shiga tashin hankali ba Saida aka kawowa motocin Omar din hari ba da Rana tsaka a hanyar zuwa office hadda Harbin da baa samesa ba aka samu Aron a kafada Wanda ya Sakasa zubar da jini sosai take Yan Sanda da jamian tsaro suka kawo daukin gaggawa Wanda duk kariyarda aka bawa Omar Saida aka samu harbinsa a gefen hannunsa Shima.

Attackers din kafin ayi yunkurin kama su Daya daga cikinsu ya harbe sauran Daya bayan Daya Kuma ya gudu baa kamasa ba.

Yan jaridu da media tini suka cika wajen ana daukan rahotanni,
Hakama tini gaba Daya familyn seelahs suka shiga tashin hankali da firgici musamman Alh lameenu da Mam Dan harsun qarasa asibitin da aka nufa da Omar din.

Amina ba qaramin tashi hankalinta yayi ba Dan haka tini tafara kuka ta kira Babba ta sanar musu,
Su kansu babban hankalinsu tini yayi mummunan tashi dajin kukan Amina Dan haka ya ringa rarrashinta da Bata tabbacin suna Nan tafe Inshallah.

Washe gari asubar fari babba ya kamo hanyar Lagos a babbar motar Lagos Yana fatan Allah ya tsare Omar ya basa kariya sbd rayuwar Aminarsa taci gaba da zama cikin Jin dadi da gata da Kwanciyar hankali.

Saida ya kwana ya wuni a hanya kafin suka iso Kuma Yana isowa Kai tsaye asibiti yafara Isa daqyar aka barsa ya shiga da taimakon Ahmed ya dubo Omar din Wanda ake kokarin dawowa dashi gida.

Alh Mam seelah da Alh Lameenu seelah duk suna tareda Omar din a lokacinda ya shigo dubasa sedai kallo Daya dukkaninsu sukai masa suka dauke Kai Dan Babu Wanda yasan waye she bare inda ya fito hakama Shima Omar din Bai sanar dasu waye babba din ba.

Gida suka dungumo suka dawo harda babban Wanda Yana saukar da idanuwansa kan cikin dayake gaban Amina Jin yayi idanuwansa suna cikowa da hawayen farin cikin dabaisan zai taba ji ba idan yaga zuriari Aminarsa,
Yau Aminarsa ce daukeda juna biyu zata haifar masa wasu yayan bayan nasa.

Ita kanta Aminar ganinsa ya Saka Hawaye cikowa daga idanuwanta suna gangarowa masu dumi hakanan taji jikinta yayi sanyi da tsananin farin ciki da kewan Dan uwanta Kuma ubanta,
Inama zai zauna da ita harta haihu Kokuma a mayarda ita gida ta haihu a gaban dadanta da Babba Dan tasan Suma zasu so Hakan.

Farin cikinsa karuwa yayi ya qaraso lafiyayyar palon baqin da akai masa iso sanyin ac da qamshin arziki Tako ina Yana tashi ga wani sanyi da laushin carpet din tsakiyar palon dayake takawa suna ratsa jikinsa suna rage masa gajiya.

Qarasawa tayi itama ta zauna gefensa tana masa sannu da zuwa tareda tambayar meyasa Bai fada mata ya taso ba bare isowarsa ba.

Murmushin Jin dadi kawai ya sake Yana Jin kaman ta haihu kafin ya koma yayiwa abinda zata Haifa huduba da kansa kafin ubansa ya masa Dan ganin yakeyi ko uban cikin bazai Kaisa son abinda zaa Haifa din ba tinda ‘ya ko ‘dan Aminatunsa ne dole suga soyayya da gata uwa Uba idan yayi kudi karbe abinda zaa Haifa zaiyi inshallah.

Abinci aka kawo masa kala kala da abin Sha duk da Yana Jin gajiya Saida yaci ya koshi kafin aka Kaisa har boys quarter yayi wanka yayi sallah ya kishingida dan hutawa da rage gajiya.

Washe gari ma ya samu lokacin Omar sosai sun zanta hakama Amina da daddare kusan raba Daren sukai suna magana tinda asuba ya juya ya koma sbd ya matsu yaje yafara shirin haihuwar aminan yakuma fadawa Dadah Dan ya kasa fada mata a waya.

***Abubuwa sunyita faruwa Daya bayan Daya na son daukan ran Omar Amma Allah na basa kariya sedai abubuwan sun fara tsananin gaske Dan kuwa ayanzu duk makusancin Omar yasan rayuwar Omar din na cikin hadarin da baa San daga Ina ne masifar ke fitowa ba hakama baa San su waye masu Neman rayuwar tasa ba a HANYOYI mafi Muni Dan aduk lokacinda Akai niyar illatasa sai anyi sanadin rayuwar wani har abin yakai yafara girgiza nutsuwa da rayuwar Omar.

Suk kansa su Alh Lameenu hankalinsu ma qaramin bayyanarda tashinsa sukayi ba shiyasa suka dauki mataki sosai aka sallami kaf securities na gidajensu da gurin ayyukansu suka zuba sababbi harma da jamian tsaro.

Wannan ne ya Dan kwantar da hankalinsu Ahmed da Omar din Amma kwata kwata nutsuwar Omar da tinaninsu sun shiga wani yanayin daban na tinanin dole akwai mummunan al’amarin Dake bibiyar rayuwarsa ba tin yanzu ba Dan kuwa mace macen da akeyi a rayuwarsa ya fara yawa daga wannan ya mutu sai wannan Dan haka yaji hankalinsa ya fita kwata kwata daga zaman Nigeria Kodan bawa iyalinsa kariya musamman Amina da abinda yake cikinta,
Ya tabbatarda duk me son rayuwarsa sbd dukiya ne to Dan haka bazaa taba son ya samu magajin dukiyarba idan har ita akeso.

To tin farko ma wayene me son dukiyar tasa?
Bayada abokan gaba,hakama shi mutum ne Mai Sirri da son rayuwar kaffa kaffa Bai bayyanarwa da duniya irin Fadi da yawan dukiyarsa ba Dan a idon duniya anfi sanin dukiyar su mam akan tasa Dan shi kusan duk Rabin dukiyar na Poland,bayan Yan uwansa Babu Wanda yasan adadin dukiyar da yake da ita.

To meyake faruwa a rayuwarsa ne?
Da gaske Ahmed yake na kusa dashi ne masu Neman rayuwarsa kokuwa dai bashi Omar jeden din ake Neman rayuwarsa ba?.

MAMUH

JAMAAL JEEY SEELAH

DEEP

HAROON SEELAH

LOVE

CRAZINESS

ZAFIN KAI

AMEENATOU

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!

AMEENATOU
Mamuhgee

ZafafaBiyar

12
A bangaren su Alh Lameenu abubuwan sun jagule musu gabaki Daya sbd wankin hula na Neman kaisu dare,Daren ma mara kyau sbd rayuwar Omar jeden Daya rak tana Neman gagararsu dauka bayan tsare tsaren da suka ringa yi ana kaiwa rayuwar hari,

Kan Mam ya dauki zafi matiqar gaske Dan gaba Daya kaman anyi masa asiri Jin yakeyi idan ba cike burinsu sukai ba kwata kwata bazasu taba samun Kwanciyar hankali da nutsuwa ba musamman yanzu da kullum Omar seelah ne yanzu a jaridu da labarai,

Shi Lameenu matar Omar ce ta tsaya masa a Rai da maqoshi Dan kuwa jikinsa na Basu zata iya Bata musu aiki kwata kwata daga ranar data samu ciki ko makamancin Hakan Dan haka shi idanuwansa akanta suke tafara barin duniyar gaba Daya yakeso kafin su sake dawowa kan Omar din Dan haka Kai tsaye ya Yanke shawarar ayi me yiyuwa a huta kafin su zauce akan dukiyar da bata shigo hannunsu ba har yanzu kaman abin Baki sai wahala sukeyi shekaru da ciwon Rai da baqin cikin da kullum zuciyoyinsu ba lafiya.

Shi Mam ba iya matar Omar yakeson a gama Dan matsalarta yanzu ba harta Omar din Dan ya gaji da ganinsa a gabansa Kuma samansu,
Ya gaji da Jin sunan Omar jeden na shiga kunnuwansa,
Ya gaji da Jin sunan Omar jeden a kafofin yada labarai,
Shi kansa Omar jeden seelah din ya gaji da ganinsa Yana yawo Yana numfashi Yana samun mutuntawa da respect da cika idanuwan mutane,
Ya gaji da duk wani abu Daya shafi Omar ga uwa Uba ‘dansa dayake tsananin son ya kasance a karkashinsa Yana tareda Omar din Yana sonsa kusan fiyeda yanda yake sonsa shida yake ubansa Daya haifesa Dan haka ya gaji a rufe chapter din Omar din kawai a huta.

Wani numfashin Jin nauyin zuciyarsa na rayuwa Lameenu ya sake Jin abubuwan da Mam din ya fada Dan Shima Kam yakai maqura,
Wani mugun nauyi ne danne da zuciyarsu duk tsawon shekarun Nan tin daga ranar da arzikinsu kasim ya bayyana a ashalawa.


Koda cikin Amina ya shiga wata Tara ya Isa haihuwa har lokacin Babu Wanda yasan dashi bayan uban cikin da Aminansa Ahmed da Aron sai su Babbah,
Duk huldarta da muamalarta dasu mum Atey Basu taba lura da ciki a jikinta ba sbd boyewa takeyi cikin hijab hakama ko gidan lameenu Basu San da cikinba sbd Aminar nada zurfin ciki sosai hakama faruwar tashi tashen hankalin Daya ringa samun mijinta ya sanar da ita kada kowa yasan da cikin shiyasa ta sake Adana kanta ma da cikin ya tsufa kwata kwata ta Dena fita koina ko gurin mum Atey din ta Dena zuwa kwata kwata sedai Haroon ne ke shigowa sosai Kuma Shima Bata taba barin yaga cikin ba.

Shirye shiryen fita da ita ta haihu a Poland Omar keyi hakama su Babbah sunacan sunata zumudi da Shirin haihuwarta Dan sunso abarta ta dawo haihuwa Amma Sam Omar yaqi yarda da Hakan dole suka hakura suka bar zancen Amma dai zasu taho idan ta haihu.

Dayake tamkar yar cikinta dadah Kejin Amina tini ta hada mata kayan fitar zaqin haihuwa da wasu maganin gargajiyar da zai Sakata samun saukin nakuda babba zai kawo mata ya dawo kafin ta haihu su taho tare.

Shi kansa babban cikin zumudin zuwan yake Dan duk yaga Omar wata sabuwar jakar arziki yake samu daga garesa Dan haka Baya ganin wahalar Nisan tafiyar kudin yake kalla da Kuma Amina dazai Gano.

Ranar asabar da asuba Babba yabar gombe yahau motar Lagos zuciyarsa cikesa zumudin haduwa da ‘yar uwarsa wadda hakanan yake Jin sabuwar soyayyarsu ta jini tana qaruwa a ransa har kirjinsa na nauyi
fatansa dai ya Isa lafiya.

Acan Lagos kuwa tin safe da Amina ta tashi takejin yanayinta Babu dadi kwata kwata,ciwon mara da nauyin marar takeji sosai gashi Omar Yana gida kwata kwata ya Dena fita a kwanakin sbd hatsarin da rayuwarsa take ciki yayi yawa Dan haka aka dakatar dashi daga fita sai an gama bincike.

Rashin fitarsa ya Saka masu jiran fitowan tasa basuda zabin Daya wuce kawo aikinsu har cikin gidansa sbd tarkonda aka hada masa a waje Yana jiransa bazai taba tsallakesaba Daya fita da tabbas sai yabar duniya a ranar Daya fitan shiyasa ma daga Aron har Ahmed sun Kai matiqar wuyan lameenu da mam sbd sun zama kamar wasu makaman kariya ga Omar din.

Batareda ta nuna halinda take ciki ba sbd kada ta damar da Omar din Amina ta ringa kulawa dashi sbd Shima Yana fama da ciwon Kai gashi masu debe masa kewa da firarrakinsu idan har suna gida to suna babban garden na Bayan gidajensu dashine ya hade gidajen nasu uku ta kofofin Baya acan suke zama suna hutawa tareda wayoyinsu hatta abincin Daren yawanci acan sukeci tare wani lokacin gaba dayansu harda iyalinsu tare suke ci cikin kulawa da shakuwa.

Mam Baya kasar Yana Poland yaje dubo Jamaal haka kawai,
Lameenu ma a ranar yayi tafiya da safe zuwa Abuja wani meeting.

A jikin mijinta ta kwanta bayan dataji karfin jikinta duk Yana Neman karewa Amma har lokacin Bata nuna masa abinda yake damunta ba.

Kwanciyarta a jikinsa ya sakashi Jin wani irin sanyi da kaunarta data cikin dayake jikinta na sake dabaibayesa musamman yanzu da kowanne lokaci zata iya haihuwa shiyasa ma ya matsu suyi tafiyar.

Qamshin jikinsa ta shaqa ahankali tana Dan rufe idanuwanta suka Danyi laushi sbd rashin kuzari.

Shi kuwa yanda take sauke numfashi ahankali cikin jikinsa tana sake narkewa ya sakashi Jin Sonta na hanasa riqe kansa Dan haka ahankali ya fara shinshinarta Yana shaqar nata qamshin Yana Jin dadin dumin jikinta a fatarsa.

Tanajin Hakan ta lumshe idanuwanta ahankali tana lafewa Dan tasan me Hakan zai haifar.
Rungumeta yayi dakyau Yana hade fuskansu guri Daya yayi kissing hancinta ahankali kafin ya hade bakinsu Yana lumshe nasa fararen idanuwan masu kyau Yana zare doguwar rigar Dake jikinta a natse.

Cikin sanyi da nutsuwa ya tafiyar da ita har sukai wata nutsatsiyar making love daga Nan bacci ya daukesa me nauyin gaske bayan yayi wanka.

Itama lallabawa tayi mararta na sake kullewa taje bedroom dinta tayi wankan tsarki ta sake wani wankan ta fito tayi sallan laasar itama ta shige daki tanason Jin ko zata iya baccin Amma Sam baccin yaqi zuwa.

Safiyya ta kira Mai aikinta datake kulawa da kusan komai na gidan tace ta kawo mata ruwan Tasha Amma Mai zafi bamai sanyi ba.

Koda Fatima ta kawo mata ruwan Taga yanayinta cikin kulawa ta tambayeta ko a kira doctor ko Akira mum Atey.

Girgiza mata Kai tayi tana sake danne abinda takeji Amma Sam Baya dannuwa Amma dai duk da haka Bude Baki tayi cikin sanyi tace

“Karki sanar da kowa zuwa anjima idan jikin baiyi sauki ba zan sanar da Daddy”

Numfashi Mai sanyi safiyya ta sauke ahankali cikin tausayin Aminar idan nakuda ce tace

“Toh shikenan Allah ya Baki lafiya yakuma saukar Dake lafiya”

“Amin” Aminar ta amsa daqyar tana Dan daurewa bayan ta amsa ruwan a dogon glass cup Tasha kadan ta ajiye.

Bayan fitar safiyya sosai tafara Jin yanayin na karuwa har Akai magrib ta tashi daga Palo Takoma bedroom tayi alwala tayi sallah,
Tana idarwa ta fito taje bedroom din Omar bayanan ya fita sallah.

Koda ya dawo a tare suka zauna palonsa sukaci abinci Wanda kadan ya Bata a baki tace ta koshi ta tattara kayan da kanta ta fita dasu.

Daga can Bata dawowa dakinta a ta shige tayi sallar ishai tayi Shirin bacci ta kwanta a dakinta sbd batason zuwa dakinsa ya gane halinda take ciki.

Yana masallaci sallan ishai Babba ya iso ba qaramin mamakin ganinsa yayi ba sbd Babu Wanda yasan yana tafe har aminan Bata saniba.

Cikin kulawa da farin ciki sosai ya tarbesa suka shigo Kai tsaye masaukinsa suka nufa sbd Amina tariga tayi bacci dukansu sun sani Dan haka babban yace abari da safe kawai tagansa har murna saitafi ma.

Ba musu Omar yayi Naam Dan Hakan Dan haka take aka kawo masa abinci kala kala aka sake gyare masa boys quarter din aka kawo cartons na ruwa da drinks aka Saka a fridge sukai Saida safe ya fice yabarsa akan Saida safen.

Har bedroom dinta yace yaga bacci ya dauketa me sanyi da nutsuwa Dan haka Bai tayarda ita ba ya kyaleta ya wuce bedroom dinsa kawai sbd yasan tana buqatan hutawa sosai Akai Akai sbd cikin jikinta.

MAMUH

MAM#LAM#OMAR#SEELAHS

JAMAAL JEEY SEELAH

DEEP

HAROON SEELAH

LOVE

CRAZINESS

ZAFIN KAI

AMEENATOU SEELAH

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!

AMEENATOU
Mamuhgee

ZafafaBiyar


Kwantawa yayi Yana waya da Nur wadda ke sanar dashi zuwan Mam ayau din gidanta ya kawo mata ziyara tareda Jamaal harma ya Bata kyautan 5000 dollar.

Numfashi ya Dan sauke ahankali Yana Jin dadin kulawansu ga Iyalin juna shiyasa ma yake Jin damuwar tinanin Dake shigarsa na son tattarawa ya koma inda ya fito sbd tsaron lafiyarsa data iyalinsa da ‘yayan da zaa fara Tara masa amma Kuma Yana cikin damuwa da baqin cikin rabuwa da ‘yan uwansa da sukai alkawarin rayuwa tare su mutu tare.

Bayan gama wayarta guraren 1 na dare ya tashi yayo alwala kaman yanda ya Saba yazo ya tayarda sallah.

Ya Dade a farke Yana adduoinsa da Babu Daren da bayayinsu tinda ya samu kansa a rayuwar Kwanciyar hankali da nutsuwa Bai taba tsallake Daren da Baya sallolin dare da adduoi ga iyayensa na asali da suka haifesa Dasu kasim ba da iyayensa na riqo harma da ‘yayan da baisan zai haifa ba Yana musu adduar zuwa duniya lafiya suyi rayuwarta lafiya Kuma su komawa ubangijinsu lafiya.

Karfe uku na dare ya miqe daga lafiyayyar gadonsa bayan ya kwanta sbd dubo Amina Dan Basu taba kwana na tareda ba idan har Yana gari sai yau din,
Kuma motsi yaji kaman harma da magana Dan haka fito Yana sake kallan agogo Kai tsaye ya nufi hanyar bedroom dinta.

Koda ya tura kofar bedroom din tana zaune tsakiyar gadonta ta hada zufa sosai idanuwanta sunyi jajir tana cikin azaba Mai tsananin gaske.

Cikin sauri ya qaraso gurinta Yana ambatar sunanta cikin kulawa Mai tsananin gaske da tashin hankali.

Hawa gadon yayi Yana kama hannunta datake qanqame gado dashi,
Cikin tausayinta me tsananin gaske yace

“Labor ne?,tin yaushe kika fara ciwon?
Meyasa Baki sanar saniba?

Saukowa yayi gadon ya koma bedroom dinsa ya dauko wayarsa yafara Neman wayar Ahmed yanason sanar dashi suna buqatan zuwa asibitin a tsakiyar dare Kokuma kawo likita gida Amina zata haihu.

Kasa samun wayar Ahmed din yayi yakoma Kiran ta Aron shikuma tashi Bai dauka ba.

Saukowa yayi kasa ya nufi bangaren masu aiki da kansa yayi knocking ya kirawo safiyya ta fito sbd tafara manyanta dole tasan kan haihuwa kafin ya samu Ahmed.

Komawa yayi dakinsa Yana ci gaba da Kiran wayar Ahmed Baya samu Dan haka ya yanke shawarar fitowa da kansa yaja mota yakaita asibiti sedai fitowarsa harabar gidan yafara cin karo da abinda ya girgizasa.

Jini yagani a gurare daban daban a harabar gidan Wanda yake fresh da alama yanzu yanzu jinin ya zuba duk inda ya fito.

Tashi hankalinsa yayi take ya juya da sauri zai koma cikin gidan sedai ko taku Daya beyiba wutar gidan ta dauke gaba Daya abinda Bai taba faruwa dasuba a rayuwar gidan Dan haka gabansa yayi mummunan faruwa da wani irin mugun sauri ya nufi ciki Yana jefa kafafunsu cikin duhu wayarsa tini ya saketa ya dawo ga matarsa.

Acan cikin gida kuwa tini nakuda ta tasowa Amina gadan gadan a yanda take safiyya ma Bata tinanin zaa iya daukanta zuwa asibiti Dan komai yazo gab.

Babbah da Shima haka kawai ya kasa bacci duk tsananin gajiyar Daya debo Yana Jin motsi ya leqo idanuwansa suka sauka akan Omar Daya fito harabar gidan seikuma gashi an dauke wuta.

Harya koma ya kwanta saikuma ya Tina da akwai me ciki a gidan kodai nakuda ta tasowa Amina ne?

Tashi tayi batareda tinanin komaiba ya fito daidai ganin wulgawar mutane kusa Guda biyar zuwa cikin gidan ta kofar Baya take gabansa ya Fadi Dan yasan dai gidan baa dauke wuta hakama su waye suka shiga gidan.

Shima duhun ya ciyo yayo cikin gidan Kai tsaye kofar da mutanen suna shiga Shima ita ya shiga Dan Baya tsoron barayi Sam tinda Shima ya samu damar satar zeyi idan bazaa kamasa ba.

Shigowar babbah ta kofar Baya da shigowar Omar ta kofar gaba duk basuyi nasarar rigan mutanen Isa ga dakin Amina ba inda take kwance cikin tsananin azaba.

Da kawu da Omar tare suka Isa kofar Hawa sama sedai an datseta taqi buduwa.

Da sauri Omar ya Kalli kofar Yana jijjigawa jikinsa da zuciyarsa na daukan wani irin rawa da mugun tsoro.

Kawu da baigama fahimtar komaiba cikin rawar murya yace naga shigowar mutane na biyo duk yanda Akai Barayi sun shigo gidan…..

Katsesa Omar yayi cikin wata irin rawar murya da tashin hankali da cewa

“Amina na nakuda su kadai ne aciki,
Ba Barayi bane,Amina na cikin hadarin gaske….

Kasa qarasawa yayi sbd mummunan rawar da jikinsa keyi zuciyarsa kaman zata fito sbd tashin hankali.

Waje ya koma da sauri Baya ganin gabansa Dan lalubo wayarsa,

Babbah kuwa Jin wannan mummunan tashin hankalin zancen kofar ya ringa duka Yana ambatar sunan Amina Amma kofar kaman Bango ko motsi Batayi sbd tsadanta da yanayin ginin.

Rawa jikinsa ya dauka tareda shiga tashin hankalin da Bai taba tinanin ya shigaba a rayuwarsa.

Acan waje kuwa securities Omar ke kwalawa kira Yana karade harabar gidan kaman mahaukaci Yana ihun Kiran sunan securities Yana sake Saka Kiransu Ahmed Wanda a lokacin Kiran ya shiga take suka nufo gidan cikin gaggawa da tashin hankali
Securities din gidan kuwa tsit Babu ko motsinsu bare alaman akwaisu ga wani irin duhu Dan Babu haske kona farin wata.

Amina Dake cikin wani mummunan hali Bude kofar dakin da Akai aka shigo ya Sanya safiyya juyowa da hasken fitilar wayar aminah din tana haske kofar Dan daukan Omar ne sedai mutanen data Gani ya Sanya wayar hannunta subucewa tana kallansu zuciyarta na daukan rawa da duka.

Amina kuwa ko dagowa Bata iya yiba saima sake rintse idanuwanta datayi sbd azaba sedai kafin ta Bude idanuwan daga rintsewan datai kakkaifan makami ya ratsa gefen kirjinta ya shige.

Budewa idanuwanta sukayi ahankali cikin wani sanyin azabar Daya danne na azaban nakudar datake ciki sedai kafin ta karasa budewa ya zare ya sake kutsa mata wuqar a gefen cikinta jininta ya feso masa har a fuskarsa dake rufe da black abu.

Yana Ciro wuqar daga cikinta wuyan safiyya data mutu a tsaye kawai ya soka ya zare suka juya da sauri suka fice sedai suna Bude kofar babba Dake Bakin Kofar cikin mummunan zaucewan tashin hankali sukaiwa mummunan dukan Daya zube a gurin sedai sbd karfin hali da tsananin son ganin Amina Bai sumeba duk da hancinsa Daya bare da jini take rarrafawa yayi Yana hayewa saman su Kuma tini suka fice suna ficewa Omar na dawowa sedai yaga ficewansu da gudu yabi bayansu a zauce Yana Jin tamkar ya rasa hankalinsa da tashin hankalin da batai Bata Saka masa Rana ba.

Ahmed da Aron sun Riga jamian tsaro isowa Dan haka Babu wata wtaa suka fado gidan.

A daidai kofar Baya suna kokarin ficewa Omar ya riqe Wanda yake Baya a cikinsu sedai ga mamakinsa kamshin Daya shiga hancinsa duk da Baya hayyacinsa ya girgizasa sedai kafin yayi nasarar ganin idanuwansa dasuke kadai ne a bayyane Lameenu ya daga wuqar hannunsa ya daga setin zuciyar Omar zai daba masa Aron yayi saurin janye Omar din da mugun sauri sedai cikin tsautsayi wuqar ta sauka tsakiyar wuyansa ta Baya take jininsa ya feso fuskar Omar gaba Daya ya rufeta.

Wani irin dakatawa zuciyar Omar tayi da bugawa Yana qamar da idanuwansa akan bayan Wanda yayi kusan Yana guduwa batareda iya ko motsa idanuwansa ba Dan kuwa shock ne asalin shock ya kashesa gaba Daya ga Aron a jikinsa ya sake gaba Daya.

Ahmed da hasken wutar gidan da aka kashe yake ya kunna Koda yazo mummunan ganin dayayi ya sakashi sakin mummunan ihu yana qarasawa da gudun gaske ya dauke Aron daga jikin Omar dayayi mutuwar zaune.

Mutuwar su kasim ce tafara dawo masa daki daki da yanda ta kasance,
Shin me idanuwansa suka ganar masa kaman lameenu,
Me yake faruwa ne da rayuwarsu?
Me shedan yake nuna masa?
Meyasa lokacinda su kasim suka rasu su lameenu Basu tayasu fada da wainda suka kawo musu hari ba sai daga baya,
Da gaske bacci sukeyi Koda ake fadan?
Wane bacci ne zaisa ayi kisa gabanka kace bakaji ba??
Innalillahi wainna ilaihirrajiun
Innalillahi wainna ilaihirrajiun.

Fita hayyacinsa yayi take yana Neman samun bugawar zuciya Ahmed ya daukesa da saurin gaske yayi ciki dashi cikin tashin hankali Yana tsinewa jamian tsaron Daya kira da Basu isoba har lokacin.

MAMUH

MAM#LAM#OMAR#SEELAHS

JAMAAL JEEY SEELAH

DEEP

HAROON SEELAH

LOVE

CRAZINESS

ZAFIN KAI

AMEENATOU SEELAH

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!

AMEENATOU
Mamuhgee

ZafafaBiyar

14


Acan Babbah Koda yakai kansa dakin Amina daqyar Yana ganin mummunan abinda ya faru a dakin ya ke jiki yayi ya Fadi Dan Jan jiki ya Isa gareta Babu abinda Baya rawa a jikinsa ya kamota gaba Daya Yana girgiza mata Kai cikin mummunan tashin hankalin da kuka me tsananin gaske kaman yaro Yana girgiza mata Kai Yana hanata magana sedai itama bazata iya maganar ba wani irin yunkurin gaske takeyi me karfi tanason haihuwa kota halin Yaya shikuwa kukansa karuwa yakeyi sbd duk yunqurinta jini ne ke zuba kaman famfo daga inda aka soketa da wuqa Hakan Kuma nuni ne da bazata Kai labari ba.

Kuka babba keyi sosai Yana rufe raunikan nata da duk rigar jikinsa Daya cire Yana ambatar sunanta da cewa

“Aminatou karki tafi ki barni Dan Allah,
Ameenatou ki bari ni na tafi na barki Dan Allah karki sake yunqurawa Ameenatou kece abinda kadai nake da ita Ina kalla inajin farin ciki Dan Allah Ameenatou karki sake yunqurawa”

Omar ne da Ahmed suka shigo hankali tashe.

Ahmed na ganin haka yaje da gudu yazo da dayar me aikin wadda itama ta taba aure da haihuwa har biyu
Tana zuwa abinda ta gani ya Sakata rikicewa gaba Daya sedai kafin ma tayi kokarin taimkawa Amina din tini Aminar tayi wani irin yunkuri me karfin gaske saigashi ta haife cikin dayake jikinta ko numfashin yunqurin Bata sauke ba ranta ya fita.

Tsabar tashin hankali da firgicin da Maryama ta shiga da madubun da safiyya ta fada ya fashe na dakin ta Yanke cibiyar ta dauko babyn ta fito kawo Dake tsananin kukan tashin hankali Yana ganin haka yasan Amina ta tafi tabarsa.

Kafin su karbi yar Dake hannun Maryama wuta kawai sukaga ta kama gidan.

Daga babbah har Omar akan gawar Amina suka tsaya cikin tsananin kukan tashin hankali mara misali sbd har gwara Omar yataba sheda mutuwar Yan uwansa ta kisar gilla Amma babba Bai taba Ganin wannan mummunan masifar da balain ba ganin idonsa na kisar gilla ta danyar jini.

Wuta ce kawai take sake balbale gidan Wanda ya Saka Ahmed fara janyosu daga gawar Dan ficewa daga gidan Amma Sam sun fita hayyacinsa kamanma sun zauce.

****Wutar gobarar da baasan ta Ina ita Kuma ta faro bace ta rufe gidan gaba daya hakama duk kofofin fita an rufesu.

Sosai wuyar tafara ci a cikin gidan gashi duk hanyar fita Ahmed ya nema Babu dole Omar ya dawo hayyacinsa ya karbi yarsa yanajin tsananin baqin kasacewar ranar haihuwarta ranar mutuwarta data iyayenta.

Rungumeta yayi tareda kallan babbah da gaba Daya Baya hayyacinsa ya miqa masa ita.

Babbah na karban babyn Jin yayi bazai iya barin ya rasa yar aminatounsa ba Dan haka cikin wutar ya kusa ya fice ta glass din window da duk ta yanke bayansa muguwar yanka ma kuwa.

Inda kawu ya fice tanan Maryama ta fito a nakashe itama duk yanka har a fuska.

Duk yanda Omar yaso fiddo gawar Amina Hakan Bata samuba sbd tsananin da wutar tayi Ahmed janyesa yayi ya fito dashi ta dole.

Yana ihun Kiran Aminansa Amma ba yanda suka iya.

Tsananin wutar ya Saka Jamaa tashi da fitowa sai alokacin jamian tsaron suka iso hakama fire service sun iso sedai kwata kwata baa samu damar Ciro gawar Amina da Aron ba da safiyya harma da securities dinsa da baa ganiba ana kyautata zaton Suma gawarsu na ciki Tinda Suma ana zargin Barayin hardasu suka kashe.

Fadar Mummunan tashin hankalin da jamaar Dake anguwar suka shiga a cikin Daren bame yiyuwa bane,
Hakama Omar tini ya Yanke jiki ya Fadi Akai asibiti dashi tareda masu basa kariya sosai.

Babba Dan Maryama Babu Wanda yagansu suna fitowa suka silale Dan tseratar da rayuwarsu musamman Maryama data haukace gaba Daya ta fice hayyacinta Dan Bata taba Ganin jini kaman yau din ba da gawa harta mutane biyu.

Duk inda babba ya Saka kafa ya dauke anan take Saka tata Dan ta Ganowa rayuwarta tsira idan ta bisa kafin safe.

Shi kuwa babba gabaki Daya ya fita hayyacinsa Babu abinda yakeji yake Gani bayan Kai kansa gida da abinda Amina ta Haifa wadda haryanxu Bai tsaya ya duba me ta Haifa din ba hakama baisan sanin a raye baby take ko mace.

Tafiya sukayi sosai a cikin duhu harsuka fice daga anguwar gaba Daya batareda angansu ba daga Nan suka samu inda suka shige suka boye.

Sai lokacin ya dago babyn daga dunqular da yayi mata yana Jin motsawarta Dan tinda tayi kukan bayan haihuwarta Bata sake kuka ba tayi shiru.

Suna cikin wani mugun tsohon shagon Akai asuba aka fito.
Ana fitowa sallah suka samu abin Hawa tin akwai duhu suka nufi Tasha.

Suna Isa toilet din tashar shine yabarwa Maryama yar yashiga bayan gidan cikin tashar ya wanke jikinsa tas hadda kayansa dasuke kaca kaca da jini ya wanke ya fito kaman zai qame sbd sanyi Amma haka ya bawa kayan mintina suka Dan sha iska ya mayar jikinsa yake ya karbi babyn itama take ta wanke nata jikin ta dawo suka fara rarraba idon yanda zasuyi.

Koda gari yayi haske sosai tini labarin gaborar gidan Alh Omar jeden tafara Dan yawo sedai baa fidda maganar kisan da akaiwa matarsa da Amintaccensa Daya Aron ba sosai.

Kawu da kansa ya ari waya a tashar ya kira numbern Dadah ya aika Hafiz shagon POS da kudi masu yawa aka Aiko masa a acct din me POS Daya samu Nan Tasha.

Har kudinsa harna Maryama ya biya suka kamo hanyar gombe da jaririyar yarinyarda Allah ya taimakesu batai musu kuka ba hakama ruwan Roba kadai suketa Bata tana jikin Maryama sbd kaucewa zargi har suka kwana suka wuni a hanya suka iso.

Suna sauka Mai tsaye gida suka nufa.

Kallo Daya dadah tayi musu hankalinta yayi mummunan tashi sbd ganinsu da jinjira.

Da farko babba kasa magana yayi sbd zuciyarsa datai wani irin bushewa da nauyin gaske hakama Bai fita daga shock ba har lokacin Amma ya hakanan ya Bude Baki daqyar ya hada kalaman cewa ‘yar Amina ce ta shiryata tukuna sbd tin daga Lagos har gombe zindir babyn take dunqule a zanin gadon dakin mahaifiyarta.

Rawa jikin dadah ya dauka kanta Yana Neman juyawa ta Bude Baki zatai magana Maryama ta fashe Da wani irin kuka mai karfin gaske tana kasa magana itama sbd sai alokacin ta samu kukan yazo mata.

Ita kanta Dadah fashewa tayi da kukan batareda sunce mata komaiba jikinta ya Bata tabbas Babu Amina,
Amina ta tafi gurin haihuwa kenan.

Kukan dadah ya Saka babba Dake daki ya idar da sallah fashewa da wani irin kuka Mai qarfi da tsananin radadi me zafin gaske zuciyarsa na yanka.

Tsit gidan yayi sbd kukan da kowannensu keyi me ciwo da qunci.

Dadah na kuka tana yiwa babyn wanka da ruwan zafi masu tsafta sai alokacin babyn ke fasa kuka sosai ba kakkautawa tanayi.

Tana gama mata ta dauko zaninta sabo me tsafta ta nadeta.

Babbah sosai yayi kukan da Saida yakoma Yana bawa dadah da Maryam da yayansa tsoro sosai Dan Babu Wanda ya taba Ganin ko hawayen Babbah bare kukansa hakama kowa yasan soyayyar Amina a ransa ko yayansa bayawa wannan soyayyar.

Fitowa yayi bayan Maryama taci abinci ya Bata kudi me Dan yawa ya sallameta akan itama ta kama hanyar garinsu ta tafi Daman sbd bazai yiyu tafiyarsa da jinjira tin daga Lagos bane ya sakashi tahowa da ita.

Ita kanta Maryama din matse take da Isa garinsu jos Dan haka take ta nufi Tasha komai dare gwara ta Isa nata ahalin itama.

Bayan tafiyar Maryama cikin tsananin tashin hankali da kuka Mai radadi babbah ke sanar da mutuwar da aminatu tayi ta kisan gilla jininta na kwarara a hannuwansa da jikinsa Amma Dan karfin hali Saida ta haife cikin jikinta ta rasa tata rayuwar.

Duk abinda yaketa dannewa tin daga lokacinda ya tsaya gaban gawar Amina Jin yayi Yana yunkuro masa take ya fara amai Yana wani irin jijjiga take ya rikicewa Dadah.

Rawa jikin dadah ya dauka itama kuka takeyi haka su hafizu da Basu wuce shekaru goma Sha biyu ba zuwa Sha hudu suka kama mata shi sukai Kai daki sedai jiki Kam ba sauki.

Mota taje ta samo cikin tashin hankali suka kwashesa zuwa asibiti take akai emergency dashi zuciyarsa ta kumbura komai zai iya faruwa.

Barinsu Hafiz asibiti dadah tayi ta nufi kasuwa ta suyiwa babyn kayan sakawa guda uku da man shafawa Se Madara ta dawo gida ta sauko da ita daga bayanta ta shiryata ta bata Madara a fida kaman yanda inda ta siyo suka nuna mata tareda koya mata.

Tana gama Bata ta sake goyata ta koma asibiti.

Isarta asibiti tararda jikinsa ya sake rikicewa Dan haka itada yaran duka kuka sukeyi sosai cikin mummunan tashin hankali.

**
Acan Lagos Koda gari ya waye Omar ya fita hayyacinsa sosai ga uwa Uba mutuwar Amina data jijjigasa sosai ta taba har cikin kansa,

Jamian tsaro sun fidda gawawwakin da tini suka soye sosai Babu dadin kalla Akai jana’izansu hadda Omar din Wanda ko tsayuwa Baya iyawa a wheelchair yake komai nasa ya tsaya.

Babban tashin hankalin Daya sake girgizasa shine Nur Dake Poland ankira itama tana asibiti tsakanin Rai da mutuwa baa San meya sameta ba Amma kaman taci ko ta shaqa abinda yakeda mummunan poison dan haka tana asibiti tsakanin Rai da mutuwa.

Wannan mummunan labarin Bai wani girgiza Omar ba saima sake Sakasa akan tinanin abinda yaketa yaqi da zuciyarsa da tinaninsa ya kasa yadda wato rayuwarsa Yan uwansa ke so kome? Shin da gaske sunada Saka hannu a lamarin dayake bibiyar rayuwarsa ruwa jallo ko tinaninsa ne ke Neman lalacewa yake zargin Yan uwansa?
Idan haka ne abinda aka haifar masa tana cikin mummunan hadarin rayuwa,
Tayaya zai Bata kariyarda Babu Wanda zai tabata sbd dukiyar duniya?
Kozai rasa komai bazai taba barin wani abu ya samu ‘yarsa daya tak ba da Aminarsa ta haifar masa.

Wasu Hawaye masu dumin gaske ne suka gangaro masa Yana Jin nauyi da radadin zuciya kansa na nauyi me karfi sbd Bai taba tinanin rayuwarsa zata mutu a dare Daya haka ba harma data ‘yarsa da bataji ba Bata Gani ba itada mahaifiyarta data rasu batareda sanin me tayi aka kashetan ba.,

Bai taba kawo tinanin zai samu arzikin samun haihuwa ba Amma ya nesanta kansa da abinda ya samu dan masifar daudar duniya wato kudi ba,
Tayaya zaiyi rayuwa da ‘yarsa idan har Yana riqe da wannan dukiyar yasan har abada dashi da ita bazasu taba zama cikin tsaro ba Dan haka bazai bari asan ma da ita a duniyar ba bare kaiwa rayuwarta hari.

Idan har da gaske Yan uwansa ne masu bibiyar rayuwarsa kaman ta yan

Zuciyarsa kusan kasa dauka tayi take Shima ya samu attack aka sake komawa asibiti dashi cikin gaggawa.

A Daren aka Ahmed yabi jirgi ya Isa gombe ya tararda halinda babba yake ciki ya tausaya musu sosai hakama ya tausayawa Babyn fiyeda kowa a halin yanzu sbd zata taso batareda tasan mahaifinta ba bare waye shi indai har tsawon lokacinda komai zai dawo daidai.

MAMUH

MAM#LAM#OMAR#SEELAHS

JAMAAL JEEY SEELAH

DEEP

HAROON SEELAH

LOVE

CRAZINESS

ZAFIN KAI

AMEENATOU SEELAH

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!


Shi kansa Ahmed wani tsananin kaunar yarinyar yakejin Yana shigarsa har cikin Rai da jininsa,

Jinin Omar abin so da girmamawa ne garesa,
Ahalin Mr Jaden Koda Baya duniya abin kauna ne garesa,
Son duk wani ahali na Mr Jaden tamkar ya tabbata ne garesu shi da Aron Wanda ya tafi Shima yabarsa,

Kaman yanda Aron ya Bada rayuwarsa Dan Bada kariya ga Omar tabbas Shima bazai taba kasa a gwiwansa ba gurin bawa Omar da abinda ya Haifa kariya ba,

Sedai kaman yanda Omar ya yanke shine idan har sunason Bata kariyar da zatai rayuwa a sake batareda tsoro ko fuskantar hadari da barazana ga rayuwarta data Wanda take hannunsu shine barinta a hannun Babbah tareda yin nesa da ita tareda Yanke alaqa dasu gaba Daya har sai ranarda komai ya fito fili ya tabbatarda abinda yake zargi akansu tinda Babu hujjoji manya a hannunsa.,

Wannan shine babban gatan da zaiyiwa ‘yarsa ya Bata kariya shine Yanke alaqa dasu batareda duniya tasan shine ya haifeta ba,
Batareda duniyama tasan yanada ‘yar da zata gajesa ba.

Rungume babyn a jikinsa Ahmed yayi tareda Jin kaman ya tafi da ita ga mahaifinta da zuciyarsa ke cikin tsananin qunci me nauyin gaske akan rashin mahaifiyarta da ita,

Wayarsa ya fiddo ahankali ya Saka Kiran Amintaccen Daya baro a asibitin gurin Omar da securities masu tsananin gaske yace ya bawa Omar wayar.

Duk da Yana cikin wani irin mawuyacin hali ya amsa wayar sbd sanin me Hakan ke nufi.

Ahankali cikin sauti mara karfi da sanyi da nutsuwa yakewa yarsa huduba ta cikin wayar da Ahmed ya Kai kunnenta sautin muryar mahaifinta na shiga kunnan ahankali.

Da sunan mahaifiyarta ya kirata bayan hudubar wato AMEENATOU OMAR JEEDEN SEELAH.

Yana gamawa Hawaye masu radadin gaske suka sauko daga idanuwansa daidai Nan ya kashe wayar tareda lumshe idanuwansa yanajin bazai taba warkewa daga wannan quncin baqin cikin da aka jefa rayuwarsa ba kaman yanda bazai taba yafewa duk Wanda yakeda Saka hannu a cikin duk kowace kisar da akaiwa Yan uwa da iyayensa harma da matarsa da ‘yarsa da aka tilasta masa rabuwa da ita ba Koda kuwa su Lameenun ne da gaske.

Ahmed baicewa Dadah komai ba Saida ya miqa mata AMEENATOU kafin ya sauke jakar dake rataye a jikinsa ya miqa mata ya Bude bakinsa da yayi nauyi ya sanar da ita maganar data qamar da ita daga tsayen tareda dorawa da kalmar

“Allah ya Raya AMEENATOU”

tana kallonsa kaman gunki harya bacewa ganinta ya fice daga asibitin gaba Daya.

Yana fita Kai tsaye a ranar ya juya ya koma sbd Bai yadda da kowa a tareda Omar ba yanzu idan ba kansa ba.

Ko da ya Isa cikin dare Kai tsaye asibitin ya nufa ya tadda jikin na Omar ya sake rikicewa hakama ga babban mamakinsa Alh Lameenu seelah harma da Mam seelah ya diro qasar suna asibitin harma da iyalansu cikin mummunan tashin hankalin da damuwa me tsananin gaske data Saka zuciyar Omar kasa dauka take yaji zuciyarsa na Neman fashewa da yanda suke nuna baqin cikinsu akan abinda ya faru da damuwa shiyasa jikinsa ya rikice.

Abinda yake sake taso masa yaji kansa na Neman bugawa shine sauyin securities da ko yaushe akeyi masa Yana daukan tsananin kulawa ne Ashe na daukan ransa ne.

Kaman yanda Basu nuna komai na haka ya danne nasa baqin cikin yana fatan samun lafiyarsa data Nur tukuna yasan ta yanda zai fara bincike akansu Dan kuwa mutuwar kasim data aminatu itace mutuwa mafi zafi dasukaiwa Yan uwansa.

Ahmed ma Sam Bai nuna komai a fuska ba saima Shirin barin kasar a take Daya fara yiwa Omar Dan ko zasuyi bincike bazasuyisa Omar na kusa dasu ba Dan akwai hadari me girma tattare da Hakan,
Hakama idan a hukuma zasu miqa zancen meye hujja ko evidence nasu Kuma maganace akeyi ta cikin gida me duniya zata fada akan Omar idan Kai tsaye ya fito ya fada Yana zargin Yan uwansa na jini akan kisar matarsa da Yan uwansa a Baya batareda yanada hujja ba.

Ahmed Bai fadawa kowa kasar zasu bari ba shi kadai ya gama shirye shiryen komai hakama washe gari dukkanin abokan kasuwancin Omar take ya hada meeting na gaggawa dasu ya sanar dasu barin Omar kasar kwata kwata Dan haka dole a nada sabon president a kamfaninsa.

Ta bangaren kadarorinsa kuwa duk masu kulawa dasu ya qara musu tsaro da ma’aikata.

Su mam irin kulawan da suke bawa Dan uwansu tareda tattalawa yasa Shima duk da baida lafiya sosai yake nuna Jin dadinsa Yana jinjinawa kaunar da suke masa sukuma Hakan na sake musu dadi sosai ba qaramin tashin hankali suke ciki ba na Lameenu dayace kaman Omar yaso ganesa Dan haka suke ta bibiyar Omar din da kulawa me tsananin gaske Dan su Gano idan ya fahimci wani abin Amma basuga alamar Hakan ba dan sosai yake nuna musu Jin dadinsa akan kulawansu da kaunar junansu na asalin jinin Seelahs.

Basu San da tafiyar ba sai ranarda su Omar din zasu wuce ya sanar dasu zai koma Poland sbd jinyar kansa da Nur da har lokacin take kwance ba sauki.

Kallan juna sukai a sace zufa na Dan jiqa Alh Lameenu ta cikin tsadaddiyar shaddar Dake jikinsa kansa ya Dan Sara Dan kuwa idan har Omar ya tafi me Akai kenan?

Su da suke fatan daga asibitin Nan sai barzahu sbd sun gama kammala komai a asibitin mutuwar tsafta zeyi irin tsarin mamman seelah,

Banbanci Aikin mamman da lameenu shine shi mamman Baya aikin gilla sbd ya tsani Bata jikinsa ko hannuwansa da jinin Wanda ya kawar,
Koyaushe yafison neat aikin da bama zaa San wani ne yayisa ba,
Zai aikaka batareda ko kadan ansan wani ne yayi Hakan ba shiyasa duka ayyukansa dayayi da kansa suke neat ba zargi ba hukuma ba komai,

Ko a qasar turawa dasukeda bincike aikinsa neat ne,
Tin daga kan sirikinsa mahaifin Dr Aleena har sirikarsa da Mr Jaden babu Wanda zai taba kawo tinanin kisa ce ba mutuwar Allah ba Dan haka Babu wani bincike Daya hau kan  mutuwarsu komai nasa a natse hankali kwance yake yinsa shiyasa ya masifar iya takunsa ko a gurin mutane anfi ganin girmansa da mutuncinsa ake masifar girmmamasa Dan ya iya Jan zarensa cikin aji da dubara.

Sabanin Alh Lameenu da shi Kai tsaye yakeyin Abu Babu kwana kwana Babu sauki ba sassauci idan zaiyi aiki da kansa na danyar jini yakeyi Dan kuwa shi jini ne zaa zubar ba Imani ba tausayi bare gudun abin zaije ya dawo shiyasa ma ya buqaci ko yanzu yayi aikin Omar da kansa sbd tabbatarda matsalarsu tazo karshe yasan shine ya kawar da ita matsalan da kansa abinda yake zuciyarsa na shekaru ya fada masa yaji sanyi.

Maganar tafiyar Omar ta girgizasu musamman mamman da yanzu ne yake buqatan daukaka kansa sbd yayansa dasuke gab da Isa riqon dukiyar mahaifinsu su zama matasan da Suma zaa ringa ambatar sunansu da mutuntawa a matsayin yayan Alh Mam seelah,
Hakama babban fargabar Mam itace Omar na komawa Poland ‘dansa dayake jiran ya gama karatunsa ya dawo dashi hannunsa Hakan bazata yiyuba sbd matiqar Omar da Mum dinsa na guri Daya Jamaal bazai taba dawowa Nigeria gurinsa ba shikuwa yanzu Yama fi Jin tsananin so da kaunar Jamaal a tareda shi fiyeda Haroon Dake tareda shi sbd Jamaal Dake nesa yafi shiga ransa sabanin Haroon da kullum suna tare.

Lameenu kuwa shi a yanzu yafi buqatan rayuwar Omar din fiyeda dukiyar tasa,
Idan Omar yabar duniya shine zaiji ya samu nutsuwa sbd ya kasa yadda da Omar Bai ganesa ba yaqi nunawa ne kawai Dan haka shi yanzu asirinsa baa rufe yake ba matiqar Omar na duniya gashi Yanxu Yana maganar yabar inda suke ganin duk wani motsinsa zai tafi inda basa ganinsa Dan haka komai zai iya faruwa Dan haka hankalinsu su dukan baa kwance yake ba da tafiyar.

Ga babban mamakinsu da shock dinsu kafin suyi wani yunkurin rarrashinsa su hanasa tafiyar a ranar ma jirginsu zai daga Ahmed Babu Bata lokaci ya buqaci securities aka rakasu har airport suka daga.

Su Mam Basu sake shiga tashin hankali da firgici ba Saida suka samu tabbacin ba Poland Omar ya koma ba Nur ma tini aka bar Poland din da ita Ashe Kuma daga Dr Aleena har Jamaal Babu Wanda yasan kasar da suka koma Dan Ahmed baibar kowace irin clue ta inda ma suka tattara suka koma din ba sbd Yana buqatan lafiyar Omar da Nur ayanzu fiyeda komai da nutsuwa da samun Kwanciyar hankalisu su dawo daidai tukuna kafin su fuskanci komai.

Kaman bacewar hayaqin Daya tashi sama haka suka bacewa kowa bat Babu labarinsu,
Duk wainda suke communicating dasu Yan amanar asalinsu ne da ko zasu mutu bazaka ji sirrin Omar a bakinsu ba.

Shi kansa Jamaal hankalinsa tashi yayi sosai da Hakan sedai mum dinsa ta kwantar masa da hankali tareda basa tabbacin duk inda Omar yake ya kebance kansa ne Dan bawa kansa kariya da damar samun lafiya tukuna duba da abinda ya samu iyalinsa a lokaci Daya.

Wanna ya Saka hankalin Jamaal Kwanciya Badan ya Dena binciken inda Dad Omar din yake ba.

Su Mam kuwa tini hankali ya tashi musamman da suna zaune cikin damuwa da tsananta binciken akan Neman Omar da kwata kwata ya Yanke kansa daga kowa hatta su duk alaqa da kusancinsu suna matsayin Yan uwansa Bai nemesu ba ya datse hadda su kenan Hakan ya tabbatarda Kila yasan wani abun gameda su kenan ko me?

MAMUH

MAM#LAM#OMAR#SEELAHS

JAMAAL JEEY SEELAH

DEEP

LOVE

ZAFIN KAI

AMEENATOU OMAR JEEDEN SEELAH

ROM

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!

AMEENATOU
Mamuhgee


Shi kansa Ahmed wani tsananin kaunar yarinyar yakejin Yana shigarsa har cikin Rai da jininsa,

Jinin Omar abin so da girmamawa ne garesa,
Ahalin Mr Jaden Koda Baya duniya abin kauna ne garesa,
Son duk wani ahali na Mr Jaden tamkar ya tabbata ne garesu shi da Aron Wanda ya tafi Shima yabarsa,

Kaman yanda Aron ya Bada rayuwarsa Dan Bada kariya ga Omar tabbas Shima bazai taba kasa a gwiwansa ba gurin bawa Omar da abinda ya Haifa kariya ba,

Sedai kaman yanda Omar ya yanke shine idan har sunason Bata kariyar da zatai rayuwa a sake batareda tsoro ko fuskantar hadari da barazana ga rayuwarta data Wanda take hannunsu shine barinta a hannun Babbah tareda yin nesa da ita tareda Yanke alaqa dasu gaba Daya har sai ranarda komai ya fito fili ya tabbatarda abinda yake zargi akansu tinda Babu hujjoji manya a hannunsa.,

Wannan shine babban gatan da zaiyiwa ‘yarsa ya Bata kariya shine Yanke alaqa dasu batareda duniya tasan shine ya haifeta ba,
Batareda duniyama tasan yanada ‘yar da zata gajesa ba.

Rungume babyn a jikinsa Ahmed yayi tareda Jin kaman ya tafi da ita ga mahaifinta da zuciyarsa ke cikin tsananin qunci me nauyin gaske akan rashin mahaifiyarta da ita,

Wayarsa ya fiddo ahankali ya Saka Kiran Amintaccen Daya baro a asibitin gurin Omar da securities masu tsananin gaske yace ya bawa Omar wayar.

Duk da Yana cikin wani irin mawuyacin hali ya amsa wayar sbd sanin me Hakan ke nufi.

Ahankali cikin sauti mara karfi da sanyi da nutsuwa yakewa yarsa huduba ta cikin wayar da Ahmed ya Kai kunnenta sautin muryar mahaifinta na shiga kunnan ahankali.

Da sunan mahaifiyarta ya kirata bayan hudubar wato AMEENATOU OMAR JEEDEN SEELAH.

Yana gamawa Hawaye masu radadin gaske suka sauko daga idanuwansa daidai Nan ya kashe wayar tareda lumshe idanuwansa yanajin bazai taba warkewa daga wannan quncin baqin cikin da aka jefa rayuwarsa ba kaman yanda bazai taba yafewa duk Wanda yakeda Saka hannu a cikin duk kowace kisar da akaiwa Yan uwa da iyayensa harma da matarsa da ‘yarsa da aka tilasta masa rabuwa da ita ba Koda kuwa su Lameenun ne da gaske.

Ahmed baicewa Dadah komai ba Saida ya miqa mata AMEENATOU kafin ya sauke jakar dake rataye a jikinsa ya miqa mata ya Bude bakinsa da yayi nauyi ya sanar da ita maganar data qamar da ita daga tsayen tareda dorawa da kalmar

“Allah ya Raya AMEENATOU”

tana kallonsa kaman gunki harya bacewa ganinta ya fice daga asibitin gaba Daya.

Yana fita Kai tsaye a ranar ya juya ya koma sbd Bai yadda da kowa a tareda Omar ba yanzu idan ba kansa ba.

Ko da ya Isa cikin dare Kai tsaye asibitin ya nufa ya tadda jikin na Omar ya sake rikicewa hakama ga babban mamakinsa Alh Lameenu seelah harma da Mam seelah ya diro qasar suna asibitin harma da iyalansu cikin mummunan tashin hankalin da damuwa me tsananin gaske data Saka zuciyar Omar kasa dauka take yaji zuciyarsa na Neman fashewa da yanda suke nuna baqin cikinsu akan abinda ya faru da damuwa shiyasa jikinsa ya rikice.

Abinda yake sake taso masa yaji kansa na Neman bugawa shine sauyin securities da ko yaushe akeyi masa Yana daukan tsananin kulawa ne Ashe na daukan ransa ne.

Kaman yanda Basu nuna komai na haka ya danne nasa baqin cikin yana fatan samun lafiyarsa data Nur tukuna yasan ta yanda zai fara bincike akansu Dan kuwa mutuwar kasim data aminatu itace mutuwa mafi zafi dasukaiwa Yan uwansa.

Ahmed ma Sam Bai nuna komai a fuska ba saima Shirin barin kasar a take Daya fara yiwa Omar Dan ko zasuyi bincike bazasuyisa Omar na kusa dasu ba Dan akwai hadari me girma tattare da Hakan,
Hakama idan a hukuma zasu miqa zancen meye hujja ko evidence nasu Kuma maganace akeyi ta cikin gida me duniya zata fada akan Omar idan Kai tsaye ya fito ya fada Yana zargin Yan uwansa na jini akan kisar matarsa da Yan uwansa a Baya batareda yanada hujja ba.

Ahmed Bai fadawa kowa kasar zasu bari ba shi kadai ya gama shirye shiryen komai hakama washe gari dukkanin abokan kasuwancin Omar take ya hada meeting na gaggawa dasu ya sanar dasu barin Omar kasar kwata kwata Dan haka dole a nada sabon president a kamfaninsa.

Ta bangaren kadarorinsa kuwa duk masu kulawa dasu ya qara musu tsaro da ma’aikata.

Su mam irin kulawan da suke bawa Dan uwansu tareda tattalawa yasa Shima duk da baida lafiya sosai yake nuna Jin dadinsa Yana jinjinawa kaunar da suke masa sukuma Hakan na sake musu dadi sosai ba qaramin tashin hankali suke ciki ba na Lameenu dayace kaman Omar yaso ganesa Dan haka suke ta bibiyar Omar din da kulawa me tsananin gaske Dan su Gano idan ya fahimci wani abin Amma basuga alamar Hakan ba dan sosai yake nuna musu Jin dadinsa akan kulawansu da kaunar junansu na asalin jinin Seelahs.

Basu San da tafiyar ba sai ranarda su Omar din zasu wuce ya sanar dasu zai koma Poland sbd jinyar kansa da Nur da har lokacin take kwance ba sauki.

Kallan juna sukai a sace zufa na Dan jiqa Alh Lameenu ta cikin tsadaddiyar shaddar Dake jikinsa kansa ya Dan Sara Dan kuwa idan har Omar ya tafi me Akai kenan?

Su da suke fatan daga asibitin Nan sai barzahu sbd sun gama kammala komai a asibitin mutuwar tsafta zeyi irin tsarin mamman seelah,

Banbanci Aikin mamman da lameenu shine shi mamman Baya aikin gilla sbd ya tsani Bata jikinsa ko hannuwansa da jinin Wanda ya kawar,
Koyaushe yafison neat aikin da bama zaa San wani ne yayisa ba,
Zai aikaka batareda ko kadan ansan wani ne yayi Hakan ba shiyasa duka ayyukansa dayayi da kansa suke neat ba zargi ba hukuma ba komai,

Ko a qasar turawa dasukeda bincike aikinsa neat ne,
Tin daga kan sirikinsa mahaifin Dr Aleena har sirikarsa da Mr Jaden babu Wanda zai taba kawo tinanin kisa ce ba mutuwar Allah ba Dan haka Babu wani bincike Daya hau kan  mutuwarsu komai nasa a natse hankali kwance yake yinsa shiyasa ya masifar iya takunsa ko a gurin mutane anfi ganin girmansa da mutuncinsa ake masifar girmmamasa Dan ya iya Jan zarensa cikin aji da dubara.

Sabanin Alh Lameenu da shi Kai tsaye yakeyin Abu Babu kwana kwana Babu sauki ba sassauci idan zaiyi aiki da kansa na danyar jini yakeyi Dan kuwa shi jini ne zaa zubar ba Imani ba tausayi bare gudun abin zaije ya dawo shiyasa ma ya buqaci ko yanzu yayi aikin Omar da kansa sbd tabbatarda matsalarsu tazo karshe yasan shine ya kawar da ita matsalan da kansa abinda yake zuciyarsa na shekaru ya fada masa yaji sanyi.

Maganar tafiyar Omar ta girgizasu musamman mamman da yanzu ne yake buqatan daukaka kansa sbd yayansa dasuke gab da Isa riqon dukiyar mahaifinsu su zama matasan da Suma zaa ringa ambatar sunansu da mutuntawa a matsayin yayan Alh Mam seelah,
Hakama babban fargabar Mam itace Omar na komawa Poland ‘dansa dayake jiran ya gama karatunsa ya dawo dashi hannunsa Hakan bazata yiyuba sbd matiqar Omar da Mum dinsa na guri Daya Jamaal bazai taba dawowa Nigeria gurinsa ba shikuwa yanzu Yama fi Jin tsananin so da kaunar Jamaal a tareda shi fiyeda Haroon Dake tareda shi sbd Jamaal Dake nesa yafi shiga ransa sabanin Haroon da kullum suna tare.

Lameenu kuwa shi a yanzu yafi buqatan rayuwar Omar din fiyeda dukiyar tasa,
Idan Omar yabar duniya shine zaiji ya samu nutsuwa sbd ya kasa yadda da Omar Bai ganesa ba yaqi nunawa ne kawai Dan haka shi yanzu asirinsa baa rufe yake ba matiqar Omar na duniya gashi Yanxu Yana maganar yabar inda suke ganin duk wani motsinsa zai tafi inda basa ganinsa Dan haka komai zai iya faruwa Dan haka hankalinsu su dukan baa kwance yake ba da tafiyar.

Ga babban mamakinsu da shock dinsu kafin suyi wani yunkurin rarrashinsa su hanasa tafiyar a ranar ma jirginsu zai daga Ahmed Babu Bata lokaci ya buqaci securities aka rakasu har airport suka daga.

Su Mam Basu sake shiga tashin hankali da firgici ba Saida suka samu tabbacin ba Poland Omar ya koma ba Nur ma tini aka bar Poland din da ita Ashe Kuma daga Dr Aleena har Jamaal Babu Wanda yasan kasar da suka koma Dan Ahmed baibar kowace irin clue ta inda ma suka tattara suka koma din ba sbd Yana buqatan lafiyar Omar da Nur ayanzu fiyeda komai da nutsuwa da samun Kwanciyar hankalisu su dawo daidai tukuna kafin su fuskanci komai.

Kaman bacewar hayaqin Daya tashi sama haka suka bacewa kowa bat Babu labarinsu,
Duk wainda suke communicating dasu Yan amanar asalinsu ne da ko zasu mutu bazaka ji sirrin Omar a bakinsu ba.

Shi kansa Jamaal hankalinsa tashi yayi sosai da Hakan sedai mum dinsa ta kwantar masa da hankali tareda basa tabbacin duk inda Omar yake ya kebance kansa ne Dan bawa kansa kariya da damar samun lafiya tukuna duba da abinda ya samu iyalinsa a lokaci Daya.

Wanna ya Saka hankalin Jamaal Kwanciya Badan ya Dena binciken inda Dad Omar din yake ba.

Su Mam kuwa tini hankali ya tashi musamman da suna zaune cikin damuwa da tsananta binciken akan Neman Omar da kwata kwata ya Yanke kansa daga kowa hatta su duk alaqa da kusancinsu suna matsayin Yan uwansa Bai nemesu ba ya datse hadda su kenan Hakan ya tabbatarda Kila yasan wani abun gameda su kenan ko me?

MAMUH

MAM#LAM#OMAR#SEELAHS

JAMAAL JEEY SEELAH

DEEP

LOVE

ZAFIN KAI

AMEENATOU OMAR JEEDEN SEELAH

ROM

ASHNA BEAUTY SKINCARE
Free class free class 
Assalamu alaikum yar uwa kina neman inda zaki koyi sanaa wadda zaki dugara dakanki Ashna skincare and more tazu muku da garabasa ta musamman inda zata kawu muku yanda ake hada wannan abubuwan kyauta
Carwash
Airfreshner
Liquid soap
Gamasu nemana hanyar shiga zaku nemeta ta wannan number kamar haka whatsapp only 09031383058
Karku Bari wannan damar ta wuceku

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!

AMEENATOU
Mamuhgee


A gombe kuwa Koda Babbah ya samu kansa ya farfado cikin Dan saukin Daya samu dadah tayi kukan Daya sauya kamannin fuskarta harta gaji,

Tayi kukan rashin Amina,
Tayi kukan tausayin babyn da Amina ta bari,
Tayi kukan tausayin Babba da yanda zai rayu cikin quncin da har abada bazai bar zuciyarsa ba na rasuwar Aminansa.

Kallo Daya Babbab yayiwa Dadan cikin ciwo yaji zuciyarsa ta sake samun rauni,
Yar datake rungume a jikinta ya kalla kafin ya miqa hannuwansa Dake wani irin rawa da rashin karfi yace ta doro masa ita.

Hadiye hawayen idanuwanta tayi kafin ta matso ta Dora masa babyn Daketa baccinta hankali kwance.

Rungumeta yayi jikinsa Yana tina ranarda mahaifiyarsa ta haifi Amina ta rasu ta bar masa ita a hannunsa a rungume,

Cikowa idanuwansa sukai da hawayen da suka kasa riquwa Saida suka gangaro kan fuskarsa data fada lokaci Daya kaman ya Dade a kwance Yana jinyar.

Gawar Aminansa ce ta dawo a idanuwannsa lokacinda take cikin jini Tako ina a jikinta.

Sake rungume babyn yayi Yana Jin duk wata so da kaunar dayake wa Aminansa ta ninkuwa so Babu adadi akan ‘yar Dake hannunsa,
Idan Yana yiwa Amina kauna ninki dari to yana Jin yanawa ‘yarta so dubu,
‘yar hannunsa kyauta ce da Allah ya basa bayan ya amsar masa Amina,
Duk Wanda yakeda Saka hannu a kan mummunan kisan da akaiwa Aminarsa to matiqar zai sansan bazai taba barin yayi mutuwar mutunci ba Amma tinda Allah ya bar masa abinda Amina ta Haifa Yana yiwa Allah Godia hakama bazai taba barin ko wani Mai sunan Omar ya kusanci wannan yar ba bare wani abin ya sameta kaman yanda ya samu mahaifiyarta.

Sakon da Dadah ta sanar masa akan Omar ya buqaci da har abada idan bashine ya nemesu ba kada su taba fadawa duniya ko kowa cewan ‘yarsa ce wannan ba,
Kada su taba barin asan waye mahaifinta koma tanada hadi da jininsa gaba Daya idan har suna son tseratar da ita su Bata kariya to su Yanke alaqa da komai Daya danganci ko sunansa ga wannan ‘yar.

Wainnan kalaman sune sukai tsananin tarwatsa zuciyar Babbah fiyeda radadin dayake ji,
Shi dayake jiran bayanin dalilin mutuwar yar uwarsa a bakin Omar din shine zai Yanke alaqar komai dasu tareda Yanke alaqa hadda ta sunansa akan yarsa.

Wani nauyi kirjinsa ya dauka tareda zafi me tsananin gaske,

Dago babyn yayi daga kirjinsa ya Kai bakinsa kunnenta yayi mata huduba Shima a hankali cikin so da kulawa me tsananin gaske kafin Shima ya Bude Baki ya ambaceta da sunan AMEENATOU NUHU BABBAH batareda yasan sunan da mahaifinta Shima ya kirata dashi ba kenan na mahaifiyarta Dan haka yarinya taci sunan mahaifiyarta AMEENATOU
Banbanci kawai shi mahaifinta ya kirata da AMEENATOU OMAR JEEDEN SEELAH shikuwa Babbah ya ambaceta da AMEENATOU NUHU BABBAH.

duk wani taurin zuciyan Babbah da rashin hakurinsa dawowa yayi sabo fil a take Dan haka da karfin hali ya kwana gari na wayewa yasa aka sallamesa batareda ya warke yanda ya kamata ba Amma yanda yakejin zuciyarsa idan ba abinda zuciyarsa keso yayiba zai iya samun bugawar zuciya Dan haka Kai tsaye gida suka nufo.

Suna dawowa wanka kawai yayi ya fice daga gidan.
Bai dawo ba sai dare.

Yana dawowa ko abinci Bai iya ci ba ya shige dakinsa haka suka kwana jigum jigum kaman gidan zaman makoki.

Da sassafe sai ga baqi sunzo gurinsa.

Dadah na daki tanaji Akai cinikin gidan aka Kai karshe batareda tsayawa lissafin komaiba Babbah ya sallama gidan take aka Saka masa kudin a banki tareda rubuce rubuce da shedu ya miqa takardun gidan.

Suna wucewa ya sanar da Dadah duk abinda sukeyi a siyar da komai yau washe gari zasu bar garin.

Da farko hankalinta ya tashi Amma duba da yanda komai yake tafiya da abinda ya faru itama taji zatafi samun nutsuwa Subar inda aka Sansu su koma inda Babu Wanda ya Sansu su Gina sabuwar rayuwa tareda Ameenatou Dan Bata cikakkiyar rayuwar yancin data cancanta.

Tin a ranar suka fara shirye shiryen barin gari sedai Basu samu wucewa washe garin ba Saida Babbah yayi tafiyar kwana shida ya dawo yaje ya Siya musu gida a inda Babu Wanda ya Sansu Kuma baa birni sosai ba a local government sbd samun nutsuwa.

Sunyi bankwana da makota da abokan arziki da kasuwanci sun bar garin gombe batareda sanarwa kowa inda zasu komaba sbd ita kanta Dadah babban Bai sanar da ita ita zasu koma dinba sbd tsaro sedai sunje ta Gani.

Tafiyar wuni guda Mai Nisan gaske sukai sai gasu a wani garin da Dadah Batama tantance sunansa ba Amma dai akwai Fulani sosai a garin dayake a gajiya sosai Bata damu da tsayawa tambayar babban ba gashi dare yayi Dan haka Kai tsaye Dan karamin gidansu Daya Siya musu suka Isa Wanda yake sabo ne daidai misalin rufin asiri Kuma ya Siya komai ya zuba tin daga kan katifun Kwanciya da Yan abubuwan amfani.

Ruwan zafi ya fita ya siyo sukasha shayi da bread sai indomie,
Hakama ya sake fita ya samo ruwan zafi a gurin me shari Wanda bana shayin ba akaiwa Ameenatou wanka aka gasata sosai sauran su Hafiz suka sukai wankan,
Shima babban wankan yayi Dana sanyi itama dadah Dana sanyi tayi
Dayake sun Riga sunyi sallolinsu tini suka kwanta sai baccin wahala da rashin dadin Rai.

Washe gari duk wani sauran abinda basuda Saida ya fita ya siyo musu shi ya kawo,
Abinci ma haka ya Siya Wanda zai Dade musu Bai qare ba ya ajiye,

Bai taushe hannu ba ya bazama yaje ya nema makaranta ya Saka su hafiz a a biya kudin da komai daga bokon har Arabic sbd so yake Kai tsaye ya fuskanci rayuwarsa shida iyalinsa,

Kayan baby Ameenatou kuwa tin daga kayan sakawa har Madara da abubuwan buqatanta Babu abinda Bai siyo ba Dan haka dadah itama ta sake jikinta yanda ya kamata tana kulawa da ita tamkar ma itace ya haihu Dan duka makota da Wanda suka ringa shigowa suna gaisawa sun dauka itace ta haihu din itama Bata Musa din ba sai aketa mata barkan haihuwan ana tambayar sunan yar.

Dayake baai mata yankan suna ba sai da sukai kwana biyu sun gama hutawa da gyaran gidan kafin Babba ya yankawa Ameenatoun tasa rago Akaci Akai sadaka.

Tin dukkaninsu sunata fama da kadaici da bakunta har suka fara sabawa tini dadah tafara Yan sana’ointa data Saba Yara ma sun fara zuwa makaranta tini,

Babbah ma shago ya Bude a kusa ba nesa ba na siyarda hatsi Dan haka suka dauki hanyar zama Yan gari musamman Babbah Daya danne komai ya koma babbansa na Baya sbd kawai su zama cikin farin cikinda idan Ameenatou ta tashi itama zata tashi cikin farin ciki tsakanin iyayenta Dan baida niyar tasan basune asalin wainda suka haifetaba duk da sunyi mata tsufa a iyayen Amma dai sune suka haifetan kawai.

Dan haka ahankali suka nitsa rayuwa na tafiyar dasu cikin Kwanciyar hankali da amince Dan tini ya rufe Babin Omar a rayuwarsa data iyalinsa Dan kuwa bayajin har abada zai bari Omar ma yasan inda suke bare tinanin ma yanada ‘ya a hannunsu.


Lagos

Zaune suke duk inda jini yake yawo a jikin Mam seelah tafasa yakeyi Yana Jin kaman kansa zai rabe sbd baqin ciki da damuwa.

Shikuwa lameenu tini yafara ficewa hayyacinsa sbd kansa Bai sake cikakkiyar lafiya ba tinda lamarin Nan ya faru sbd ya kasa tantance gaskiyar abinda yake gudana a Kai da zuciyar Omar Wanda har lokacin baida alaqa da kowa Babu labarinsa.

Ga dukiyar dai ya tafi yabarta kusan a hannunsu Dan duka kadarorinsa yanzu kusan a hannunsu suke amman Sam basuda nutsuwan cinsu tinda basuda tabbacin Shirun nasa na Menene,
Amma dai ko na Menene Abu Daya suka tabbatarda shi shine fitowarsa Koda zasuyi gaba da gaba ne saisun kar karshen matsalarsu Dan yanzu rayuwarsa ma itace abin buqatan tinda yasan Menene sukai masa.

Shigowar BB babban Dan hannun damarsu Mam dinne ya Saka Lameenu dagowa da idanuwansa dasukai ja ya kallesa kafin yayi magana cikin girmamawa BB ya Kalli Lameenun kafin ya Maida kallansa kan Mam Yana Dan sauke Kai cikin nasa zafin zuciyar da fargaban abinda zai fada yace

“Ranka ya Dade binciken da muketa son tabbatarwa akan gawawwakin da jamian tsaro suka fitar bayan kashe gobarar gidan gaskia ne gawa uku kadai aka samu daga cikin gida sai gawar security dinnan Daya daga waje bayan Kuma idan aka cire Sir Omar da Ahmed gawa BIYAR ya kamata a Gani a cikin gidan…….

Wani mugun zufa me zafin gaske ne ya tsinkowa lameenu kansa na sarawa
Shikuwa Mam wata mummunan sarawa kansa yayi ya dauki ruwan Dake gabansa yakai bakinsa Yana Sha sbd Jin koina jikinsa kaman Yana ci da wuta.

Dan gyara tsayuwa BB yayi Yana kallan Lameenu Daya zuba masa ido Yana jiran sauran bayanin yaji Shima wani zufa ya tsitsifo masa sbd abinda zai fada yace

“Cikin gawawwakin da aka samu an samu tantancewa da tabbacin akwai ta matar sir Omar din Amma Kuma Babu ciki a jikin gawar Wanda ni Kuma ta tabbatarda naga tsohon ciki a tareda ita a Daren……..

Ruwan da Mam ke Sha ne suka dawo ta hancinsa gaba Daya ba shiri sbd mummunan tashin hankalin da Bai taba Jin irinsa ba.

Lameenu kuwa take bugun zuciyarsa ya Nemi tsayawa cak sbd firgicin da Bai taba samun kansa ciki ba.

MAMUH

AMEENATOU

DR J SEELAH

DESTINED

LOVE

ROMANCE

LIFE

REVENGE

HAROON SEELAH

IDENTICAL TWINS

ZAFIN KAI

THE SEELAHS

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

17
Shi kansa BB zufan yaje hadawa zuciyarsa na tsalle Dan yasan ansamu babbar matsala data jawo musu wani Sabon aikin me girma daban.

Mam kuwa bayan ta hanci da ruwan suka biyo bar cikin kansa sukai yaji Yana Neman zaucewa da sauri ya dago idanuwansa da suka sauya take zuwa jajir ya Kalli BB dukkanin jikinsa na Neman sakewa daqyar ya hado kalmomi a bakinsa cikin sanyi da nutsuwan son fahimtar komai daki daki yace

“Wane ciki kake Bada tabbacin ka Gani a jikin matar Omar?
Na haihuwan Dan mutum kokuwa na samun qoshi datai a gidan??”.

Kansa ya saukar kasa bayan ya Kalli lameenu Wanda shi kwata kwata Neman rasa gane komai yakeyi
Ya Dan sake saukar da kansa qasa yace

“Tabbas cikin haihuwa ne a jikinta,
Kuma kaman yanda Daya daga cikin securities dinmu Dake ganin gidan ya tabbatar mana tabbas tana daukeda juna biyu tsoho matar Sir Omar din..

Hakama a Daren Koda muka shiga ni naga cikin da idanuwana sedai abinda yasa ban fada ba na dauka ba amfani tinda itada cikin sun tafi kenan sai gashi ance Babu ciki a jikin gawarta hakama baa samu gawar baby Koda konanniya ce a gidan,
Gashi Babu sauran mutum biyu Daya kamata Suma ace an samu gawarsu a gidan,
Dame aikinta Daya Wanda kowa ya tabbatarda masu aikinta biyu ne hakama a Daren ranar shi Sir Omar din yayi baqo Wanda bamusan ko wayeshi din ba a gun sir Omar din
a cikin gidan ya kwana muma da idonmu mun gansa mun sumar dashi Amma baa samu gawarsu ba…..

Jinin Mam da lameenu wata irin qunar masifaffen tashin hankali sukeyi musamman Lameenu da idanuwansa suka rufe baiga cikinba da Saiya tabbatarda a tsakiyar cikinta zai kutsa azabbiyar wuqarsa me barka kayan cikin mutum ya tabbatarda mutuwar haihuwar magaji ko magajiyar Omar jeden seelah.

Mam kuwa a Karan farko da zufar tashin hankali mara misaltuwa ta rufesa sbd babbar babbar uwar matsala da budaddiyar masifa ta riga ta fadowa rayuwarsu tinda Omar ya rufesu akan samun haihuwarsa hakama idan har Babu ciki a jikin gawa Kuma Babu gawar baby a gidan to ta tabbata Omar ya boye abinda aka haifar masa hakama idan ya boye abinda ya Haifa Hakan na nufin ya San wani abu Dan bazai yiyu Babu komaiba Omar ya boye musu haihuwarsa ta farko daya kamata ace sune sukaiwa abinda aka haifar huduba Dan shine kaf yakewa nasu yayan huduba.

Wace sabuwar masifar ce wannan ta bullo musu?
Me Lameenu yayi?
Tayaya zaace yaje yayi aiki irin wannan da kansa Amma ya kasa tantance ciki a jikin Amina..

Cikin wani irin mafi girman tashin hankali da sake jiquwa a zufan gaske duk ac Daya gama cika palon Lameenu yace

“Kenan nakudar haihuwa takeyi a Daren Kokuma wani abin na damunta sbd a dakinta me aikinta Daya take tareda ita hakama Shima Omar ya fito a cikin Daren har harabar gida…… innalillahi wainna ilaihirrajiun.

Wani kallan baqin ciki da tashin hankali Mai tsananin gaske Mam yayiwa Lameenun Yana Jin inama dashi su BB suka hada suka kashe cikin duhun ya huta da baqin cikin dayake ji yanzu akan wannan shirmen da baqar ranar Daya nuna musu Dan samun haihuwan Omar itace babbar baqar kaddarar data sake Hawa kansu tinda Babu yanda zaayi ko sun kashe Omar dukiya ta zama tasu yanzu yanada me gadons gaba Daya,

Kashe Omar batareda sun tabbatarda sun gane inda abinda aka haifar masa yake ba kaman aikin banza ne Dan haka dole saisun fara kawar da magaji ko magajiyarsa sun tabbatarda babu me gadonsa bayansu kafin su kawar dashi,

Gaba Daya yanzu lameenu ya jiqa masu aiki ya dawo musu dashi Baya,
Ta Ina zasu fara da sanin inda ma zasu Gano mutanen biyu Dan idan ma akwai haihuwan ko Babu a bakinsu zasu tabbatarda komai a zahiransa.

Lameenu ma Jin yayi zuciyarsa da gangar jikinsa na rawa sosai akan ta inda zasu fara Neman wannan haihuwar da itace tayi musu shamaki yanzu da cikar buri bama Omar din ba Dan kuwa shi fitowarsa kadaice ta shiga tsakaninsa da mutuwarsa Dan kawar dashi ya zama dolen dole tinda yasan komai dabai kamata ya sani ba akansu.

BB kansa ma cikin baqin ciki da zafin zuciyar samun wannan babbar matsalar a aikinsu yakeji duk da yanzu ko zasu rayukan mutane dari saisun Nemo inda mutum biyun Nan suke Dan wannan Karan Mam seelah ne da kansa sai cike aikin batareda barin matsala ya kawar da matsalarsu.

Dayake Lameenu yasan shine ya Bude kofar wannan sabuwar masifar data samesu Kuma yasan Mam Bai taba samun matsala a abu ba idan ya tashi aiwatarwa a natse yake cikakkiyar aikinsa ba damuwa Dan haka duk yashiga damuwa kan tashin hankali Amma dai koma yayane yasan bazasu taba samun baccin nutsuwa daga Nan har shekaru masu zuwa matiqar Mam Bada hannunsa ya kawo karshen jinin Omar ya batar dashi a duniya ba.

Babban arzikin Omar yaci shine Basu taba sanin qanwar mijin Ayshatu kanwar kasim yake aure ba,
Hakama Basu taba sanin waye ma mijin Ayshatu din ba bare inda yake Dan haka suka bazama sakin mahaukaciyar dukiya Baji ba Gani Mai aikin gidan Omar jeden suke nema da baqonsa,
Amma dai me aikin sukafi Maida hankali nema itada aka sani sbd shi baqon haryanxu basuda tabbacin wayeneshi?
Daga Ina yake?
Meye alaqarsa da Omar din?
Yaya kamanninsa suke?
Dan haka Maryama suke nema ido rufe Baji ba Gani,
Ta bangare Daya kuwa su aje matsalar Omar a gefe saisun gama data abinda ya Haifa din Wanda suke da tabbacin Yana sane ya boyesa koma inane sbd kada su sani.

****Ahankali ahankali Suma cikin tsananin rashin Kwanciyar hankalin zuciya da tsananin son cikar buri lokaci da shekaru suka ja musu batareda sun samu sanin inda Maryama take ba Amma dai Basu taba cire Rai kona daqiqa bane daga tsananta bincikensu Wanda duk tsawon shekarun da aka dauka wannan burin koyaushe karfi da zaquwa yake qarawa ransu sbd kullum dukiyar Omar tamkar hakin da ake bawa ruwa takeyi sai yaduwa take sake yi tsananin Sonta da maitarta na karuwa ransu tana yaduwa a jini da gangar jikinsu tareda tsiruwa a zuciyarsu duk kuwa da daukaka da tarin arzikin da Suma suketa qaruwa a rayuwarsu.


Shekaru sun tafi a yanzu Sunan SEELAHs Babu inda Bai shiga ba Dan kuwa sunyi wata irin kafuwar da Babu Wanda zai iya girgizasu idan ba ubangijin Daya Basu ba,

Sunyi suna me karfin gaske,
Sunada power fiyeda yanda ake tinani,
Sune masu fada aji,
Masu taka Wanda suka so,
Masu yin yanda suke so,
Nera da dollar sun zaunu a SEELAHs kaman basusan meye matsala ba a rayuwarsu,

Tin shekarun da suka gabata suka tashi daga inda suke suka sauya anguwar datafi kowace anguwa tsaro da tarin asalin masu nerar data amsa sunanta nera,

Kaman yanda gidajensu suke a jere acan Baya hakama yanzu mansions dinsu a jere suke guda uku sbd duniya su uku ta sani haka zasu cigaba da zama su ukun har sai Omar yabar duniya Dan haka Koda suka tashi barar da dukiya aka Gina mansions din da Omar sukayi duk da har lokacin Bai taba dawowa Nigeria ba duk da ya bayyana Amma inda yake rayuwa yanzu komai dukiyar dasuke ji Dan ita Basu Isa su tinkaresa da matsala ba a gurin sbd shi kansa ya goge sosai yanzu baida wani sanyi ko kawaici kaman Omar din Baya sosai yake tafiyarsa business dinsa da rayuwarsa batareda ya waiwayo Nigeria hakama Yana sane yaqi waiwayo yarsa yafison yagama ganin gudun ruwan Yan uwansa Dan Yana bayyanarda ita zata zama cikin hadari duk tsaron dayakeda shi bazai iya wasa da rayuwarta ba ya daukota ba Dan yasan ko Babbah zai rasa ransa Yana can Yana kulawa da ita cikin Kwanciyar hankali da tsaro musamman dasuka samu tabbacin su kawun sun bace Babu me labarin inda suke duk bincike kuwa su kansu Basu Gano inda suke ba Dan haka ma ya kyalesu sai koma ya lafa zai nemeso duk inda suke.


DR JAMAAL SEELAH Wanda aka Fi sani da DR JEEY SEELAH matashin likitan daya qware sosai a aikinsa,
Likita ne da ba iyayensa kadai ba dukkanin mutane suke tsananin alfahari dashi sbd qwarewansa akan aikinsa duk da ta bangare Daya mutum ne Mai tsananin zafin Kai da Baya daukan reni barema kallan kadai idan kayi kaine kake Rena kanka sbd asalin abinda ake kira da kwarjini da Asalin class me sakaka kama kanka kawai daga ganinsa.

Duk duniyarsa mutum uku ne kadai suke ganin Asalin dariya ko kyakkyawar murmushinsa Dake kashe me kallansa,

Daga mahaifiyarsa Rabin ransa da Babu Wanda ya Kai masa ita a duniya,
Sai ‘dan uwansa Rabin jikinsa Barr Haroon seelah sai patients dinsa Suma ba duka ba,

Bayan wainnan ko mahaifinsa dayake tsananin sonsa fiyeda duk abinda ya mallaka Baya ganin wainnan abubuwan daga garesa.

JEEY SEELAH shine Asalin definition na SEELAHs kaman yanda Dad dinsa me fada sbd rashin tsoronsa da zamana Dan Kai tsaye hakama reni Baya tinkarosa,
Izzarsa da nutsuwarsa tareda class me sanyi ko su iyayensa sun shafa masa lafiya kwarjininsa suke Gani suna daga masa kafa ba kamar Haroon ba duk da idan ba nutsuwa kayi ka tantance kamewan JEEY ba kwata kwata haryanxu baka taba ganesu sbd kamanninsu sosai suke sake kamewa Dana juna.

DR JEEY SEELAH shi gaba Daya kusan rayuwarsa a Poland yayita da mahaifiyarsa harya gama karatu ya fara aiki acan kafin ya tattara ya dawo Nigeria sbd takurawar Dad dinsa da Dan uwansa Amma dai Yana yawan zuwa duba mahaifiyarsa,

Akwai rayuwar turai sosai a tattareda shi musamman duba da yanda yake gudanar da rayuwarsa Dan kwata kwata baya iya rayuwa gida Daya da iyayensa Dan haka Akai masa part dinsa daban a cikin mansion din Wanda yakeda Dan nesa da bangaren su Dad da Haroon.

Bayan banbancin halayya da rayuwa tsakaninsa da haroon akwai na hasken fata Wanda shi yafi Haroon sbd banbancin tsadaddiyar rayuwar da sukeyi komai nasa na musamman ne da ko mace kafin a samu me gudanar irin wannan classy rayuwar sai an tona.

MAMUH

DR JEEY SEELAH

BARR HAROON SEELAH

AMEENATOU BABBAH

THE SEELAHS

ROMANCE

ZAFIN KAI

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

Al’ummar NIJER kuma ku nemi wannan number don yin naku payment din 09033181070

karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!

18
Shekarun Dr Jamaal Seelah Kusan 15 zuwa 16 da dawowa hannun Dad dinsa kwata kwata,
Kuma a wainnan shekarun abubuwa da yawa sun faru wainda suke akan wani matsayi na daban.

Tinda Jamaal ya dawo gurin mahaifinsa ya zama dukkanin wani abin alfahin Dad din sbd iliminsa da zafin kansa a komai daban yake Dana kowa dayake cikin ahalin seelahs,

Likita ne shi Kuma marikin dukiyar mahaifinsa ne shi Mai kulawa da kusan duka kamfaninsu batareda Saka hannun Haroon aciki ba sbd gaba Daya Haroon ya koma tamkar wani matsoraci kaman yanda Dad din ke fada shiyasa kwata kwata Dad din Baya wani yinsa.

Haroon shine yasan ciki da wajen huldodin su Dad sosai sbd shine lawyer dinsa a yanzu Daya zama cikakken lawyer me zaman kansa Kuma kwararren Daya San aikinsa,
Yasan duka boyayyun illegal huldodinsu da Babu Wanda JEEY ya sbd tsananin taka tsantsan da boyewan da suke masa Dad Baya kaunar yasan ko aikinsa Daya mara kyau Dan kuwa JAMAAL din na sani zai iya barinsa har abada ya komawa Dr Aleena Kuma zai iya Jin haushi ko tsanarsa ko janyewa daga garesa Dan haka duk wata mummunan boyayyar harkarsu Babu wadda JAMAAL SEELAH ya sani suna tsananin kiyaye Hakan,

Haroon Daya San komai baida ikon fadawa JAMAAL din bare Bude hanya komai kankantarta da JAMAAL din ze sani hakama shi Daya sani Yana taka tsantsan sosai akan bayyanar sirrinsu sbd sanin hukunce Sharia da shariar kanta,
Sharia da aikin shariar ya ratsasa sosai da yake kiyaye kaidojin aikinsa Baya shiga shiga huldodin Amma dai shine me riqe da mukullin rufe sirrin batareda barin hanyar fitarsa ko kadan ba hakama Baya taba barin kowace matsalar da zata bayyanarda huldar iyayensa ta aikin danyar zinariyar Dake tafiya da rayukan mutanen da Basu da adadi ba hakama da drugs masu tsananin hadarin gaske wainda BB ne akan wannan bangaren duk da shine riqe da sirrinsu na boye da babu Wanda ya sani Haroon din Shima baisan iyayen nasu sun taba dauka rayukan mutane da hannuwansu ba Kuma Yan uwansu tamkar jininsu Dan haka Bai taba kallan Dad dinsa ko daddy lameenu a matsayin komai ba face jajirtaccin Dake Gina ahalin seelahs a boye batareda sanin irin gwagwarmayar dasuke fama da ita ba.

JAMAAL SEELAH a yanzu da dukiyarsu da komai yake hannunsa Yana gudanar dasu ne akan ilimi da kwarewa sosai dukiyarsu Daketa business din gaskia da duniya ta sani take sake habbaka da samun cigaba da nasarori Dan haka Dad ke sake Jin tsananin alfahari da farin cikin kasancewar Dr Jamaal Seelah dansa ne jininsa ne.

A can Poland a asibitin mahaifiyarsa yake aiki Amma anan din duk girma da tsari tareda dukiya me yawan da Dad dinsa ya kashe aka Gina masa asibitinsa ta kansa maidata yayi asibitin marasa karfi da tallafi Dan kuwa raayinsa ne gidan asibitin duba mara lafiya cikin tsananin sauki da Bada taimako sosai.

Hakan da yayi Dad Bai hanasa ba Bai Kuma nuna komaiba duk da Hakan yayi tsananin Bata ransa Se kawai sukai Hakan batareda saninsa ba ana kawo magani mara quality a asibitin Amma cikin ikon Allah Hakan Bai taba bawa Dr JAMAAL din matsalaba saima sake daukaka da suna da mutunci harma da girma dayake samu gurin mutane sbd tausayinsa duk da kwata kwata baida sakewa ko kadan sai a gurin patients dinsa wannan zakaga ya sake musu kyakkyawar fuskarsa me daukan ido sosai Amma badai ma’aikatansa ba harna asibiti harna sauran business dinsa.

Daga Baya Suma su Dad da sukaga asibitin sake qarawa SEELAHs girma da mutunci sosai takeyi tareda mutunci sai suka koma suna Jin dadin Hakan Amma dai a fili kawai cikin ransu Dad din Babu abinda yake so da burin kaman Jamaal ya aje komai kwata kwata ya shiga cikin huldansu ya riqe komai sbd dagashi har daddy lameenu kallan Jamaal sukeyi amatsayin sa’arsu Dan duk abinda ya Saka musu hannu Akai sai yayi musu yanda sukeso harma fiye Dan haka suka rasa yanda zasuyi su sakashi cikin huldansu na boye sunada tabbacin zasu samu harma abinda basutaba tinanin samu ba karshe ma dukiyar Omar Dake kashesu da ransu a duk numfashin dasuke shaqa tasu zaso tafi tasa su Dena wahalarda kansu duk da ciwon dukiyar Omar da rayuwarsa ma gaba Daya wani mummunan kurjin ciwo ne Da Babu ranarda zai fashe yabarsu saisun rufe kasa da idanuwansa.

Dr Jamaal Bai cika zama available sosai ba a Seelahs specialist da safe sai yamma Kokuma da daddare shine Asalin lokacinda kake samunsa a asibitin Dan yafi samun nutsuwa sosai acan da dare zai zagaya patients nasu sosai ya duba su tareda Basu kulawa sosai.

Su kuwa a bangaren su Dad Hakan shine daidai yayi musu
Da safe Yana tareda su a gurin aiki da yamma zuwa dare Yana asibitinsa sukuma ana gudanar musu da tasu huldar lokutan.

****Rayuwa tayiwa kowa yanda yake so sosai harma da qari dan kuwa lokaci yaja ayau sunkai JAMAAL SEELAH yana musu huldodinsu da duk sukeso batareda yasan da yawa ayyukan dayake musu na harkar banza bane sun taru sun rufesa duk da kulawansa sosai sun fisa kiyayewa sbd Bai taba tinanin wani abu Yana gudana a cikin familynsa ba da Bai saniba,

Sam Babu tsoro ko shakka ko rashin saa a lamarinsa saima izza da Kai tsayen da Babu acikin familyn kamansa,

Idan akwai abinda yafi farin ciki da Kwanciyar hankali tareda alfahari da Jin Babu kamansa to Dad Mam Yana ciki,ko sunan wani idan ba Jamaal ba bayason ana ambata a ‘dansa,

A duniya ko asirinsa Baya tsoron ya bayyana ga duniya kaman yanda shakkarsa Daya da tsoronsa Daya JAMAAL yasan su din su waye ne,
Me sukeyi a boye,
Ina suke zuwa,
Me suke hadawa da kuncewa uwa Uba abubuwan da sukai da rayukan da suka kawar ciki hadda na Dad Omar dinsa Daya kasa cire masa shi daga zuciyarsa kwata kwata duk kwata kwata haryanxu Babu Hulda tsakaninsu da Omar din.

Wannan kadai ne yake jijjiga zuciyarsu da tsoro da fargaba Amma bayan wannan ko Hukuma da duk wata sharia da masu yinta baima daukesu abin sakawa a lissafi ba Dan ya Dade da karbe wannan power din a hannunsa dukkanin wata hukuma da sharia sune suke juyata yanda sukeso su Saka a kawar musu da Wanda duk sukeso da sunan sharia.

Yanzu cigaba da karfin da suka sake samu akan barnarsu shine da sharia suke amfani a kawar Dana kawarwa a rufe na rufewa har karshen rayuwa,
Sun Dena Bata hannuwansu da jini Amma na Abinda Omar ya Haifa da Omar din shikam halastacce ne a gurinsu.

A bangaren Daddy lameenu ma kaman yanda Mam ke bugun gaba da alfahari da Jamaal haka yake wannan alfaharin dashi Dan kuwa manyanci ya Saka da yawa fiyeda Rabin nauyin dayake kansu Jamaal din ya dauke musu hakama Bai taba banbanta matsayi ko kaunar Dad dinsa akanshi ba sbd sanin shi din qanin mahaifinsa dayake kallo uwa Daya Uba dayane Dan haryanxu kaf familyn Babu Wanda haryanxu yasan ba uwa Daya Uba Daya SEELAHs suke ba.

Allah ya hore musu Jamaal din fiyeda yanda sukai tinanin samun ya dawo gurinsu dan haka Dr JAMAAL JEEY MAM SEELAH ya zama tamkar wani kofa ko bangon kariya da dukkanin ahalin seelahs Tako ina shi zaka fara tinkara idan zaka tinkari familynsa musamman iyayensa.

Haroon seelah tini ya zama kaman wani shadow a gidan baka cika jinsa ba idan ba mugun abinsu da Jamaal Bai saniba bane zasu yi to shine zaa nemosa.

Kauna da shakuwa dayake tsakanin twins din wani irin karfi gareta da Babu ranar da Dad Baya bawa Haroon tabbacin kada Koda wasa Jamaal yasan meye sirrin dayake gudana a cikin seelahs Dan hakan daidai yake da rabasu da zaiyi har abada,
Shi kansa Haroon tsoro da shakkar bari Jamaal Koda tsautsayi yasan wani abu ko fahimtar wani abu bare sanarda shi Dan gudu da shakkar fitintinu da tashin hankalin dazai iya biyowa Baya,
Shi kansa Yana shakkar Jamaal yasan cewa shi yasan komai Amma Bai sanar masa ba Dan haka Shima a cikin shakka da taka tsantsan din Jamaal yake.

****Yau a gida ya kwana sbd tafiyan dayayi wani aiki da suke Gina sabuwar kamfanin qera karfe na Seelahs a Nasarawa ba a cikin gari ba can wajen gari sosai kusada wani kauyen da Baya nesa da cikin Nasarawa din hakama kusan filin Gina kamfanin ya shiga garin sosai Dan haka kaman a garin ma zaa ce kamfanin take dan girmansa yaci kusan garin sosai.

Baccin ragewa jikinsa gajiya yayi na kusan awa uku bayan dawowan nasa kafin ya tashi sanyeda farar doguwar wandon TT me santsi ta kayan bacci.

Jikinsa Babu Riga daga doguwar wandon data zauna a qugunsa kaman zata sauka sai farar fatar jikinsa Dake glowing tana daukan ido hutun dayake cikin Yana bayyana.

Ba slippers a fafaren qafafunsa sbd saukowansa daga gado kenan Kai tsaye toilet ya nufa Kai tsaye ya Bude ya tareda zira takarmin toilet din marasa nauyi da dadin takawa ya zare doguwar wandonsa Yana nufar shower Kai tsaye Dan wankan yake buqata kafin komai.

Ya jima a cikin toilet din ba sosai ba kafin ya fito daure da towel ash daure a qugunsa kaman towel din zata Fadi sbd lazy daurin da yayi masa
qamshin shower gel na LE LABO SANTAL ne ke tashi jikinsa ahankali me sanyin dadin shaqa.

Ficewa yayi daga bedroom din nasa a yanda yake ya nufi hanyar dining room.

Fridge ya nufa Kai tsaye ya Bude ya dauko energy drink din E-Bull ya Bude yakai bakinsa yasha Yana juyowa yaji an Bude kofar palonsa Kai tsaye an shigo batareda ya waiwayoba yasan Haroon ne sbd shi kadai ne me shigowa bangarensa Kai tsaye batareda buqatan kira a waya Dan Jin Yana Nan ko Neman izinin shigowa.

Haroon Daya qaraso tsakiyar palon tareda nufo inda Jamaal din yake Kai tsaye
Yana kallan yanayinsa Haroon yayi ya Dan dauke Kai Yana Bude fridge din shima ya dauko drink din me sanyi kadan ya Bude yafara Sha Yana son sanar da Jamaal din son karban harkar sabuwar kamfanin nasu na Nasarawa.

MAMUH

DR JEEY SEELAH

BARR HAROON SEELAH

AMEENATOU BABBAH

THE SEELAHS

ROMANCE

ZAFIN KAI

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!

AMEENATOU
Mamuhgee

19
Haroon duk yanda yaso sanar da Jamaal kasawa yayi sbd shigarsa a aikin site din bazaiyiba tinda kwata kwata bayason aiki guri Daya da Jamaal inde na kulawa da harkokin Dad dinsu ne Dan tsoron bawa Jamaal daman fahimtar wani abin Koda tsautsayi ne Dan haka yauma hadiye zancensa yayi Yana dawowa Palo ya zauna a daya daga cikin lafiyayyun kujerun palon Yana cewa

“Amma yau din a gida zaka kwana tinda tafiya ka dawo ba buqatan zuwa asibitin ko?”

JEEY din baice komaiba Saida ya karasa shenye abinda yake hannunsa ya ajiye gwangwanin E-Bull din ya juyo Yana nufar hanyar bedroom dinsa Yana gyara towel dinsa kadan Daya kusa zubewa a qasa ya Bude Baki Yana cewa

“Inada patients Dake jiran dawowana na dubasu,
And inada ma da surgery da zanyi so meyasa zanyi kwanciyana a gida?
I can’t even sleep or have a rest if ba hospital din naje ba you know that”

Yana kaiwa Nan ya shige bedroom dinsa Dan shiryowa.

Bai wani jima sosai ba ya fito shirye cikin farar freesize Casablanca hoodie rigar data bayyanarda freshness dinsa sosai
sai half trousers fari Shima da slippers din Bally a kafarsa da haskenta da tsaftanta kaman ba akai yake tafiya ba.

Qamshin turaren Allure ne na Chanel ya gauraye palon gabaki Daya daga fitowarsa Wanda ya tabbatarwa da Haroon ya fito ya Dan dago nasa fararen idanuwan Shima ya kallesa Yana ajiye remote dayake hannunsa Yana sauya channel Yana duba time na agogon dayake daure a hannunsa yace

“Please kayi dinner damu mana to kafin ka tafi asibitin,Dad yayi tinanin zuwanka da Rana Kaci abinci tareda mu amma baka fito ba.”

Zama yayi kusa da Haroon din Yana kunna wayarsa da tinda ya shigo gida ya kasheta Dan samun hutun dayake buqata.

Zamansu guri Daya ne kadai wasu lokutan yake taimakawa kowa ganesu da tareda banbance waye Jamaal waye Haroon sbd fatarsu Daya Dan banbanta sai Kuma halayya da yanayi Amma suna rabewa basa guri Daya shikenan gane waye wannan waye wancan zaiyi matiqar yin wuya har Dad dinsu kuwa musamman idan zaiyi maganar Sirri da Haroon ya ringa kokarin tantancewa kenan kada yaje yayi da Jamaal ya lalata aikin shekara da shekaru.

Cikin sauti me nutsuwa da Kwanciyar hankali ya Bude Baki yace

“Idan na tsaya Kaine zaka kaini asibiti bazan driving ba ka yadda da Hakan?”

Murmushi me kyau da nutsuwa Haroon ya sake Yana gyada Kai da cewa

“Har bakin office ma kuwa zan kaika DR JAMAAL SEELAH.”

Murmushi Shima ya saki Yana kallan Haroon din Dake Dora masa da bayanin yanda Dad zaiji dadin Hakan Dan farin cikinsa a rayuwa ya zauna table cin abinci da gabaki Daya iyalinsa.

Kiran sallan magrib ya Saka Haroon miqewa ya nufi hanyar Daya bedroom din dayake palon na Jamaal Yana cewa

“Kayi magana da mum kuwa?takira dazu tana buqatan sanin yanda ka dawo wayanka is off.”

Shigewa yayi bedroom din batareda yaji amsan JAMAAL din ba,
Toilet ya nufa Kai tsaye yayo alwala ya fito suka fito tare zuwa masallacin gidan da suke sallah a ciki tareda su Dad da masu gadinsu da securities.

Tareda iyayensu sukai sallah suna gamawa sukayo ciki gaba Daya Banda Dad Lameenu daya fita tareda drivernsa zuwa wani gurin.

Dad cikin kulawa ya Kalli Jamaal Dake cika masa ido tamkar bashine ya haifesa ba ya tambayesa yanayin aikin Nasarawan Dan kuwa ba qananun dukiya zuka zubawa wannan aikin ba Wanda idan bakiyiba zasu tafka asarar da jijjigasu matiqa Dan haka Koda wasa bari kowa ya Saka hannu a aikinba sai Jamaal ne kadai project din da komai da komai yake hannunsa.

Cikin nutsuwa suke tattaunawa har suka Isa cikin main palon mansion din inda yake tsare da luxuries na Jin dadin rayuwa da asalin Hutu.

Hanyar dining room suka nufa dukkaninsu daidai fitowan mum Atey da itama Hutu da Jin dadin rayuwa yake bayyane a tattareda ita.

Tana ganin Jamaal ta washe Baki cikin kulawa tana cewa

“Dr jeey tin dazu nake cewa kana hutawa baka fitoba bare muyi Maka barka da dawowa”

Dan kallanta tayi a gazarce Yana Dan sake fuska kadan batareda murmushinsa ya bayyana ba ya amsa da

“Eh na gaji ne Koda na iso Ina buqatan ishashiyan Hutu,.thank you”

Fitowan Ayesha ‘yarta ne ya sakashi Dan daga girarsa Daya sama Yana Dan dauke kallansa daga gefen kwata kwata suna cigaba da magana da Dad akan abinda suke tattaunawa.

Gurin Haroon ta nufa tana sake fuskanta gaba Daya da farin cikin ganin Jamaal din tace

“Dr sannu da dawowa.”

Batareda ya waiwayoba yanda ya kamata ya Dan juyo kadan yace

“Yawwa thank you”

Zama tayi a kujeran kusa da Haroon tana gaida Dad Shima kafin ta dawo da kallanta kan Haroon tana magana kasa kasa kada kowa yaji me take fada masa Yana dariya fuskansa a sake sosai sbd akwai shaquwa da kulawa sosai a tsakaninsu.

Mum kuwa gefen Dad ta zauna sai ya zamana gefen Jamaal din shi kadai ne Daman Hakan shine raayinsa Dan haka take masu aiki suka qarasa kawo abubuwan da Babu a dining din su ruwa da drinks da cutlerys Dan Basu gama hada table ba masu gidan suka hau.

Mum Atee sosai takeson samun shiga kamar me gurin Jamaal sbd tini ta gama da kame Haroon ta koma itace uwarsa komai da ita yakeyi a matsayin uwa shi kuwa Dr ko a mafarki ba’a Haifa macen da zata maye gurbi ko samun matsayin mahaifiyarsa ba bayan mum dinsa itace kadai tak dinta Dan haka duk tsananin dagiya da son nuna masa tsananin kauna da kulawa da mum Atee keyi Bata taba samun shiga yanda takeso ba Amma dayake ta iya naci da kisisina Bata Dena nuna masa kulawa da tattalin ba saima sake dagewa datakeyi Dan tagama fahimtar Dr din shine SEELAHs ma gaba dayanta yanzu da zuwa Nan gaba hakama Dr ne kadai zata kama ta kama dahir a zaman seelahs harma ta taka matsayin shugaba a cikin matan zuriar duk da akwai wainda suka rigata dadewa a family harda manyan Yaya Amma dai nata burin daban ne akan nasu Dan ita ba zaman auren kadai tazo yiba hadda nemawa Kai suka da matsayi.

Cikin nutsuwa da wayewa sukecin abincin da sakewa dukkanin kulawan mum Atee akan Jamaal take tana tura masa abubuwan datasan Yana ci tana basa tabbacin sbd shi Akai girkin.

Sun jima sosai gurin cin abincin kafin suka gama suka baro dining din Kai tsaye Palo suka dawo suka zauna harsu mum din suka zauna suna magana tsakaninsu ita Dan Haroon da Ayesha shikuma Yana magana da Dad.

Anayin ishai suka fito Sallah suna gamawa Kai tsaye bangarensa ya nufa ya sauyo kansa daga guntaye zuwa dogon Riga da wando na Dior black ya fito Yana qamshi ahankali wayarsa kawai ce a hannunsa sai laptop.

Haroon already Yana harabar gidan Yana waya Dan haka Yana ganin fitowan Jamaal din ya Bude motar ya shiga Shima Yana isowa ya Bude ya shige suka fice harabar gidan securities da suka San Dr Jamaal din ba dawowa zeyiba a Daren suna masa a dawo da safe lafiya.

A hanyar ta zuwa tinda suka fito Jamaal ya kira mum dinsa ya Saka handsfree ya ajiye a tsakiyansu suna magana da ita su duka biyun cikin tsananin kaunar datake musu da wadda sukewa junansu Suma.

Suna Isa Haroon a harabar asibitin ya ajiyesa ya juya ya fice sbd ana jiransa wani guri.

Shi Kuma Kai tsaye ya wuce office dinsa duk inda ya wuce ana masa barka da zuwa cikin girmamawa da kulawa harya Isa office ya Bude ya shige.

Laptop din ya fara ajiyewa da wayarsa kafin ya rage AC kadan sbd tin kafin ya iso ake sake tsaftace office dinsa a kunna AC dasu humidifier.

Ajiye remote din yayi bayan ya rage AC Yana nufar files din dayake kan desk dinsa Bai taba ba ya nufi toilet ya wanko hannuwansa ya fito bayan ya goge hannun da towel fari qarami.

Sensitizers ya fara shafawa hannuwansa kafin ya nufi files din ya fara dubawa.

FADILA ALIYU MUHD shine sunan dayake kan file din.

Budewa yayi cikin nutsuwa Yana dubawa tareda karanta dukkanin bayanan dake ciki.

Dr zayyan ne ya shigo office din bayan yayi knocking Yana sanyeda kayan theatr da fitowansa kenan ganin Jamaal ya sakashi sakin ajiyan zuciya da numfashi me sanyi sbd suna tsananin buqatansa akan patient din da aka juye masa file nata.

MAMUH

DR JEEY SEELAH

BARR HAROON SEELAH

HASSAN AND HUSSAIN

AMEENTOU

FADILA

LOVE

ROMANCE

CRAZYINLOVE

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!

20
Dagowa yayi bayan ya gama sauraron bayanan Dr zayyan akan patient din Daya gama karanta severe long term asthma take fama dashi Wanda gabaki Daya rayuwarta da oxygen take rayuwa.

Idanuwansa ya dago yakai kan inda ake rubuta shekarun patient yaga shekarunta duka duka ashirin da Daya.

Dagowa yayi ya kalle Dr zayyan kafin yace komai nurse ta kwankwasa office din cikin sauri ya shigo ta sanar dasu ana buqatansu emergency ne yanzu yanzu fadilan taqi yadda a Saka mata oxygen dinta tayi nisa komai zai iya faruwa a daidai lokacin.

Dr jamaal dinne ya wuce gaba riqesa file din suka biyo bayansa cikin sauri.

Tin kafin ya iso nurse Farry na hangosa ta dauko masa hands gloves ta tarbesa da ita ya miqa mata file din hannunsa yana sakawa Yana karo sauri Dan isowa ga patient din da kusan ranta ma zaa iya cewa ya kusa fita Dan kuwa ta fizge oxygen nata gaba Daya gashi matsalanta pneumonia ne yafara mata mummunan kamu kafin asthma ya rikido.

Yana qarasawa da sauri yakai hannuwansa duka biyu ya Dora akan nata tareda dafeta Yana cewa ayi sauri a Saka mata oxygen din da gaggawa.

Dayake tayi nisa sosai Babu Bata lokaci aka mayar mata da oxygen din har lokacin Bai saketaba sbd Nisan datai ba lallai oxygen din ta shigeta da sauri ba Dan haka ya Bada umarnin ayi gaggawan kawo alluran da zai mata.
Gaba Daya sauri sukeyi Dan cetan rayuwarta musamman iyayenta dake kofar dakin suna kuka sosai Dan tini suka cire Rai daga gareta ganin yanda rayuwarta yake sama Yana qasa numfashinta na barin jikinta.

Addua suka hau cikin tashin hankali da fatan samun sauki da lafiyan Fadilan.

Sunyi tsananin laushi da zama abin tausayi akan ciwonta da lalurarta tsawon shekaru,
Duk abinda suka mallaka ya qare tas basuda komai bayan rayuwarsu sbd ciwon fadila,
Da oxygen take rayuwa koyaushe Yana tareda ita,
Mahaifiyarta da mahaifinta ita kadai garesu hakama tayi karatu sun inganta rayuwarta sedai ciwonta a yanzu da itama take ganin ta gaji sbd ta zamarwa iyayenta lalura,
Komai dasuka mallaka tana kallo ya qare duk sbd ciwonta dayake cin kudin da yanzu sun Dade da fin karfinsu dan haka take ganin kaman idan ta mutu zasu rage Shan azabar da sukesha sbd ita,

Mahaifinta yakai a yanzu ayyukan wahala yakeyi ya samo musu abinci Dana ciko cylinder oxygen dinta,
Takai ta kawo ma yanzu ba cinsu da shansu yake nemowa ba oxygen dinta yake yiwa nema a wahala da kunci tareda tsananin rashi suke rayuwa.

Kusan lokaci me tsayi likitoci suka sauka akanta kafin suka samo numfashinta ya dawo daidai duk da ba sosai oxygen din take kawai lungs dinta ba sbd mugun Nisan datai
Allah ne kadai yayi tanada kwana a gaba ma da tini wani zancen akeyi Amma dai ta samu oxygen din Kuma Daman nata Dan kadan ne ya rage dole Dr Jamaal ya Bada umarnin aka Saka mata sabo na asibitin tasu.

Rubuce rubuce yayi sosai a file nata tareda zuba mata fararen idanuwansa masu kyau Yana kallanta kafin ya dauke idanuwan nasa ya maidasu kan rubutun dayakeyi ya gama ya miqawa nurse din Dake gefensa suka fito Yana zare gloves din hannunsa Yana tattaunawa da sauran likitocin suka nufi wata patient dinsa Dayake ji da ita dattijuwa ce sosai tana fama da diabetes duk ya rikitata kaman me matsalan kwakwalwa ga tsufa Dan haka aketa fama da ita shikuma Yana lallabata sosai shiyasa idan ba shi ya Bata magani ba Bata sha sai anyi daqyar.

Round yayi a asibitin ya duba patients sosai har kusan 11 kafin ya juyo ya dawo dakin dasu fadila suke ya sake dubata yayiwa iyayenta tambayoyi sosai akan ciwonta Yana sake rubutu acikin file din kafin ya Basu tabbacin Inshallah zata tashi Amma ba yanzu ba zata iya kawai gobe da Rana ko Yamma ba Dan haka su kwantar da hankalinsu.

Sai 12 ya koma office dinsa yana shiga Kai tsaye toilet dinsa ya wuce ya wanke hannuwansa sosai tareda fuskansa ya sake shafo sensitizers ya fito ya rage hasken office din yazauna tareda janyo laptop dinsa ya Bude bayan ya dauko ruwa me sanyi kadan daga fridge dinsa ya Bude yasha kadan ya ajiye gefe yafara aikin dayake gabansa.

Washe gari bayan sallan asuba kaman yanda ya Saba Saida ya sake duba patients dinsa da yawa harda fadila kafin ya wuce gida.

Haroon Bai zo ba driver ne yazo ya daukesa sbd safe ne sosai.

Suna Isa gida Kai tsaye part dinsa ya nufa Yana shiga ya tube kayan jikinsa ya jefasu laundry room dinsa ya fito da underwear kawai ya jikinsa ya nufi bedroom dinsa.

Wayarsa kawai ya kashe ya jefar kan sofa ya nufi toilet ya shige
Wanke bakinsa kawai yayi da mouthwash na spray mint flavor batareda yin wani brush din ba Dan yayi a office
Yana gamawa wanka yayo ba jimawa sosai ya fito daure da towel cikin nutsuwa ya shirya a gaban mirror tsaye kafin ya saka underwears da kayan bacci marasa nauyi ko kadan ya haye gadonsa ya rufe jikinsa tareda kashe hasken dakin take bacci ya daukesa me dadi da nutsuwa.

Baccin awa biyu da rabi yayi kafin ya tashi ya sake brush ya shirya ya fito cikin ash Armani’s ya nufi cikin gida Kai tsaye palon Dad dinsa ya nufa acan suka gaisa ya fito daidai fitowan Haroon suka nufi dining room tare suna magana.

Breakfast sukai suna gamawa suka fito Kai tsaye motarsa Bentley continental gt ya nufa ya Bude ya shige tareda tayarwa Kai tsaye ya nufi gate securities suka Bude masa gate ya fice
Shima Haroon ko gate din baa rufeba ya Saka kan tasa tsadaddiyar motar ya fice zuwa nasa office din.

SEELAHs ya nufa office dinsa Wanda yanada ma meeting da baqi da safen su Dad ma duk zasu halarta sbd mahimmancin Taron meeting din.

Se karfi uku da Rabi ,hudu saura mintina kadan ma ya baro office Dan haka Yana dawowa sallah ya fara yi a masallaci kafin ya shige.

A dining na palonsa ake Kai masa lunch dinsa ana jere masa Dan haka abincin ya zauna yaci Yana gamawa sake kwantawa yayi bacci sai yamma ya tashi yayi wanka ko abincin Dare baici ba ya fice sbd hankalinsa Yana asibiti.

Yana Isa acan yayi sallan magrib Yana fitowa masallaci office dinsa ya dawo dan yanada patient da zai duba.

Sai bayan ishai yasha ice tea a office dinsa da cake kafin ya fito round nasa.

Fadila ce patient ta karshe Daya duba Kuma yayi mamakin ganinta zaune Amma gaba Daya Babu farin ciki ko kadan a tattareda ita,
Mahaifiyarta tayi kuka har idanuwanta basa dubuwa ga damuwa qarara a fuskanta,

Shi kansa mahaifinta Yana cikin tashin hankalin sallaman da zaa musu basuda kudin oxygen nata
Sunsan Babu oxygen Babu rayuwar yarsu ne Dan haka suke cikin mafi girman tashin hankali.

Da farko Dr Jamaal din ya dauka damuwan tashin hankalin jiyan ne Bai sake su Dan haka ya sake Basu qwarin gwiwan ta warware Inshallah.

Godia sukai masa suna sake maimaita farin cikinsu akan taimakon gaggawan Daya bawa fadilan jiya.

Fadila Dake zaune idanuwanta a rufe da oxygen dinta a hancinta Bata iya Bude idanuwanta ta kallesa ba sai qamshinsa Mai sanyi da dadi Daya cike iskan gurin gaba Daya Yana Sakata Jin jikinta na sake mutuwa gabaki Daya.

Shima a hankali ya juya ya Dan kalleta kafin ya dauke idanuwansa akanta Yana barin gurin.

Ranar ma a asibitin ya kwana sbd sunada emergencies sosai Dan haka Koda gari ya waye sosai yake a gajiye yabar asibitin.

Kwanansu fadila biyu a asibitin aka sallamesu batareda an cajesu komaiba sbd Dr Jamaal din Daya sanar da Hakan.

Daqyar baban fadilan ya samo kudin da sukai refilling Rabin cylinder na oxygen suka tafi.

Sati biyu sukai suka dawo asibitin da ita Rai hannun Allah Kuma sukai babbar sa’ar Dr Jamaal na asibitin Dan haka Shine ma ya amshi matsalarta tareda shiga damuwa sosai sbd ganin Halinda take ciki yafi na Baya muni.

Daqyar suka samu numfashinta ya dawo bayan sunsha wuya sosai Dan haka Kai tsaye ya tattauna da iyayenta sosai ya fahimci tsananin rayiwan da suke ciki da azaban da fadilan Kesha tin tana yarinya har zuwa yanzu datake ganin kaman ta zama musiba ga iyayenta.

Da kansu iyayen suka ringa masa Hawaye suna rokonsa ya fahimtar da ita suna tsananin Sonta ahakan Basu taba gajiyawa da ita ba bare kallanta a matsayin musiba.

Lamarin fadila da iyayenta tsaya masa yayi arai Dan haka Ya karbi file dinta gaba Daya ya mayar da ita patient dinsa da shi kadai ne yake dubata hakama ya dauke musu siyan oxygen nata shine me siya.

Ta Dade sosai wannan Karan kafin aka sallamesu Kuma duk wanna taimakon da dadewan da sukai asibiti Bata taba dagowa ta kallesa ba sedai ta riqe qamshinsa da kaf asibitin Babu me irinsa bayan shi kadai,

Shi kansa Bai taba tsayawa ya kare mata kallo Dan ba dabiansa bane qarewa mace kallo dan haka tsakaninsu gaisuwa da Godia ne kadai Amma umman da baban sun Saba ahankali ahankali Dan sosai Allah ya Saka musu kaunarsa da tsananin ganin girmansa Dan tinda suke wannan dawainiyar ta ‘yarsu Babu Wanda ya taba taimaka musu sai shi Dan haka suke tsananin kauna da ganin girmansa.

MAMUH

DR JAMAAL

AMEENATOU

HAROON SEELAH

FADILA

JEDEENDS

THE SEELAHS

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!

21
Acikin kankanin lokacinda bamai tsayi ba iyayen fadila suka zama tamkar wasu ahalin Daya hada jini dasu Dan kuwa sosai yake taimka musu bayan matsalan ciwon Fadila wadda a yanzu tafara Dan sakewa tana amsar rayuwarta da kaddararta sbd shi din Daya bayyanar mata da wata sabuwar rayuwar hakama tana ganin iyayenta cikin walwala sbd taimako da kulawansa sai kawai ahankali take kallansa da wani irin matsayi me girma.

Shi kansa Dr Jamaal idan akwai abinda Bai taba tinanin zai samu kansa a rayuwarsa kwata kwata ba to son wata ‘ya mace ne Amma Kuma ga dibbin mamakinsa sai gashi zuciyarsa Mai tsananin kamewa da kiyaye ko kallan mace ta kamu da wata tsaftatacciyar son fadila Mai tsananin gaske da Bai taba tinanin samun kansa a wannan fannin ba.

Son dayake mata ya ginu ne daga tausayi me tsanani tare Kuma da nutsuwanta da yanda ita gaba Daya Bata taba abokiya ba bare sakewa da mutane sbd tana kallan kanta a matsayin matacciyar data ke yawo da kararrin kwana,

Bata taba sakewa tayi muamala da mutane ba koyaushe a kadaice take sbd halinda rayuwarta ke ciki na koina da oxygen take yawo maqale a hancinta Babu abinda batareda shi oxygen dinnan takeyiba Dan haka rayuwarta take tsit Babu kowa a cikinta face iyayenta,

Hakan ne shikuma yayi masa sbd macen da batada hayaniya ko tashin hankali ko Daya itace macen dayakeda raayi wadda bazasu samu hayaniya ko damuwan zama ba,
fadila ta samu shiga zuciyarsa ne sbd wainnan halayen nata hakama ba qaramin so me girma da tsafta zuciyarsa ta kamu dashi Dan hka Kai tsaye ya sanar da iyayenta da sukaji kaman zasu shide Dan tsaban farin ciki da basa fadilan da dukkanin Saka albarkansu.

Fadilan da farko duk da sanin nesa nesa sosai yayi mata zarra yafi karfin ajinta dari bisa dari Amma kasa amincewa tayi da Hakan sbd tasan tausayi ne yake mata tsagwaronsa Amma ahankali ahankali tsarinsa da kalan tasa kulawan ya Sakata mutuwa gabaki Daya akansa batareda tasan da Hakan ba sai jinta tayi cikin sonsa sosai fiyeda yanda ma shi ya samu kansa.


Haroon ne Kai tsaye Wanda yasan JEEY din yasamu irin macen dayake so duk da yayi tsananin mamaki me girman gaske dayaga fadilan black beauty da ita me tsari da nutsuwa Amma Kuma a yanda yasan JEEY yasan tsari da rayuwarsa ba lallai fadilan itace macen da raayi da rayuwarsa ke buqata ba sbd fadilan tayi sanyi da nutsuwa da yawa Wanda shi Kuma nasa nutsuwan da rayuwar rashin son hayaniya yafi na fadilan Dan haka rayuwarsu taruwa zatai ta mutu ba dadi ko annashuwa acikinta Dan haka yakega kaman rayuwar JEEY da mace me yar hayaniya da son Nishadi ya kamata sbd ta kawo annashuwa rayuwarsa.
Amma tinda Dr Jamaal Seelah guda ya Riga ya bawa fadila zuciyarsa babu abinda zaiyi bayan Shima ya kaunace sosai tareda girmama raayi da zabin Rabin jikinsa.

Alaqar Dr Jamaal da fadila yayi nisa sosai Wanda ahankali ahankali ya dawo da ita mace Mai farin ciki da annashuwa da walwala ba kaman yanda rayuwanta yake a Bayaba a tauye cikin qunci,
Shi kansa yana mamakin yanda yake tsananin son fadila wadda ta wani bangaren sai kawai Sonta ya fara sauyashi zuwa ga Maison qara zurfafa iliminsa na Addini Dan babanta malamin Addini ne Dan haka sai kawai ya sake zama busy Sam baida time na zaman gida ko zaman Shan iska da fita dasu Dad kaman yanda suka Saba duk weekend shi da Dad dinsa da Dad Lameenu da Haroon harma da matan family din wasu lokutan.

Idan yaje office da safe duk abinda yake gabansa ajesa yakeyi idan 2 tayi ya baro ya dawo gida ya shirya ya wuce karatun dasuke dauka shi da baban fadilan a wani course dayayi musu Register Mai tsada na karatun Addinin basa fitowa sai gap da magrib suna fitowa abinci da wanka kawai yakeyi ya wuce asibiti ya kwana acan wani lokacin Kuma ya dawo gida.

Baban fadilan ayanzu ya zama kaman mahaifinsa sosai suka samu shaquwa hakama ummanta wadda itace mace ta farko data samu matsayin uwa a gurinsa bayan Mum dinsa.

Ahankali ahankali harkokinsu Dad suka fara tabuwa da wannan sauyin da aka samu daga JAMAAL din Dan kuwa aikin site ma tini ya fara kokarin damqawa Haroon komai sai gashi baaje koina ba suka fara samun matsaloli abubuwa na tabuwa.

Babban abinda yake Kara dagawa su Dad hankali da sauyin shine faduwan dasuka farayi hakama yanda Jamaal din ke sake zurfafa a harkar Addini sai sukejin tsoron tayaya zai fara dasu idan yaji rai ta Dan Adam su baa bakin komai take a hannunsu ba
take sukaji kwata kwata aurensa dama yarinyar da iyayenta Bai kwanta musu ba musamman Dad Jin yayi yayiwa yarinyar da mahaifinta mummunan tsana hardai yanda yake bayyane so Mai tsananin gaske yakeyiwa yarinyar.

Dad Lameenu yafi Dad daga hankalinsa Dan kuwa bincike ya tabbata musu da mahaifin yarinyar yagama mallake zuciyar JAMAAL Dan haka komai lalace musu ma zeyi Idan Jamaal ya auri yarinyar,
Gata ba lafiyayya ba.

Duk yanda suka daga hankalinsu a boye da tsanar auren dayake son aje a nema masa baisani ba Dan Basu taba nuna masa shiyasa haka yakejin ma auren yake buqatan ayi kawai dan fadila ta dawo cikakkiya a rayuwarsa da kulawansa Dan ganin yakeyi koyaushe zaa iya samun matsalan oxygen nata wani abu ya sameta idan Bata tareda dashi.

Sosai yake sake samun sabbin akidu da ilimin Addini sosai Dan haka duk da Baya samun time na aikin dukiyarsu sosai Amma dai yanzu Yana tsananta taka tsantsan da bincike Dan Hana Haram shigowa cikin tsaftacciyar dukiyarsu.

Baban fadilan da kansa yake Kara masa karfin gwiwan tsananta bincike Dan kaucewa Haram.

Wannan shine babban kuskuren dayayi batareda yasaniba shi baban fadilan Dan kuwa shigar da zargi da tsananta binciken dayake Saka Jamaal yi tsakaninsa da iyayensa Dan dukiyarsu tini yakai maqura gurin tsananta batawa su Dad Rai.

Dan haka Kai tsaye Dad yace Jamaal bazai auri fadila ba Bai amince ba kwata kwata.

Mamaki ne ya kama Jamaal sbd baiga illan fadila Dan haka Shima yace baiga matan da a duniyar Nan zai iya nawa matsayin matarsa ba idan fadila.

Kafewa Dad yayi Shima akan wallahi tallahi Jamaal bazai auri fadilan ba.

Tin lamarin na kaman wasa sai gashi ya zama babba Dan kuwa maganar fasuwan auren Neman tabbata yakeyi Dan Mam Kai tsaye ya kira Dr Aleena Dan yasan ita kadaice duniya zata iya Hana Jamaal auren yarinyar ya hanu.

Dr Aleena kwata kwata batason Jamaal din Yana samun yawan sabani da Dad dinsa kaman Baya shiyasa ma Daya matsa ita ta hakura tabar Jamaal din ya dawo gurinsa Dan gudun abinda zaije ya dawo Dan idan Mam ya rasa abu yafison kowa ya rasa Dan haka ita tsananin son datake wa danta ta hakura ta gansa daga nesa yafi mata ace Baya duniyar gabaki Daya.

Maganar aurenma Yana gama magana da ita ta kira Jamaal din ta rarrashesa akan ya janye daga maganar fadilan ya sauya wata idan tausayinta yakeyi kobai aureba zai taimakawa rayuwarta.

Shiru yayi Bayan ya gama sauraron bayanan Mum din ya sauke numfashi mata sauti Dan yanajin fadan ya rabu da fadila wani abu ne har abada bazai iya ba,
Su tinaninsu tausayinta kadai yakeyi?
Basusan wane irin karfin son dayake mata da zai iya rabuwa da Dad ya aure su koma gurin mum dinsa suyi rayuwa acan.

Maganarta ta Saka hankalin mum din tashi Dan kuwa tasan fitina ce kwance zaiyi da Dad dinsa akan auren Duk da tana son fadilan itama sosai da ‘dan nata sbd ganin irin zurfi da kakkaifan son dayake mata da batama dauka Jamaal Seelah zai taba son mace a kusa ba harma Mai karfi irin Hakan.

Koda ta sanar da Dad din Jamaal ya dage kan yanason yarinyar ransa mummunan sake Baci yayi Dan haka ya fuskacesa da kansa yayi masa fada sosai
Shi kansa Dad Lameenu Kai tsaye yace Bai aminta da aurenba.

Haroon da mum Atee ne suka ringa son lallabata Jamaal su fahimtar dashi ya hakura tinda mahaifinsa Baya son yarinyar
ga tarin mamakinsu daga karshe Jamaal zabar komawa yayi gurin mum dinsa.

Haroon rintse idanuwansa yayi cikin sabuwar damuwa Dan daman abinda yasan zai iya faruwa ne Kuma yaketa gudun ya faru din.

Mum Atee kanta sosai ta shiga fargaba ta ringa binsa da lallashi da son fahimtar dashi rashin kamatan Hakan Amma gaba Daya yaji zai iya aje komai na Seelahs ya koma Dr Jamaal din mahaifiyarsa ita data amshi fadilansa hannu bibbiyu.

Wannan shine mafi bacin Rai da tashin hankalin da Dad dinsa ya shiga ganin kawai Rana tsaka Jamaal ya zabi mace fiyeda su,
Kuma macen ma nakasashiya da zata Bata musu aiki da yawa tareda sauya musu Jamaal din gaba Daya Dan kuwa tin yanzu ya sauya fiyeda kashi 70 akanta ana auren Jamaal zai janye daga tarin companies dinsu da nauyin seelahs gaba Daya dayake kansa ya koma likita kawai Kuma me tattalinta shikenan su komai nasu ya rushe a banza bayan tin kafin ayi auren uwarta ma suka hada jini da majina da gumi suka hada dukiyar.

Dad Lameenu Daya tsani tsayawa lamari na basa ciwon Kai batareda ankai karshen matsalar ba ayita ta wuce Jin yayi zai iya komai akan Hana Jamaal tafiya yabarsu hakama bazai iya barin ayi auren ba tinda auren Jamaal din kaman downfall dinsu ne abubuwa da yawa zasu biyo Baya,
Na farko saisun wayi gari Jamaal ya tattara komai ya ajiye ya koma asalin Dr dinsa kawai,
Na biyu mahaifin yarinyar Daketa son dorasa akan wata turban dazai haddasa babbar fitina a tsakaninsu da babu Wanda yasan ma Ina zata tsaya,
Na uku auren Nan rabasu da Jamaal zaiyi kwata kwata zai koma kaman mahaifinsa fadilan shine mahaifinsa hakama yanda yakeson yarinyar Babu abinda zai hanasa tattara kulawansa akanta.

To duka idan Hakan ta faru su meye matsayi Dan makomarsu?.

MAMUH

DR JEEY

AMEENATOU BABBAH

HAROON SEELAH

THE SEELAHS

LIFE

HOTLOVE

TOOHOT

ROMANCE

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!

22
Fadila da tinda aka fara wannan tashin hankalin ta shiga nata tashin hankalin Mai tsananin gaske da damuwa tareda janyewa daga kowa Dan kuwa tasan bama zata taba samun Jamaal ba yaudaran kanta takeyi data bari ta jefa kanta a duniyar da Bai kamata ace ta jefa kanta ba.

Ummanta da baban damuwa suka shiga Suma gashi damuwan yafara tabata yau lafiya gobe ciwo harta Kai oxygen ma wasu lokutan da dama tana zarewa kanta batareda saninsu ba saidai su sameta tana kokarin rasa rayuwarta suyi gaggawan Kiran Dr Jamaal din Wanda Shima tini kansa ya fara daukan caji Dan kuwa sosai take kokarin rasa rayuwanta a lokuta da dama idan Hakan ta faru.

Zafi sosai kansa ya dauka kaman yanda iyayenta Suma kansu ya dauki zafi daga karshe batareda sanin Jamaal din ba baba yaje har office din Alh Lameenu seelah yayi magana dashi bayan dogon jiran Daya Sha da bin dokoki sbd baida appointment dashi.

Bayani da nasihu yayi masa akan su hakura subar yaran suyi aure tinda suna son juna Kuma ya sake Basu tabbacin yarsa batada wata tarbiya mata kyau ko halayen da zasu sakasu Jin Dana sanin barin dansu ya aureta ciwonta Kuma kaddara ce da Allah yafi kowa sanin dalilinsa na yinta a Hakan.

Harya gama bayaninsa da nasihunsa Harma da waazinsa Dad Lameenu baice komaiba sai daga karshe yayi masa Godia fuska a sake Yana nuna ya gamsu da bayaninsa Kuma insha zasu tattauna da Dan uwansa zasu taho da jamaarsu maganar neman auren.

Bayan tafiyar baban numfashi Dad Lameenun ya sauke Yana Jin gwara su bari ayi auren idan har sunason riqe Jamaal a hannunsu batareda ya barsu ba.

Da daddare suna tareda Mam a office dinsu na gida yayi masa bayanin komai Wanda kusan Shima Mam din shawarar Daya Yanke kenan ganin Jamaal din yafara Shirin barin kasar da gaske barinsu zeyi Wanda yafison ya rasa wani bangare na dukiyarsa me yawa Daya rasa Jamaal a bangarensa.

Ranarda Jamaal yagama samarwa fadila Visa auren kawai za’a daura musu ya tafi da ita Dad dinsa akan dining gurin cin abinci ya sanar dashi ya amince da auren idan har zai zauna dashi bazai barsa ba har abada sedai mutuwa.

Wani sanyi ne ya fara cike zuciyar Haroon kafin mum Atee data sakin hamdalan farin ciki hakama Ayesha data shiga damuwan tafiyarsa.

Shikuwa dagowa yayi ya zubawa Dad din fararen idanuwansa batareda yayi masa alkawarin dayace yayi masa dinba Dan kuwa baiyi alkawarin barin mahaifiyarsa har abada ba haka Kuma idan ya daukota daga qasarta ya dawo da ita kusa dashi baiyi mata adalciba shiyasa Bai taba gwada cewa zai dawo da ita kusa dashi ba kwata kwata duk yasan idan yace ta dawo kusa dashi din zata dawo Amma dai bayason yi mata Hakan Dan qasarta itace Kwanciyar hankalinta da nutsuwanta.

Murmushin yaqe Dad din ke sakewa na yake Yana nunawa Jamaal din ya amsa fadilan dari bisa dari.

Numfashi Jamaal din ya sauke Yana Dan lumshe idanuwansa tareda Jin wani nauyi dayake kirjinsa ya sauka Dan kuwa Koda ya tafin zuciyarsa bazata taba samun wannan nauyin ya sauka ba tinda bawai baya kaunar mahaifinsa bane Yana tsananin kaunarsa fiyeda tinani kawai dai shi ya iya boye Abu ne dakuma yawan samun sabanin raayin dayake samu da Dad din ba kaman Haroon ba da duk abinda Dad yafada masa yayi me kyau da mara kyau to ya zauna.

Cikin farin ciki me tsanani da Jin dadi Haroon yayiwa Dad din Godia Yana bayyanarda Jin dadinsa ga sulhun da aka samu tsakanin Dad da Jamaal din Dan idan Jamaal ya tafi ya barsa baisan wace rayuwar zai fuskantaba a gurin Dad din idan Jamaal Baya nan hakama yasan bazai taba iya musu ayyukan nasarorin da Jamaal yake musu ba musamman bangaren manyan harkoki da baida sani ko kadan akansu.

Jamaal ma Jin yayi tausayin Dad din nasa ya shigesa sbd ya amince ne da auren yasani Badan har dari bisa dari din Daya fada ba Yanason auren sedan Yana tsananin sonsa fiyeda nasa farin cikin bayason rabuwa dashi.

Godia yayiwa Dad din cikin nutsuwa da kulawa tareda bayyanar masa da kaunar da Dad din ke tsananin son Gani daga garesa.

Hakan da yayi ba qaramin Saka Dad din farin ciki me girma yayi ba Wanda harya bawa Haroon tausayi sbd idan akwai abinda Allah ya jarabta Dad din dashi shine Jamaal da kaunarsa.
Ko Alh Lameenu lokuta da yawa shi kansa Yana tsoro da shakkar yanda Mam ke tsananin son Jamaal Dan haka yake gudun kada Hakan ya zama raunin Mam su samu matsala sosai me girma tinda Jamaal din kwata kwata ba page Daya suke dashi ba akan abinda suke aikatawa Dan ma Allah ya rufa musu asiri ba shine lawyer ba Haroon ne da kashinsu ya Dade da bushewa duk power dasuke riqe da ita suna juya sharia yanda suke so da sai Jamaal ya tabbatarda sun rasa komai.

A Daren ranar firan da suka jima a tsakaninsu basuyiba Saida sukai shida Dad ciki kulawa da kauna har tsawon dare kafin ya fito ya wuce part dinsa tareda Haroon da Shima ranar kaunar Yan biyunsa ta motsa a part din zai kwana.

Bedroom dinsa ya wuce Kai tsaye ya fada wanka zuciyarsa na samun nutsuwan dayake buqata wadda ya rasa a kwanakin sbd rigimansa da Dad.

Haroon ma Dayan dakin ya nufa wankan yayi ya fito Kai tsaye ya nufi bedroom din Jamaal ya Bude closet dinsa ya dauko kayan bacci black ya Saka ya fito yaje kwanta,sai a lokacin Jamaal din ya fito ya shirya cikin fararen kayan bacci ya kwanta tareda dauko wayarsa Yana Kiran fadila a natse.

***Amincewan Dad shine babban abinda yayiwa kowa dadi da farin ciki har bangaren su fadilan wadda batada wani qwari ko kuzari Amma tayi murna sosai.

Babu Bata lokaci Jamaal ya buqaci ayi auren Dan kuwa a yanda yake sane da ciwonta yayi tsanani sosai Dan kuwa yanzu lungs dinta sunyi Nisa sosai oxygen ma Neman gagara riqesu yakeyi Dan haka yake buqatan auren zai fita da ita yaga wasu likitocin da zasu duba case dinta sosai tareda shi.

Bai sanarwa kowa ba har iyayenta matsalanta yayi muni sedai daga su har fadilan jikinsu yayi sanyi sosai Dan sosai kullum take sake zama weak numfashin ma ahankali ahankali take iya shaqarsa.

Hakanan suke lallabawa Dan asamu ayi bikin,

Fadila da kanta ta cire Rai daga rayuwa a yanzu Amma dai babban fata da burinta shine ta samu zama matar Jamaal kafin Allah ya dauki ranta,
Tanason cika masa burinsa na son ganinta a matsayin matarsa mallakinta kafin ta koma ga Allah Dan haka take fata Dan rokon Allah ya Bata qwari da qarin kwanakin da zata cika masa wannan burin.

Su kansu iyayenta duk yanda jikinsu yayi sanyi ga yanayinta a yanzu ta Basu qwarin gwiwan karban kaddararsu,
Suma a yanzu fatansu ta zama matar Jamaal kafin Allah ya dauki ranta
Idan hakan ta faru zasuyi farin ciki ko bayan ranta sbd burinta ya cika Kuma Jamaal ya zama sirikinsu baiyi musu wahalar banza a banza ba.

Jamaal kwanakin auren na sake kusantowa Amma kwata kwata kansa ya dauki zafi baida lokacin komai bayan tattaunawa da Neman yanda zaiyi ya kawowa fadilan sauki ta samu shakar numfashi me dadi da nutsuwa Dan lamarin yafara karya masa zuciya Amma Koda zaiyi yawon duniya da kasashe ne zai Nemo mata lafiya idan har Allah yayi zata warke din.

Kwanaki na sake kusantowa na auren fadila na sake zama weak sosai Dan yanzu gaba Daya tayi fayau kaman Babu jini a jikinta hakama sai qanqancewa takeyi tana rama da komawa karama.

A daidai wannan Gabar iyayenta sunyi kuka harsun godewa Allah sbd tinda take fama da ciwon tsawon shekaru Bata taba komawa Hakan ba sai yanzu gashi ita kanta wannan Karan ta fidda Rai daga rayuwa adaidai lokacinda taso ace ta rayu Dan bawa Jamaal farin ciki.

A rayuwar seelahs Babu Wanda ya taba tinanin zaa samu Jamaal a hali na fita hayyaci sbd kwallafa Rai a Abu sai yanzu.

Duk yanda su Dad suka dauki matsayi da girman yarinyar a zuciyarsa abin ya wuce Nan Dan haka hankalinsu yasake mummunan tashi akan lamarin auren.

Gaba Daya Jamaal ya aje komai ya tattara hankalinsa gaba Daya akan Neman mafitan ciwon fadila,
Kai tsaye ya ajiye komai har aikin asibiti sbd gaba Daya ta koma a kwance take rayuwa a kwanakin ga oxygen din kwata kwata kaman ya Dena mata aiko Dan haka take ya fasa jiran sauran kwanakin auren yace a daura kawai zai fita da ita waje mum dinsa ma tana Jira zasu taru da wasu likitocin su duba matsalanta Daya kasa Ganowa.

Babu Wanda yayi musu da maganar auren nasa dayace a matso dashi Dan Babu wani biki ko hidiman ma da zaayi tinda amaryan a kwance take tana Neman numfashinda zata shaqa ma ta rayu.

Haroon baitaba sani ko ganin haka asalin so yake ba sai akan Dan uwansa Wanda Bai taba Ganin abinda Jamaal yaso fiyeda komai ba bayan iyayensa dashi sai Fadila,

So ne me tsafta da karfin gaske da Allah ya jarabcesa dashi na yarinyarda ba lallai ta rayu ba Dan koshi da ba likita ba baiga alaman tashi ga fadila ba sedai kwata kwata Jamaal ya kasa yarda da fadilan bazata warke ba ta tashi ta basa ‘yan biyun datai alkawarin basa Shima yayi alkawarin ita kadai ce zata zama uwar yayansa,
Ita kadai ce macen dayake son ta Haifa masa wasu Jamaal and Haroon Kokuma Mamman da Omar.

Tausayinsa sosai Haroon yakeyi tin yanzu Daya kasa gane komai ya jinginar da rayuwansa kwata kwata akan fadila da iyayenta da suka koma sune masu basa hakuri da qwarin gwiwa.

MAMUH

SEELAHS

AMEENATOU BABBAH

LOVE

HOTLOVE

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!

23
Mum dinsa ya buqaci zuwanta a kasar sbd ta tayasa duba yanayin na fadila dayake tsananin basa faduwan gaban da Bai taba samun kansa da tsoron wani abu ba sai yanzu Dan kuwa ko chances na surviving nata yaqi yadda ya duba sbd Bayason Jin ko kalaman rasawa.

Duk wani ayyuka Dake gaban Dr Aleena ajiyesu tayi tayi shirin zuwa Nigeria cikin damuwa sbd Jamaal da gaske ya Saka damuwan da tsoron matsalan fadila sosai.

A daidai gaban dayake yanzu shine ko dubata Baya iya yi da kansa saidai sauran likitoci su dubata.
Da kanta take kokarin bawa kanta kuzari da karfin hali Dan basa nutsuwan cewa tana samu sauki duk da Babu saukin datake samun saima tsananta da abin yakeyi.

Ranar da mum dinsa ta sauka Nigeria
Tareda Haroon sukaje daukota airport.

Kyakkyawar baturiyar da bazaka taba cewan itace ta haifi manyan zaratan matasan Dake tsaye suna jifanta da kallan tsananin kauna da kewa musamman jamaal da ganinta gabansa ya Saka dukkanin rauninsa Daya kasa bayyana gaban kowa bayyana a gaban mahaifiyarsa.

Itama kallansa tayi tareda zuba masa idanuwanta masu haske irin nasu tana kallansa zuciyarta na karyewa da tausayin abinda take hangowa acikin idanuwansa.

Hannuwanta ta ware daidai lokacinda ya ranqwafo yayi mata kyakkyawar runguma Yana lumshe fararen idanuwansa dasuka Dan sauya Yana Jin nauyin Dake zuciyarsa Yana rabuwa sbd ganinta
itama rungumarsa tayi dakyau tana Jin inama zata iya cire ciwon fadilan ta dawo dashi kanta Dan kawai bawa Jamaal din farin cikinsa.

Sun jima ahakan tana fada masa magana me sanyi cikin kunnuwansa tana shafa bayan kansa kafin suka saki juna ya riqe hannunta Daya Yana Jin nutsuwan Daya rasa tsawon lokaci na shigarsa kadan kadan.

Rungume Haroon tayi tana Jin kaman zata hadiyesa Shima kafin suka juya zuwa mota hannunta na cikin na Jamaal Wanda ke sanye da guntun wandon Dior da rigarsa ash sai fcap da sunglasses fuskansa Babu wani walwala sosai sai daukan ido yakeyi acikin Rana shida mum dinsa harma da Haroon da baiyi haskensu ba.

Mota suka shiga Kai tsaye Haroon ne me tuqin mum na Baya sai Jamaal din a gaba.

Kai tsaye gidansu fadila mum ya buqaci a fara zuwa tafara dubata tinda shine abinda ya kawota kasar.

Suna Isa kofar gidan babanta na waje tareda siddeeq ‘dan kanwarsa data jima da rasuwa itama Yana karatu a Lagos din a hostel yake zama Amma tinda ciwon fadila yayi tsanani ya dawo gidan dole sbd baban yakai baida cikakkiyar lafiya Shima sbd zuciyarsa Dake kasa daukan rashin yarsa duk ya Tina da Hakan.

Suna ganin motar Seelahs suka San Jamaal ne.

Haroon ne yafara fitowa Dan haka suka tinkarosa siddeeq na masa barka da zuwa Saida Jamaal din ya Bude dayar kofar ya fito suka gane ba shine suka tinkara ba Haroon ne Dan haka suka juyo suka dawo bangarensa suna masa barka da zuwa.

Cikin girmamawa ya gaida baba Yana tambayar siddeeq exams dinsa Daya gama a jiya.

Fitowan Dr Aleena ne ya Saka baba da siddeeq kallanta suna tabbatarda itace mahaifiyar su Jamaal din sbd kamannin da suka hada Dan haka cikin mutuntawa da girmamawa sosai suka gaidata suna mata sannu da zuwa cikin turanci.

Amsawa tayi itama a mutunce kafin sukai cikin gida gabaki dayansu.

Umma ma tarban mutunci da girmamawa taiwa mum din da Haroon duk da Shima ya zama kaman na gida yanda Jamaal yakoma Kai tsaye Dan gidan baida shamaki da koina da komai.

Dakin fadila suka nufa tana zaune a jingine da gado an mata kariya da pillows masu taushi idanuwanta a rufe tana Jan wani kasalallen wahalallen numfashin dayake shiga lungs dinta daqyar.

Kallo Daya mum tayi mata ta juyo cikin sanyin jiki ta Kalli Jamaal Wanda yanayinta yake karanta Dan ko a Poland tana cikin manyan likitocin da ake alfahari dasu manya.

Qarasawa tayi har inda fadilan ke zaune ta Bude idanuwanta ahankali da Jin qamshinsa da shi kadai ne yake Ankarar da ita da zuwansa.

Akan mum ta sauke idanuwanta dasukai ciki sosai Bata iya budesu duka sosai sbd rashin karfi sosai.

Durqusawa mum tayi gabanta tana mata sannu cikin tsananin kulawa da nutsuwa kafin ta Kai hannuwanta biyu ta kamo hannun fadilan Daya tana gyara zamanta gefenta cikin sanyi ta tambayeta Yaya jikin.

Cikin nutsuwa da sanyin murya me tsananin taushi ta amsa tareda yi mata sannu da zuwa sbd karfin hali.

Tsit dakin yayi kowannensu na tsaye daga waje daga Jamaal din Se mum ne kadai a dakin tafara dubata tana Jin shakkar abinda tafara tinanin matsalan take.

Kallansa tayi lokacinda ta zare oxygen din hancin fadilan takai hancinta tana shaqa kadan tana Dan rufe idanuwanta Dan shaqarsa cikin relaxing komai nata.

Numfashin fadilan ne yafara sama sama Dan haka ta mayar mata dashi ahankali tareda sake kamo hannunta tana Jin pulse nata.

Cikin abinda Bai gaza mintina arbain na zuwa hamshin ta kusan gama karance matsalan fadilan ta gangan jikinta.

Kallan Jamaal tayi Wanda gaba Daya ya tashi daga likita a lokacin ya koma kaman me jiran sakamako.

Numfashi ta sauke tareda miqewa tsaye ta dawo gefensa ta tsaya a natse tace

“Ina buqatan ganin file nata yanzu a fito dashi daga asibiti a kawomin”

Kallan fadilan yayi tareda kamo hannunta Daya acikin nasa yayi mata sannu kafin ya Kalli mum cikin Dan sassauta murya Yana baro gurin fadilan yace

“Mum asibitin zaa tafi da ita yanzu ai sbd acan ne zatafi samun cikakkiyar time da kulawa da duk abinda ma zamuyi…”

Kallan fadilan itama mum tayi cikin sanyi da tausayi kafin ta dawo da kallanta kansa tace

“Abarta a gida zan dubata anan tareda duk abinda nakeson tantancewa sbd Ina tinanin koma Menene matsalan daga oxygen data shaqa ne yayiwa lungs nata mummunan illa a yanda na karanci numfashinta da kyau da yanda kirjinta yake amsa zuwa lungs din but Ina buqatan sabon oxygen akawo daga wani gurin daban bana asibitinku ba.”

Manyan idanuwansa da suka mum din kallansa tana Jin sanyin jiki ya zuba mata Yana Jin gefen kansa na sarawa sbd tinanin oxygen nata nada matsala shine abinda Bai taba shigowa kansa da bincikensu ba sbd daga asibitinsu ake Bata shi Dan haka ma ne Bai taba tinanin Koda bugun iska wai zaa samu matsala a oxygen din datake shaqa ba,.

Hakan ne ya hanasa Gano asalin matsalan Dena shigarda da numfashi keyi dakyau kenan duk qwarewansa a aikinsa ko me??

Jin yayi kansa na Neman daukan zafi Dan haka mum tayi saurin fahimtar dashi tana tinani ne kawai Amma suna buqatan wani oxygen din kafin su tabbatarda Hakan ne.

Fitowa dukai dukkaninsu shine a gaba mum din na Baya Basu sanar da kowa komai ba Sukai musu sallaman zasu dawo anjima suka fito.

A mota shiru yayi yaja sauraron bayanan Mum datake qara Bude masa komai sbd itace take gabansa sosai a kwarewa da sanin aikinta.

Haroon ma kasa yadda yayi da zaa iya samun matsala a cikin oxygen din Daya fito daga asibitinsu sbd wannan babban laifi ne ake magana Wanda zai Saka a dole license na asibitin gaba Daya a rufeta Kuma hakanma zai iya taba aikin likitocinsu da yawa harma dashi Jamaal din.

Shiru Jamaal yayi Bai iya cewa komai sbd Jin zuciyarsa na tarwatsewa idan har ya tabbata akwai abinda yake cikin oxygen din fadila yayiwa lungs nata mummunan illar da Babu gyara bazai taba yafewa kansa ba akan sakacinsa.

Suna Isa gida Kai tsaye hanyar bangarensa sukai parking ya fito da kansa ya budewa mum din mota ya kama hannunta ta fito
Haroon kuwa kayanta ta fiddo dasu daga bayan motar suka nufi kofar palonsa.

Kai tsaye har bedroom din dayake part dinsa Daya yakaita Haroon ma ya shigo da kayanta yana sake juyawa zancen fadila a ransa tareda tsoron halinda Jamaal zai shiga idan Hakan ta tabbata,
Yana tsananin son Dan uwansa fiyeda komai da kowa a duniyarsa Dan haka bayason damuwa ko bacin Rai Bare tashin hankalinsa Dan haka duk ya rasa sukuni.

Key din motarsa ya dauka ya fice Kai tsaye asibitinsu ya nufa ya buqaci oxygen daban da sunan wani patient din zaa sakawa hakama ya buqaci wani daban da sunan fadilansa kafin ya dauko file nata ya fito asibitin.

Wani asibitin abokinsa ya buqaci wani oxygen din take ya biya ya karba ya dawo gida.

Koda ya dawo mum tayi sallah taci abinci ta huta ba laifi Dan haka ta sake wanka suka fitowa zuwa gurin fadila batareda Haroon ba sbd shine yayita kulawa da mum din tareda Mum Atee da Bata nunawa Dr Aleena din komai na hakama mummy Sarat matar Dad Lameenu ta shigo sbd Dr Aleena mutuniyata ce sosai
Tarba me kyau tayi mata tareda asmy da hawwah yayanta.

Kai tsaye daga gida office dinsa suka koma asibiti acan suka hau tsananin bincike da tantancewa tareda aune aune.

Kansa ba qaramin zafi ya dauka ba
Ita kanta mum din tana cikin fargaba da tashin hankalin abinda zasu iya tabbatarwa.

Haroon ya kira yaje ya taho dasu umma da fadila wadda kwata kwata bayason ana damar da ita da yawo.

A cikin Daren kwana sukai shi da mum dinsa da wasu amintattun likitocinsa suna bincike da aune aune harma da hotunan Daya kamata suyi mata duk sunyi.

Sai asuba suka samu kansu tareda tabbatarwa da Jamaal chances na surviving dinta Bai wuce 2% ba sbd koma Menene aka rikida oxygen din data Dade tana shaqa yayiwa lungs nata da cikin mummunan illanda sai addua kawai Amma dai idan har ta take lokacin aurensu zasu tafi da ita waje su miqawa wasu manyan likitocin su Gani ko zaa samu 2% din tayi Aiki.

Sakamakon Bai gama kammaluwa duka ba Dan haka mum ta Hana a sanar da Jamaal din abinda suka fara Gani Dan bandashi Akai sauran aikinba ta sallamesa ne.

Da kansa ya mayar dasu umman gida Haroon Kuma ya tafi da mum gida.

MAMUH

DR JAMAAL JEEY SEELAH

AMEENATOU SEELAH

DR ALEENA SEELAH

MAM SEELAH

LAMEENU SEELAH

OMAR SEELAH

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!

24
Koda suka Isa gida mum tayi magana sosai da Haroon ta sanar dashi matsalan datake shakkan sanar da Jamaal Dan batasan tayaya zai fara ba Kokuma ta Ina zai fara binciken Wanda yayi wannan mummunan aikin na rashin Imani da tsoro tareda rashin tausayin daukan ran Wadda take fama da rayuwarta tin haihuwa.

Shiru Haroon yayi sbd Shima hankalinsa ya tashi da wannan zancen Dan kuwa yafara Jin tsoro da wani irin tashin hankalin na sake shigarsa idan har Jamaal ya tsananta bincike duk da baisan waye yayi wannan aikinba Amma dai Yana shakkar binciken Hakan ya binciko masa abinda zai karasa dagula Rai da kansa bayan yanzu lafiyan fadilan suke tsananin fata Dan itace farin ciki da abinda Jamaal dinsu ke buqata.

Koda Jamaal ya dawo gidan cikin Bai Nemo kowa ba Kai tsaye bangarensa ya nufa ya shige bedroom dinsa ya rufe kansa aciki.

Wanka yayi Yana fitowa sallahn azahar kawai yayi ya kwanta sbd kansa Dake Neman tsagewa da ciwo.

Bacci sosai yayi Wanda yake cikeda mafarkai masu nauyi Dan haka Yana tashi da laasar wani wankan ya sake jikinsa ya sake daga nauyi ya shirya ya fito cikin doguwar jallabiya fara qal Data kwanta jikinsa tayi masa wani irin kyau na nutsuwa.

Masallaci ya fita acan yayi sallah tareda Dad dinsa Wanda yayita Kiran wayarsa Baya samu.

Zuba masa idanuwa Dad din yayi bayan sun gama gaisawa ya tambayesa jikin fadila sbd gobe ne daurin auren nasu Wanda zaayi sa kaman na Wainda suka samu cikin shege sbd kawai yanayin amaryan.

A daidai wannan lokacin da gabar Jamaal din kansa yayi sanyi matiqa tareda shiga wani irin fargaba da tsoro me tsananin gaske.

Kai tsaye bangaren Jamaal din suka nufa hadda Dad din Wanda zaiyi magana da Dr Aleena Dan Basu zauna suka tattauna ba tinda tazo.

Suna shigowa tana zaune Palo tana karanta wasu bayanai ta email dinta da Dr Martinez ya dawo mata dashi Akan matsalan fadilan Data tura masa bayanan da komai nata tin jiyan.

Akan Jamaal idanuwanta suka fara sauka ta rufe iPad din hannunta tareda kifeta gefenta tana mayar da kallanta kan Mam da Shima ita yake kalla cikeda kulawa Dan har cikin ranta Yana Sonta Amma yasan bama zai fara maganar mayar da aurensa da ita ba sbd Jamaal dayaji zafin rabuwarsu fiyeda komai hakama dawo da aurensu Jin yakeyi kaman zata iya sanarda Jamaal wani abin game dashi ne shiyasa bayason zaman Jamaal a hannunta ya dawo dashi hannunsa tintini.

Sannu da zuwa tayi masa cikin sakewa da kulawa tana sake murmushinta me kyau da tsari.

Shima cikin farin cikin ganinta da kulawa yake amsawa yana qarasawa ya zaune kujeran gefenta Jamaal kuwa gefenta ya zauna Yana Saka hannunsa cikin nata sbd samun sassaucin abinda yakeji zuciyarsa na ciki ayau din.

Fira sukeyi sosai tsakanin mum din da Dad da Haroon Wanda ya raba hankalinsa kan firar da Kuma Jamaal Wanda Bai iya furta ko kalma Daya ba Dan Yana cikin nasa tinanin daban.

Abinci mum Atee ta Aiko anan bangaren aka jere musu a dining din Jamaal ta Basu Daman cin abinci a tsakaninsu da ‘yayansu.

Mum da kanta ta takurawa Jamaal cikin kulawa Mai tsananin gaske yasamu yaci abincin yasha ruwa yabar dining din and magrib datai.

Yana barin gurin mum ta bisa da kallo kafin ta dawo da kallanta kan Mam Dan karantar yanayinsa sbd ko kadan batason yasan me suka gano batareda sun fitar da fadilan waje ba.

Sallan magrib sukai suna gamawa Jamaal yabar gidan da motarsa.

Dad da Haroon ne tareda Dad Lameenu suka dawo ciki.
Kai tsaye office dinsu na gida suka nufa harda Haroon suna tattauna maganar wani aikin dayake hannunsa na fito da yaran BB da tsautsayi yasaka aka kama dayansu sbd wani aikin boyen da yayi musu.

Suna gama maganar dagowa Dad yayi ya Kalli Haroon Yana karantar yanayinsa tsawon mintina kafin yace

“Meyake faruwa ne da Jamaal Bayan gobe ne daurin aurensa??
Akwai wani matsalan ne Daya kamata na sani?
Menene yake faruwa?

Dad Lameenu ma zubawa Haroon idanuwansa yayi Yana kallansa Dan Jin Abinda yake faruwa da Basu saniba.

Dagowa Haroon yayi ya Kalli dad din Yana Jin jikinsa na sanyi,
Numfashi ya sauke ahankali kafin ya sake dagowa cikin sanyin murya yace

“Jikin fadila ne yayi tsanani sosai,
Mum ma ko bayan isowanta jiyan Saida ta dubata sosai karshe ma a asibiti suka kwana akanta Amma dai angano matsalar daga oxygen data amfani dashi yayi mata mummunan illa Kuma abin tashin hankalin shine oxygen da ita kadai take amfani dashi ne aka gurbata da wani abin Amma dai mum tana kan binciken zasu gane Menene”

Dad Lameenu wani numfashi ya hadiye ya koma masa ciki kafin ya Dan juya ya Kalli Mam Wanda Babu abinda yayi
kafin yayi wata magana Mam din ya rigasa da Bude Baki a natse yace

“To shi Jamaal din yasan da Hakan?
Yasan me sakamakon ya bayar?

“No sai sauran results din sun Hadu zuwa gobe mum zata sanar masa”

Wani sanyayyar numfashi Mai hade da bayyanarda alhini da tausayi Dad Lameenu ya sake
Shikuwa Mam har lokacin Bai nuna kowanne irin yanayi ba sai shiru da yayi kafin ya sauke karamin numfashi Yana Mata fatan samun lafiya ya sallami Haroon din ya fice yabarsu.

Tinda ya fita babu Wanda yayi magana a cikinsu sbd zuwa yanzu da suka manyanta kowa yagama sanin tinanin da kowa keyi a kowanne lokaci wani abin ya taso.

Jamaal Bai dawo gida ba sai dare sosai bayan ya baro gidansu fadila jikinsa a matiqar mace Dan yau fadilan da kanta take kuka tana rokon ya mata alluran da zata rasa hankalinta Dan ta Dena Jin Abinda takeji zuwa safe.

Iyayenta kuka sukeyi da Hawaye a gabansa na tausayinta
Duk wata karfin zuciyarsa Saida kukan fadilan ya karya masa shi.

A goben da zaa daura masa aure da ita a goben Inshallah zasu bar kasar sbd komai na tafiyan ya kammala goben ne ranar tafiya.

Mum dinsa ma jikinta mutuwa tayi da yanayinsa Dan haka Bata takurasa sosai ba akan abinci,ice tea ta hada masa kadai ya Sha ya shige bedroom dinsa.

Wanka yayi ya kwanta Kai tsaye Yana rufe idanuwansa wani nauyi na karuwa a zuciyarsa.

Karfe uku na tsakar dare Haroon ya fito daga bangarensa cikin tashin hankali da damuwa me tsananin gaske ya nufo part din Jamaal da wayarsa a hannu yayi knocking.

Knocking yakeyi sosai Amma Sam Babu alaman ma suna jinsa Dan haka ya cikin tashin hankalinsa Dake karuwa ya Kalli wayarsa Dake sake ringing Kiran siddeeq Yana shigowa..

Juyawa yayi kawai da sauri ya koma dakinsa cikin gaggawa da rawar jiki ya Dora jacket babba akan sweatset din Dake jikinsa ya zari keys din motarsa ya fito.

Baiyi wata wata ba ya fada motan ya tayar cikin zafi yayi wani mugun horn dashine ya tayar da Dad dinsu da shi kansa Jamaal din harma da mum dukkaninsu a tare suka tashi zaune suna sake Jin horn din a kunnensu sosai.

Time kowannensu ya kalla cikin mamaki Mai girman gaske.

Ziro kafafunsa daga gadon Jamaal yayi tareda saukowa Yana nufar window na dakinsa ya ware curtain Yana kallan harabar gidan daidai motar Haroon din na ficewa daga gidan cikin wani irin gudu me zafin gaske.

Sakin curtain din yayi cikin tsananin mamaki tareda juyowa Yana ziro slippers a kafafunsa Shima jacket din ya Sako kan kayan baccin jikinsa ya fito Palo Kai tsaye Yana nufar kofar ficewa daidai Nan mum itama ta fito tana cewa

“Lafiya kuwa?
Meyake faruwa?

Batareda ya juyowa ba yace ta koma daki zai dubo meyake faruwa.

Yana fitowa harabar gidan Dad ma Yana fitowa cikin mamaki da shakkar abinda ya fidda Haroon a lokacin.

Securities din gidan ma duka suna tsaye a harabar gidan

Dad da mamaki yace

“Meyake faruwa?
Waye ya fita da motan Haroon din?

Jamaal kuwa Yana isowa Kai tsaye yace

“Wats going on here?”
Waye ya fita?
Ina Haroon?

Daya daga cikin securities dinne ya Kalli Dad yace

“Sir,sir Haroon ne ya fita Amma security Daya yabisa sbd dare ne sosai Kuma baima tsaya mukasan meye matsalan ba ya….

Jamaal da kallo Daya yayiwa gate din da Haroon ya fice Bai tsaya Jin sauran zancen ba ya juya ya koma Kai tsaye key ya dauko da wayarsa Daya kunna Yana kokarin Kiran numbern Haroon.

Dad na ganin fitowansa da key cikin mamaki da tashin hankali yace Maza securities su janyo mota su bisa Dan bazai bari yayansa duka biyu su fice a Daren ba batareda yasan meyake faruwa ba da rashin tsaro.

Mum ma hankalinta tashi yayi mummunan yi da sauri ta dauro jallabiya me girma akan kayanta ta fito Amma Jamaal yace kada Dad yabari ta biyosa.

Daukan wayar Haroon yayi daidai da isar Jamaal motarsa cikin murya Mai sautin Kai tsaye yace

“Meyake faruwa?
Meyasa zaka fita a wannan time din?
Bazaka iya sanar da kowaba kafin ka fita?
Ganinan fadamun inda kake kawai…

Shiru yayi tareda dakatawa daga Bude motan dayake kokarin yi maganar da Haroon din ke fada cewan gobara ne sosai ya kama gidansu fadila.

Wani mummunan jiri ne Mai qarfi sosai ya debesa yayi saurin daga motar
Mum ma da saurin gaske ta qaraso gurinsa itada dad tana tambayarsa Menene Amma Sam Bai ya cewa komaiba sai idanuwansa da suka sauya take ya dago ya zuba mata Saida gabanta yayi mummunan faduwa.

MAMUH

AMEENATOU

ZAFIN KAI

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!

25
Dad na ganin Hakan yayi saurin kallan Abdul Yana cewa Maza a fiddo mota a biyo bayansu da ita sbd yasan koma ya cewa Jamaal yayi zamansa ba zaman zeyiba Dan haka ya koma ciki Ya Sako jallabiya doguwa fara kal ya fito.

Koda ya fito tini Jamaal yabar gidan Dan haka Kai tsaye shi da mum da securities suka mara masa Baya zuciyarsa na nauyi da fatan kada komai ya samu ‘yayansa a cikin wannan sililin Daren ace sun fita Babu Wanda yake tareda jamian tsaron lafiyarsa a cikinsu har gwara Haroon ance security Daya ya bisa
To Jamaal fa¿.

Mum kuwa duk a tsorace take ma kwata kwata sbd tsoron idan ba wani abin ne ya faru ba me girma ko zai faru,
Koma dai Menene itadai fatanta Allah ya tsare mata ‘yayanta ya Basu kariya da kaucewa musiba da masifa kowace iri.

Dad daya kasa tantancewa ko canko Menene yake faruwa shiru yayi Yana fatan Isa ga yayansa cikin gaggawa kafin kome zai farun ya faru tukuna…

Bayan motar Jamaal suke hangowa Yana gudu sosai Wanda ya Saka jinin Dad fara Hawa Yana Jin zuciyarsa na wani irin tsalle da rawar tashin hankali Dan kuwa Jin yayi kaman zuciyarsa ne a cikin motar Jamaal din ana wannan gudun da ita.

Mum kuwa idanuwanta a rufe ma suke tana Jin alamun itama BP dinta ya haye sama a take.

Hanyar gidansu fadila da suka nufa ya Saka Dad Jin wani irin Abu me nauyi Yana saukowa daga maqoshinsa zuwa kirjinsa sbd ya tabbatarda idan ba ciwonta yayi ajalinta ba to tabbas lameenu ya aika su BB rufe aikin kwata kwata kafin asanar da Jamaal sakamakon Wanda Shima akwai tanadin da yayiwa Hakan Amma a cikin sanyi da cike aiki take batareda barin kowace alama ba.

Tin daga nesa wutar Dake cin gidan sosai suke ganinta
Take jikin mum ya dauki rawa hawayen tashin hankali na ciko idanuwanta sbd Jamaal kada yace zai shiga gidan.

Dad da Shima dukkanin jikinsa ke cirewa sbd wannan tsoron tini yace ayi parking cikin daga murya.

Ko gama parking baayiba Dad ya Bude motan ya fito yayi gurin Jamaal da sauri Yana Kiran sunansa hankalinsa tashe sedai Jamaal din Baya jin komai fadila kawai dayake buqatan Gani a hannuwansa.

Haroon da siddeeq ne suka hango zuwansa da gudu Haroon yayo gurinsa ya tareda tareda rungumesa sosai daidai isowan Dad idanuwansa kaman zasu fado sbd tashin hankali da sauri ya rungume Jamaal din ta Baya Shima Yana Jin zufa na tsinko masa.

Jamaal zare jikinsa yakeson yi Amma sun masa wata irin kyakkyawar runguma Haroon na cewa

“Fadila is safe siddeeq ya fito da ita”

Wannan kalaman ne suka Saka Jamaal din jikinsa ya saki tsawon minti Daya kafin ya dago idanuwansa jajir Yana buqatan ganin fadilan.

Ambulance ta asibitinsu ce ta iso cikin gaggawa aka dauki Fadila wadda batasan Ina kanta yake ba tareda umma wadda itama take a sume sbd hayaqin Daya bugeta.

Motan kashe gobara ce itama ta iso daidai lokacin sukuma suka bar gurin zuwa asibiti cikin gaggawa.

Siddeeq barinsa Akai tareda mutane da masu kashe gobara harma da Police da suka iso gurin cikin tashin hankali sbd baba Dake cikin gidan baa fiddosa ba,

Mum asibiti suka marawa su Jamaal Baya itada da Dad Wanda yakejin Yana dawowa hayyacinsa daidai sbd barin yayansa gurin Dan motan Haroon ne bayan ambulance din sukuma suna bin tasa motar.

Ana Isa asibiti cikin gaggawa likitoci suka amshi fadila da umma aka shige emergency dasu
Haroon kuwa da Dad Jamaal din suka zauna tareda dashi Dan basa karfin gwiwa.

Mum da ita aka shiga emergency din Dan taimakon gaggawa fadilan take buqata sbd Bata tareda oxygen nata tini ya fizge yana can.

Zaman jiran tsammani me azabar gaske sukeyi dukkaninsu tin daga Jamaal din har Dad da Haroon,

Haroon sai Kai da kawo yakeyi Yana Jin kaman ya yayewa Dan uwansa abinda yake ji.

Sai asuba likitocin suka samu shawo kan fizgo numfashin fadila aka Saka mata wani oxygen din bayan mum ta tantancesa.

Umma kuwa Daman tini ta farfado Dan Daman hayaqi ne ya sumar da ita Amma dayake mijinta da yarta ne a ranta tini ta farko cikin sanyin jiki da fargaban baba da akace Yana can tareda siddeeq ita Kuma fadila tana asibitin tareda ita.

Dad da mum ne suka koma gida bayan sallan asuba suka bar Haroon tareda Dan uwansa.

Suma bayan sallan asuba dubo fadilan yai suka dawo office dinsa anan yayi shiru Yana tinanin yanda zasuyi su sanar da umma gawar baba na asibitin.

Siddeeq ya kalla cikeda kulawa da tausayawa Dan Shima maraya ne gaba da Baya su baba dinne gatansa danginsa yanzu baba ya rasu.

Har karfe tara na safe suna asibitin Kuma Basu sanar da umma komai ba sai guraren goma suka taho dakin datake Jamaal ne Kai tsaye ya sanar da ita rasuwan baban cikin dacin zuciya da tausayi me tsanani.

Numfashi ta sauke ahankali me zafin gaske batareda ta motsa ba sbd jikinta ya Bata Hakan Kuma zuciyarta tini ta amsa Hakan ta karbi jarumta.

Dago jajayen idanuwanta dasukai jajir tayi ta Kalli siddeeq Dake Hawaye sosai zuciyarsa na tarwatsewa.

Cikin karfin hali ta Bude Baki ahankali tace

“Haka Allah ya kaddaro Kuma na amsa wannan hukuncin na ubangiji,Allah yaji qansa yayi masa Rahama ya bamu danganar rashinsa.”

“Amin” dukkaninsu suka furta cikin damuwa da sanyin jiki.

Karfe goma da Rabi Akai janazah dinsa aka rufesa suka dawo.

Kaman yanda yake ayau din zaa daura aurensa da fadila baa daga ba Dan haka bayan karfe biyu na Rana aka halarci masallacin da zaa daura musu aure.

Cikin fararen kayanda suka bayyanarda kamanninsu sosai shida Haroon suka fito tareda mahaifinsu Wanda Shima fararen kayan ne a jikinsa irin na ‘yayansa Wanda aka zuba kudi kaman baa San darajansu ba aka Siya kayan aka Dinka.

Qamshinsa daban yake Dana kowa Dan haka take qamshinsa ya doke nasu nasa kadai ake ji Kuma a Hakan cikin Baya tattareda walwala ko Daya sbd halinda matarsa take ciki duk da haka kawai saukin da Basu tsammata ba yazo mata da safen duk da batada karfi ko kadan har lokacin Amma ta Bude idanuwanta sosai tayi magana dashi tareda nuna masa ta samu karfinda inshallah zata iya adon aurensu da zaayi a yau din.

Karfe biyu daidai Aka daura masa aure da Fadila kaman yanda yake buri da fata ta tabbata cikakkiyar hankalinsa,matar Dr Jamaal Mamman seelah.

Bayan daurin auren Yan jarida da media da ba’ama San ya Akai suka sani ba suka karaso gurin sedai kafin su samu Daman daukan hotinansa yabar gurin batareda ya tsaya komaiba sedai Haroon ne ya tsaya a amatsayin Jamaal din yana miqa godiyarsa ga wainda suka halarta Yana amsa adduoinsu batareda ansan bashi a gurin ba Dan hatta su Dad din Basu dauka Haroon bane Jamaal ya tafi.

Siddeeq ne yake Jan motar Jamaal din har suka Isa asibiti zuciyarsa wani fayau yake jinta jikinsa na sanyi kalau batareda yasan wane irin yanayi ne yakeji a jikinsa ba.

Suna Isa asibitin kusan dukkanin wani likitan Dake asibitin Yana dakin fadila cikin tashin hankali da gaggawan cetan ranta kowa na nuna kwarewansa Dan sanin mahimmancinta Mai tsananin girma ga Dr Jamaal din.

Hatta mum dinsa tana dakin cikin nuna kwarewanta da son cetan ran sirikitarta wadda rashinta zai taba rayuwar danta fiyeda yanda suke tinani.

Ganin umma zaune bakin dakin idanuwanta jajir dukkanin jikinta a Sanyaye zuciyarta tayi wani irin nauyi da kirjinta ke Neman kasa dauka.

Dakatawa yayi cak bakin Kofar dakin ganin yanda nurses ke fitowa da gudu suna komawa cikin bawa abinda sukeyi mahimmanci me girma.

Siddeeq ma kasa motsawa yayi daga inda yake tsaye zuciyarsa na bugawa da karfi ya juya Ina Dr Jamaal din yake ya kallesa da jajayen idanuwansa Dake sauyawa da fargaban abinda suka tarar.

Kasa motsawa Dr Jamaal din yayi tsawon mintina biyu Yana Jin dukkanin wani sanyi na gauraye gangar jikinsa kafin ya daga kafafunsa ahankali ya Isa kofar dakin ya Bude ya shiga daidai kunnuwansa na dauko sautin maganar Dr zayyan.

“Time of Dead 3:06”

Innalillahi wainna ilaihirrajiun” shine abinda mum ta fada jikinta a matiqar Sanyaye zuciyarta na shiga wani irin sanyi da mutuwar jiki me tsananin gaske.

Sauran likitocin ma gaba Daya jikinsu sanyi yayi musulman ciki suna ambatar

“innalillahi wainna ilaihirrajiun da allahu Akbar”

Kafiran ciki kuwa tausayinta Dana Dr Jamaal ne yake rufesu sbd tasha wuya sosai itama a iyama lokacinda ta fara zuwa asibitin kadai bare rayuwarta ta Baya.

Ficewa likitocin suka fara ganin Dr Jamaal din a tsaye bayan sun rufeta har fuska sun gama rubuta komai a file dinta anyi signing anrufe an ajiye a gefe shikenan ita ta huta da gwagwarmayar duniya.

Mum dinsa ce kadai ta rage ta tako ahankali batareda ta iya cewa komaiba sai hawayen Daya ciko idanuwanta Yana gangarowa ta rungumesa ahankali cikin mutuwar jiki tana basa hakuri hawayenta na Kara gudu.

Fashewan kukan umma me sautin daya sake karya zuciyar kowa ne ya sauka cikin kunnuwansa take ya rintse idanuwansa dasukai wani mummunan ja yanajin dukkanin zuciyarsa na kakkaryewa tana watsewa.

Siddeeq ne ya rungume umma Yana tarota jikinsa sbd kukan datakeyi hadda na mijinta data rasa a ranar kukan Bai fitoba sai yanzu data rasa yarta taji abinda ya dunkule a zuciyarta ya fashe mata.

Wani irin kuka me cin Rai da qunci me tsanani takeyi sautinsa na karya dukkanin zuciyoyin sauran likitoci da Jamaar Dake gurin Amma Babu me iya cewa komai sbd tana buqatan yin kukan.

A ciki ma mum ce keyiwa Jamaal din kukan dashi zuciyarsa Bazata iyaba sbd Jin ma yakeyi baida sauran emotions kwata kwata bayajin komai face dutse a zuciyarsa.

Labarin na Isa gurinsu Dad da Haroon gabaki dayansu asibitin suka dungumo cikin tashin hankali musamman Haroon Dan kuwa JAMAAL ne a ransa,
Jin yakeyi rasuwar fadilan Shima tana gigita kansa da nutsuwansa dan haka a rikice ko Gani sosai bayayi suka iso asibitin.

MAMUH

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!

26
Shi kansa Dad da Dad Lameenu cikin damuwan halinda Jamaal yake ciki suke,
Mum Atee da Ayesha ma tini suka iso motansu mummy Sarat na bayan tasu Dan haka take asibitin ya cika da familyn seelahs cikin damuwa da tashin hankalin yau wace irin Rana ce?
Mahaifinta ya rasu yau,
An daura mata aure yau itama ta rasu a yau din.

Haroon na isowa kallo Daya yayiwa Dan uwansa yaji idanuwansa sun ciko da Hawaye masu tsananin zafin gaske suna gangarowa ya rungume Jamaal din.

Dad ma na isowa rungumesa yayi Yana kallan mum Dake hawaye sosai sbd tausayin fadilan da wuyar datasha tareda tausayin danta Dan shine yake cikin azabar zuciya yanzu me tsanani ta sani.

Dakin gawar suka bari suka koma office dinsa gaba dayansu familyn kowa fuskansa Babu dadi Dan tausaya masa bisa ba rashin dayayi Dan kuwa Babu Wanda Bai tabbatarda irin so da matsayin da fadila take dashi a rayuwarsaba.

Umma siddeeq ne kadai a tareda ita sai mum data koma gurinsu daga baya Dan ummanma itace abar tausayi fiyeda kowa Dan itace tayi rashinda sai me karfin Imani ne zaiyisa Rana Daya Bai zauce ba.

Ganin Halinda umman ke kokarin shiga ya Saka mum Bada umarnin a kwantar da ita cikin gaggawa Dan taimaka mata.
Bayan an kwantar da umman harma anyi mata allurai da wasu abubuwan an samu tayi bacci ta baro gurinta ta dawo gurin Jamaal Daya kebe kansa a dakin dayake cikin lafiyayyar office dinsa ta fara kokarin yi masa nasiha da basa karfin gwiwan bawa zuciyarsa hakuri.

Gida kowa ya koma sbd Shirin janazah dinta wadda zaayi a Seelahs din bisa ga umarnin Dad tinda ta riga ta zama matar dansa.

Kafin lokacin yayi Yan uwan umman su uku tini suka iso daga garinsu mata biyu namiji Daya.

Su kansu sun tausayawa Jamaal sosai bayan yar uwarsu dasuke cikin tsananin tausawa rashin datai.

Fadan halinda Jamaal ya shiga Baya misaltuwa Dan kuwa ya kebe kansa daga kowa baya buqatan kowa Baya son kusanci da kowa ko kadan.

Abu Daya da suka sani shine Babu Wanda yaga hawayensa bayan Dan uwansa idanma yayi sbd ya nesanta kansa da kowa bayan Haroon Babu Wanda yasake ganin ko fuskansa.

Yanayin jikin umma Daya rikice da Kuma shi kansa Jamaal din Daya rufe kansa ya Saka dole aka daga jana’iza din har zuwa da safe dakuma yayan baban fadilan Dayake hanyar isowa Shima.

Sai dare sosai Jamaal ya baro asibiti tareda Haroon suka iso gida bayan Haroon yaje ya kamawa Yan umman din masauki hakama Dan baba ma Daya iso duka guri Daya aka saukesu tinda gidan ya kone Babu yanda zaa iya kwana cikinsa.

Koda suka iso gida karfe kusan Sha biyu na dare Dan haka Kai tsaye part din Jamaal din suka nufa.

Mum da Dad ne a palon suna magana cikin Dan daga murya sbd bacin ran da mum ke ciki me tsananin gaske tace

“Kasan Hakan shine yayi sanadin rasa ran yarinyar Nan bawai gobaran da aketa yadawa ya kasheta ita da mahaifinta ba?

Tayaya zaace acikin asibitin iya oxygen dinta ne datake amfani dashi ake gurbatawa da Poison,
Shin bakai tinanin halinda ‘danka zai shiga ba idan ya rasa macen dayake so fiyeda komaiba?
Tayaya kake tinanin zaka fuskancesa idan yasan sakamakon Poison datake shaqa a oxygen ne ta rasu,
Tayaya kake tinanin zai amsa zancen kaman kasheta ne Akai Kai tsaye Babu kwana kwana?
Bakaji tausayin yarinyar Nan ba tsawon rayuwarta rayuwa takeyi cikin wahalar rashin numfashi sai an Siya mata??

Cikin nutsuwa batareda daga hankali ba Dad din ya kalleta da idanuwansa yace

“Ko zan me kike nufi da wainnan kalaman naki?
Me kike nufi da oxygen nata?
Ke da kike likita kikasan aikinki har kikasan akwai poison a iskan datake shaqa meyasa Baki sanar masa shi ‘dan naki ba kika bari har ta rasa ranta….

Katsesa mum tayi hawayen idanuwanta suna qara gudu tace

“Ban taba son sanin ‘yayana Susan waye Asalin mahaifinsu ba sbd Hakan zai tarwatsa zuciyansu,Amma wlh tallahi Babu ranar da bana danasanin Kaine uban yayana masu tsafta,
Me kake tinani?
Na fito na fadawa JAMAAL Ina tinanin mahaifinsa yasan Menene yake damun matar da zai aura sbd shine yasan meye ne yake damun oxygen datake shaqa??
Bazan fada masa ba Amma koman Daren dadewa yayanka zasusan waye Asalin mahaifinsu Wanda Baya barin komai ba dalili,
Yanzu data bar duniyar saika ringa kwana da Shirin koyaushe danka zai iya sanin waye ya kashe masa matarsa data mutu a ranar da aka daura masa aure da ita…

Wani numfashin me sanyi da nutsuwa Dad din ya sauke zaiyi magana Haroon dayake gaba ya shigo Yana kallan mum dinsu da kalaman dayake ji abakinta Dan kuwa bazai taba yadda da Dad dinsa zai iya kisa ba duk da Barnar dasuke aikatawa bayan fage Amma mahaifinsa bazai iya kashe Rai ba bare macen da already tana fama a tsakanin Rai da mutuwa.

Jamaal kuwa idanuwansa dasuka qarasa rinewa gabaki Daya ya dago ya zubawa Dad din Wanda ya miqe tsaye Yana kallan jamaal din zufa na joqosa daga kuryan jikinsa.

Mum ma mummunan faduwa gabanta yayi zufa na tsitsifo mata Dan kuwa Bata fatan Jamaal yaji abinda suke fada.

Dad Jamaal din yake kallan Yana kokarin danne abinda yake ransa Yana ambatar sunansa cikin kulawa zeyi magana Jamaal din ya juya ya kallo Mum ya Bude bakinsa da yayi masa wani irin mummunan nauyi Kai tsaye yace

“Results din fadila duka sun tabbatarda oxygen nata ne yayi sanadin komai har rasuwanta right??

Wani mugun zufa da faduwan gaba ne ya Saka mum juyawa ta Kalli Dad Wanda Shima ita yake kalla kafin ya matso zaiyiwa Jamaal din magana Jamaal ya katsesa da sake jefawa mum tambayarsa.

Numfashi ta sauke zuciyarta na nauyi ta matso tareda kamo hannunsa Daya cikin tsananin sanyi da baqin ciki tace

“Eh, oxygen nata shine yaringa poisoning nata ahankali harta rasu Amma muna Saka ran daga karfin da yayi mata ne da oxygen din shiyasa ya zama kaman poison ya mata illa..

Baice komaiba zame hannunsa yayi daga cikin nata ya zari keys din hannun Haroon ya juya ya fice.

Duk yanda Haroon yaso binsa kasawa yayi sbd mamaki da shock din dayake ciki Shima duk da Babu tabbacin Dad dinne itama mum kawai zargi ne sbd Dad baiso aurenba da farko.

Koda ya Isa asibiti Kai tsaye file din fadila ya dauko yafara dubawa ko Gani sosai bayayi kafin ya fito ya nufi lab dinsu a cikin Daren ya buqataci sabon awo tsakanin oxygens din sabo da tsoho Dana fadila.

Haroon baro gida yayi ya biyosa asibiti Amma Sam kwata kwata ya kasa samun ganinsa Dan kuwa a cikin Daren gaba Daya ya daga hankalin asibitin akan sabon awo da komai Wanda ya bawa likitoci da ma’aikatan lab dinsu tsoro da shiga tashin hankali Dan kuwa da farko binciken boye Akai baa son daga zancen.

Koda asuba tayi tsaban tashin hankali har an hada results din Wanda ya tabbatarda mutuwar fadila due to gurbatan oxygen nata ne.

MAMUH

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!

27
Wani mummunan jiri ne ya dibi Jamaal din Wanda sai alokacin ya fashe Da kukan Daya girgiza Haroon da mum dinsa da isowanta kenan asibitin cikin tashin hankali da tsananin tsoro sbd Kwana sukai itama da Dad din cikin tashin hankalin fitina da maganganun da suka Sakata Jin son barin qasar a ranar.

Duk wani sheda ko alaman inda poison din ya samu shiga oxygen dinta Jamaal yayi daga daren zuwa safe Bai gane ba sai Abu Daya wato yawan zuwan BB asibitin Wanda ya samu tabbacin duk karshen wata yake zuwa so Daya dubiyan kaninsa yaronsa da suka karya da gangan suka ajiyesa asibitin yaqi warkewa sbd Daya kusa warkewa saisu sake lalata gyaran.

Hakama mum dinsa ta kasa fada masa komai taqi sake maimaita masa tabbas mahaifinsa ne yayi Hakan,

Wane asalin rashin Imani ne zai Saka a taba fadila macen da numfashin duniya Bata iya shaqa saina Siya,

Gida suka dawo Kai tsaye palon Dad dinsa ya nufa zuciyarsa na qunan dayake Jin har wata wuta ce take cin kansa.

Babban abinda fara bawa su Dad din mamaki da shakka shine Kai tsaye kafin goman safe tini akaiwa su BB da yaransa kaf mugun Kamun Daya fara yaduwa a labari tareda tabbaci akan zargin kamasu da sirka poison acikin oxygen na asibitin SEELAHs Wanda yayi sanadin rayuwar matar Dr Jamaal Seelah din,
Hakan ya qarawa labarin saurin yaduwa sosai da gudu kaman wutar daji take Yan jarida sukaiwa asibitin da gidan kawanya.

A yanda Jamaal ya nufo su Dad din mum dinsa ce tayi saurin Shan gabansa tareda riqe hannunsa Dan duk mugun halin Dad bazata so yayanta suyi sa’insa da mahaifinsu ba bare maganar datai da Dad a ajiyan ta tabbatar mata da Dad Babu abinda bazai iyaba Dan haka ta riqo hannun jamaal ta girgiza masa Kai cikin qaramin sauti ta Bude Baki tace Karkayi komai karkace komai wannan umarni nane,
Haqqin dayake hanunusu bazai taba taba yayana ba kaman yanda bakuda sani bakuda haqqi bazanso ka taba gurbata kanka aikinsu ba.

Cikin Bacin Rai me tsananin gaske Dad da Alh Lameenu suke kallanta zaiyi magana cikin hada zufan tashin hankali mum Atee ta shigo cikin tashin hankali tana sanar musu ga asibitin SEELAHs can ana kokarin Banka mata wuta.

Dayake tini Jamaal ya Saka Aka sallami kowa tareda dauke gawar fadila tana can anai mata sutura baice komaiba Se hannun mum din Daya kama ya juya suka bar palon sbd ta dauresa da maganarta da alkawarinta bazaicewa su Dad komai ba Amma yayi alkawarin sai ya tabbatarda basuda komai,
Ahankali zai tabbatarda yasan komai da mum taqi fada masa da abinda su Dad din ke boyewa,
Bai damu da dukiyar seelahs ba Saiya tabbatarda Babu komai Daya rage acikinta sbd da ita akai kisan fadila.

Karfe goma da Rabi Akai janazan fadila aka rufeta,
Ana dawowa ya sallami su umman da kudi me yawa da zaa kula da umman kafin ya waiwayosu.

Siddeeq kuwa anan Lagos din ya samar masa gurin zama kafin daga baya zai bisa idan anmasa komai.

A wannan mummunan ranar baa kwana ba SEELAHs suka rasa asibitinsu tareda shiga shakku a zuciyoyin mutane da take abin yafara kokarin tabasu duk da su Dad din sun tashi tsaye kada Hakan ya tabasu Dan kuwa sunfara ganin matsala babba na Neman tinkaro su.

A wanna mummunan ranar Dr Jamaal Mamman seelah ya Yanke duk wata alaqarsa da ahalin seelahs ya goge sunansa daga kudin tarihin gidan Dan har abada bazai taba sake hada alaqa dasu ba kowace iri ce ya yanketa Baya buqatanta.

Haroon ya shiga Mummunan tashin hankalin wannan masifar data fadowa familynsu a Rana Daya lokaci daya,
Tayaya zai iya rayuwa a tsakanin mutum biyu dayafi so a rayuwarsa sun rabu sun yanke alaqa a tsakaninsu,
Kaman yanda Jamaal din ya Yanke alaqansa da Dad Kai tsaye Dad din cikin fushi da bacin Rai ya yanke Shima alaqansa dashi sbd Hakan ne kadai zai rufa asirinsu su tsira a yanzu sbd a wuni Daya yayi qasa da asibitinsu ga faduwansu na Neman tasowa a qanqanin lokaci Dan haka nesantar su da Jamaal din kadai zai sakasu samun tattara mutuncinsu su dawo dashi a idon mutane da abokan kasuwancinsu kafin manyan sirrikansu su bullo komai ya lalace batareda sun shirya ba Dan Basu hango wanna masifarba su kansu a yau din.

Dr Aleena kanta Hakan shine nutsuwa da Kwanciyar hankalin datai shekaru Bata samu ba yanzu da alaqa ta Yanke kwata kwata tsakanin Jamaal dinta dasu Mam din Dan haka ta tattara itada Jamaal a ranar suka bar qasar a cewansu har abada bashi ba dawowa bare alaqa tsakaninsa dasu,
Haroon na ran Mum Amma Kuma koyaushe Haroon din zabar mahaifinsa yakeyi akan mahaifiyarsa Amma Kuma kaunar Dan uwansa ta take ta kowa da komai Dan haka tafiyar Jamaal ta jijjiga duniyarsa Dan baisan ya zaiyi rayuwa babu Dan uwansa dayake kalla kaman Yana kallan mahaifiyarsa da Bata taredashi.

Jamaal Koda yabar qasar Nigeria yabarta cikin tsananin ciwo da quncin zuciya da tarwatsewanta,
Abinda yakeji a zuciyarsa wani dutse ne da bazai taba sauka da zuciyansa ba,
Son fadila yayiwa zuciyarsa mummunan illan busar masa da ita da bazai taba hucewaba bare son wani abin ba daban bama mace ba wadda wannan Kuma wani Babi ne Daya rufe ya kona bare ma ace akwai ranar budewansa.

Ita kanta mum tabaro kasar cikin tsananin damuwa da ciwon Rai sbd sun ringa sun sauya mata ‘da da dawowansa daidai Kila har abada Se Kuma wani ikon Allah datake fatan yazo,amma Jamaal Kam ya koma Asalin Dr jeey dinsa babu wata sakewa ko walwala Se kamewa.

Suna Isa Poland ko wata Bai rufa ba ya tafi Umrah daga can ya wuce Hutunda Bai dawo ba sai bayan watannin dasuka sauyasa ya koma wani lafiyayyan balareban bature ya sake budewa sosai sbd geamin da sauya rayuwarsa da yayi gaba Daya.

Ita kanta mum din ganinsa Saida ya Sakata Tara hawayen farin ciki a cikin idanuwanta na ganin wata irin kyau da tsantsan hutun Daya bayyana a tareda shi da wata lafiyayyar qasumbar data kwanta a fuskansa farinsa yayi mugun bayyana.

Sabuwar asibitinsa akai bikin budewa take yafara aikinsa tareda Bude Babin sabuwar rayuwa.


Ameenatou,Ameenatou wlh idan na kamaki a hannuna saina balla hannunki”

Hafiz ne ya fada Hakan Yana daga takarmansa Da baa Saka musu ruwa a jiqe suna tsiyayar ruwan wankan datai masa dasu zuciyarsa kaman zatai bindiga ta fashe sbd takaici.

Dadah Dake tayata Saka zip din doguwar rigar atampar data Saka sbd duk girmanta da zamanta budewar komai yi mata akeyi sbd tsaban gata da sangarta hatta ruwan wanka wani lokacin se an Saka yananta sun Kai mata tace

“Meenon Dadah wanka kikai masa da takarma ko sbd Neman magana?.

Dariyar data lotsa dimple dinta sosai tayi tana yin Dan qasa da murya sbd kada Yaya Hafiz din ya juyota tace

“Dadah bansan takarman basason ruwa bafa Kuma tin safe yau fada kawai yaketa yi dukana yakeson yi kawai”

“Duka dai? Kaman wata babyn roba Saiya dakeki Ina kallo.

“Eh Dadah nidai wlh karki bari ya dakeni tinda dai na zama budurwa kaman yanda Babbah ya fada.”

Kaman Yaya Hafiz din yaji abinda ta fada ya shigo dakin da takarmin Yana cewa

“Wlh bazan yadda ba tinda aka hanani dukanki se anbiyani takarman Nan,
Kunsan nawa na siyesu kuwa?
Idan ban ballaki ba zuciyata bazaitai sanyi ba”

Kanta yayo tayi saurin yin bayan dadah tana cewa

“Wlh bansan sabo bane bafa”

Wani sabon takaici ne ya ciyosa yace

“To dole Se kinmin wanka da takarma tsaban reni”

Kallansa dadah tayi zatai magana yace

“Allah dadah Kun gama Saka yarinyar Nan ta Rena ni,
Kwata kwata Kun sangartata Bata ganin girmana,
Yanzu fa wannan takarman bayan daurin auren da zani sbd zuwan Asalin me gidanmu na aikin site da zaiyi a kwanakin Nan ya sakanu siyansu sbd zaa dibi ma’aikatan da zaa tafi dasu can kamfaninsu na Lagos aiki ni inason zuwa shiyasa nakeson fitowa fes Amma tsaban mugunta yarinyar Nan ta jiqamun su”

Daga bayan dadah so takeyi tayi magana tana gudun ya jefota da takarman Dan haka Saida ta sake shigewa sosai tace

“Wannan baturen Dana taba Gani a site din da dadewa danaje karban kudin tafiya makaranta gurinka shine ze sake zuwa?
Dan Allah zanje kaje Dani Yaya Hafiz zan shanya Maka takarmin…..

Cikinta yayo cikin takaici kafin ya kamota Babbah ya shigo gidan take ta Bude Baki daga bayan dadah tace

“Babbah gashinan Yaya Hafiz ze taba baka yar budurwa”

MAMUH

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

28
Babbah na Jin Hakan yasan itace batada gaskia Dan bakinta Sam Baya bari tayi banna ko Neman magana ta cut dan haka ya nufo dakin Yana cewa

“Kai Hafiz banason zafin Rai fa,
Me tayi?
Yafe mata idan ta sake na bari ka Dan kadan dauki matakin Amma dai yanzu yafe mata kaga tayi wanka Karka Sakata gumi.”

Wani sabon takaici ne ya siqe Hafiz yace

“Hakafa da ake mun ya Saka yarinyar Nan ta Rena ni gaba Daya bata ganin girma na,
Allah duk ranar data shiga hannunsa saina balla siraran kafafun Nan nata”

Fitowa tayi daga bayan dadah tana marairaice fuska hadda ciko idanuwanta da Hawaye tana matsowa gabansa ganin Babbah na Nan tasan bazai taba barin a Daketa ba a gabansa shiyasa ta fito din ta Kalli Hafiz Dake juyawa zebar dakin tayi saurin riqo hannunsa tana sake narkar da fuska tace

“Yaya Hafiz dina Dan Allah kayi hakuri wlh tallahi inshallah bazan sake jiqa Maka takarminba bama zan sake sakawa ba nayima Maka alkawari na shiryu”

Dago idanuwansa da sauran fushi ke cikinsu yayi ya kalleta Yana Hana kansa hakura Dan yasan fada tayi indai itace ko fita bazaiyiba saita sake Bata masa Rai sunyi fada.

Hawayen idanuwanta take kokarin saukarwa tana sake basa hakuri take yaji zuciyarsa ta fara saukowa daga fushin sbd duk masifan rashin jinta Neman maganarta basa iya fushi da ita Dan kaman yanda su dadah suka gama sangarta haka Suma Yannan nata sun gama sangartata da kauna me tsananin gaske da dukkanin gidan ake mata Sam Babu me qaunar ganin hawayenta shiyasa idan taso Abu Hawaye take musu saisu kasa riqe fushinsu su watsar.

Harararta yayi Yana daga takarman Dake hannun nasa ya kalla kafin ya dawo da kallansa kanta Yana daidaita murya daga fushin da yayi yace

“Shikenan na hakura Amma kika sake tabamun kaya saina fasa Miki Baki kinsanni sarai.”

Gyada Kai tayi da sauri tana cewa

“Eh bazan sake ba,komai bazan Saka tabawa naka ba saina tambayeka,Amma Dan Allah Yaya Hafiz da gaske baturen Nan zai sake zuwa site din aikinku?

Tsoki Hafiz din yayi Yana fincike hannunsa daga nata Yana wucewa cikin haushin ma Bata lokacinda da yayi Dan ya dauka tuban gaske tayi Ashe sbd me gidansu da shi Yama kasa iya riqe sunansa take magana Wanda Rabon da su gansa anjima sosai Dan tini aikin site din ya tsaya cak Anma Dena project din kwata kwata dukansu an sallamesu Se yanzu ne zaa sake tayarda aikin an mayar dasu aikin masu rabo kuwa har Lagos zaa tafi dasu.

Gefen dakinsu ya nufa ya shanya takarmansa kafin ya shige dakinsu Yana kokarin qarasa shirinsa ya fita abinda yake gabansa.

Ita kuwa juyar da idanuwanta tayi tana juyawa ta koma dakin dadah tana cewa

“Babbah nidai kace Yaya Hafiz koba yau ba idan baka Nan karya Dakar Maka ni,
Nida nakeson auren bature tayaya zai aureni idan akaimun Tambo.”

Batareda babban ya kalletaba Yana fitowa daga dakin yace

“Bama ze fara dukanki ba bare tambon ai yasani sarai,
Yadai samu sa’ar dokarmun ke a Baya yanzu kuwa Babu yanda zaayi Ina kallan tsaleliyar budurwa a gabana Ina jiran ganin aurenta ya dakarmun ita, ko kudi aka basa bazai dakeki ba indai Ina Nan.”

Dadi zancen yayi mata ta juyo tana kallan Dadah data karasa Saka mata zip tana cewa

“Dadah ko Babbah Baya Nan Dan Allah ki ringa tinawa Yaya Hafiz zancen Nan Koda nayi masa lefi”

Miqewa dadah tayi tana nufar gaban tsohuwar madubinta ta dauko turaren Ameenatun dasu Hafiz ke Siya mata Baya taba yankewa tareda duk wani abu da sabuwar budurwa ke buqata kwata kwata basa wasa da lalurarta ko buqatunta sbd tini suka manta da ba uwarsu Daya ubansu Daya da itaba Dan kaunar da suke mata kusan duk Neman da sukeyi Dan inganta rayuwarta ne duk da ta renasu sosai har gwara Yaya Abdul tana girmamasa sosai akan Hafiz data Rena sbd biye mata dayake yi kusan Babu ranar da basa fada tin kafin suyi wanna girman,
Da suka girma kuwa tini suka koma yanzu shiri anjima fada yace Saiya karyata ko balla mata kafafu.

Fesa mata turaren me sanyin kamshi daidai dadah tayi tana dauko mata hijab gogagge kalan kayanta ta miqa mata tana cewa

“Ki Dena shiga sabgarsa tinda Kinga dai bakyason tabo ko Daya a jikinki,
Idan Baki Dena ba ko a hanyar rakaki makaranta Saiya miki dukan ba sanin kowa bare me cetan ki.”

Bata fuska tayi tana qarasa Saka hijabin tace

“Ai Babbah yace ko a waje karya taba masa ni”

Takarmanta dadah ta fitar mata kofar daki tana cewa

“Zo ki tafi kinyi latti sosai”

Jin haka ya Sakata fasa Saka takarman tana dawowa Baya ta dauko wayar Dadah din ta danna Taga karfe Hudu saura mintina kadan ita da ake fara tarewan latti karfe biyu da rabi.

Dadah na ganin ta ajiye wayar tana narke fuska tafara daga murya tana Kiran Hafiz.

“Hafiz fito ka Kaita makarantar ka roqi malam Dan Allah ayi mata hakuri bazata sake latti ba uzuri ne yasakata lattin.”

Hafiz Dake daki Yana Saka kayansa Yana jinsu yayi musu shiru Dan babu hakurin da zaije bawa malam Dan kullum haka takeyi duk ya lalace ya qare a hanyar makarantarta bawa malamai hakuri da uzurin karya Baya hanyar bokonta Baya hanyar islamiya kaman mara aikin yi.

Sake qwala kiransa Dadah tayi yanaji yayi kaman Baya gidan Dan yakai malaman suna ganinsa suke sauya fuska.

Babbah Daya fito bandaki sarai ya hango Hafiz din a daki yace

“Yana jinki Kaita ne bazaiyiba idanma kin takurasa haka zaibi hanya Yana mangaremun yar budurwa Dan haka muje na Kaita da kaina ai mun Saba ba akanta farau latti ba hakama ai uzuri ne,wuce maza muje.

Saka takarmanta tayi ta fito dadah na miqo mata jakarta tana cewa “A dawo lafiya yar budurwan Babbah”

Hafiz Dake kallansu ta window da harara yabi Bayan Ameenatoun Yana cewa

“Duk anbi an sangarta yarinya Bata ganin girman mutane Dan an renasa ace kullum Saiya Rakata makaranta saikace qaramar yarinya,
Duk an ishemu da wata yar budurwan Babbah da Dadah mtseww”

Dadah Dake jinsa cewa tayi

“Idan ka gama yi mana fada ubanmu saika fito ka wuce inda zaka tafi ka dawo da wuri ka biya mata ku dawo tare.”

Yana Jin Hakan ya fito baice komaiba ya fice Yana gyara zaman rigar shaddarsa a jikinsa dan qamshin turarensa me arha na tashi Dan gurin fira zasu gurin budurwansa.

Yana fita Dadah ta bisa da kallan mamaki tana girgiza Kai Dan tasa wannan Doron dayake dagawa Yana qamewa fira zasu.

Yana fita Abdul ya shigo gidan sanye da kayansa na aikin securityn Bankin first bank kadai dayake ta gurarensu.

Gaida Dadah yayi Yana cewa

“Budurwan gidan ta fita ne naji gidan tsit.”

“Taje makaranta Babbah ya tafi Rakata jiya da shekaran jiya bataje ba tana fama da yatsarta datai tintibe Se yau ya Sena mata ciwo ta shirya ta tafi”

Yana Jin Hakan yashigewansa Yana cewa

“Wannan budurwan daya bita da Kun cire mata shi Dan Babu Wanda zaiso ta ahaka Kun gama lalata kayarku”

Banza tayi masa ya shige ya tube ya fito sanyeda da wando dogo ba Riga da kwandon kayan wankansa ya wuce Bandaki bayan ya debi ruwa a bokita Dan Shima wankan zeyi ya fice fira zashi Shima yau din Dan ya kwana biyu Bai ziyarci budurwansa ba.

A hanyar makaranta Saida Babbah ya Siya mata agwaluma cikin bakar leda ta Karba ta Saka jaka suka Isa tana Dan narkewa babban shikuma Yana ganin Hakan ya Bada himmar yiwa malam bayanin rauni taji jinya sukai sosai.

Malam iliya ya Saba da wannan karfin halin na Babbah Dan haka baiyi musu ba yace Allah ya tsare gaba ta wuce aji kawai.

Wucewa tayi Babbah na mata adduar adawo lfy da adduar Allah ya Bata ilimi fiyeda kowa makarantar.

“Amin” tace masa tana wucewa gaba kadan kadan tasake cewa

“Babbah kasa Yaya Hafiz yazo daukan fa”

“Tin kafin a tashi zan korosa”

Dariyar mugunta tayi tana wucewa aji da sauri.

Tana shigowa ajin kawarta ta musamman ta tarbota cikin murna daga Nan sukai gurin zamansu.

Dayake sune manyan makarantar da zasuyi sauka a kwanakin kusa a tacesu shiyasa su kadai ne ajinsu daban Amma sauran makarantar kusan aji Daya suke sedai kowa da karatunsa da ake masa Yana bayarwa ranakun laraba da litinin.

Tin kafin lokacin tashi ya qarasa yi Babbah ya ringa Kiran Hafiz a wayarsa me malatsai Yana cewa yaje ya taho da Ameenatou din.

Hafiz idan akwai abinda yafi zafi da takaici Yana cikinsa Dan kuwa a gaban budurwansa yake babbah keta masa wannan Kiran Dan haka dole yayi sallama da ita ya nufi hanyar makarantar Yana tafe Yana masifa da bacin Rai.

Yana Isa ana tashinsu suka kamo hanyar gida Yana Jin kaman ya mata shegen duka a hanya Amma Yana Hana kansa sbd balain Babbah dazai tarar a gida.

Ita kanta dayake tasan a siqe yake da ita Dan haka ta matso kusa dashi tana fada masa Dan Allah idan zaije fira gobe suje tare Taga matarsa su Saba mana.

Duk yanda zata Saka fushinsa sauka ta sani Dan itace ke kunnasa Kuma ta saukesa Dan haka kafin su Isa gida tini suka shirya fira sukeyi sosai hadda dariya.

Dayake magrib ta matso sosai suna Isa gida Baima shiga ba ya juya ya masallaci dagacan Kuma akwai inda zashi.

MAMUH

AMEENATOU

HOTLOVESTORY

HOTROMANCE

ZAFIN KAI

TWINS

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!

29
Da daddare Bata wani ci abinci ba furan babbah kadai tasha kadan tace batacin abinci ta koshi,

Rakata wanka dadah tayi sbd Bata iya zuwa bandaki ita kadai da daddare sai anrakata Dan haka tana Gamo wanka doguwar Riga kadai ta Saka ta Kwanta bacci Dan Allah yayi mata baccin wuri Dan haka yawanci Se dare Hafiz ke samun cikakkiyar yanci a cikim gidan daga wahalan Ameenatou da takaicinta.

Dakinta shine a tsakiyar nasu Babbah Dana su Yaya Hafiz din sbd duka duka gidan dakuna uku rak sai bandaki da tsakar gida da kitchen dinsu karami.

AMEENATOU BABBAH wadda kusan kowa ya sani da budurwan Babbah kaf wainda ke garin shedu ne Kuma zasu Bada sheda a koina cewan Babu yar gata Kuma sangartacciyar da gata yayi mata yawa a garin kamarta,

Babbah fadan tsananin son dayakewa yar budurwan tasa bama Mai yiyuwa bane,hakama dadah akanta kowa ya sheda yakuma tabbatarda son da ake cewa ana yiwa auta na musamman ne Dan kuwa kauna da banbancin datake nunawa akan Ameenatou daban yake a ranta akan sauran yayan nata.

Su Hafiz kuwa dasuke yannanta sunfi kowa Bata kariya da tattalin tarbiyanta da kiyaye huldodinta da kowa,
Bata zuwa gidan kowa,Bata yawo baa aikenta komai yimata sukeyi,
Tin tana yarinya sune suke Rakata makaranta su daukota haryanxu data zama budurwan datake nanatawa Rakata akeyi makaranta kuma a koma a rakota gida ko Daya daga cikinsu Kokuma Babbah da kansa Wanda duk manyancinsa babu ruwansa zuwa yakeyi takakka idan aka Daketa a makaranta shiyasa kowama ya gaji ya shafa mata lafiya basa dukanta sbd sharia ce da zance Baya karewa har gaban manyan gari Kona makaranta
Babbah Sam Sam Baya yadda da laifin Ameenatou Koda sama da kasa zata hade kuwa Baya yadda da tayi lefi Kuma wani lokacin Yana sane da batada gaskiyar Amma Baya yadda sedai idan sun dawo gida yayi mata fadan kafin ya lallasheta daga baya.

Duk da su bamasu hali bane Suna rufin asiri sbd su Hafiz na aikin karfi hakama babban duk da manyanci sosai Yana Dan babbuga sanaar dabbobin Daya Saba Babu wani samu sosai Amma sbd inganta rayuwan Ameenatou Babu Wanda yayi qasa a gwiwan Nema.

Ameenatou Bata rasa komai ba sbd Tako ina Babu abinda take nema ta rasa,
Tana cikin gata gaba da bayanta hakama har yanzu datake budurwanta batasan basu babbanta ne suka haifeta ba kaman yanda a garin kaf Babu Wanda yasan da Hakan,
Har mamakin akeyi yanda sukeda manyanci sosai Amma sunada qaramar ‘ya sedai Babu Wanda ya taba kawo tinanin basune asalin iyayen nataba duba ma da yanda suke tsananin jinta fiyeda komai.

Ameenatou duk gatanta da sangartan da Akai mata tanada tarbiya sosai Dan kuwa sun Bata kyakkyawar rayuwa su Hafiz musamman Yaya Abdul Basu bari gatan ya lalatata gaba Daya.

Bangaren Bata ilimi kuwa sai inda karfinsu ya kare Dan kuwa makarantar primary ma ta kudi tayi Bata gwamnati ba duk da bawai kudi Basu yawa sosai ba Amma dai private school ce.

Secondary ma Bata gwamnatin takeyiba yanzu tana shekarar gamawa Dan haka daidai gwargwado tanada iliminta kaman su Hafiz din da Suma sunyi karatun bokon Dana Addini kowannensu nada diploma Amma dai Babu wani aikin bare Dora karatu me kyau da amfani sai suke Yan buge bugensu.

A cikin gidan kauna da shaquwa ce sosai a tsakaninsu da barkwanci tin daga kan babban har Dadah dasu Hafiz,
Sosai suke cikin Kwanciyar hankali da farin ciki,
Hafiz da Ameenatou akwai shakuwa da rigima sosai fiyeda Yaya Abdul duk da Shima akwai shaquwan da kauna sosai Amma shi Bata renasa ba kaman yanda ta Rena Hafiz.

Duk inda zata makarantar boko ko islamiya ko wani abin daban basa barinta fita ita kadai shiyasama duk irin shirmen soyayyar da kawayenta keyi ita Bata yi hakama Allah Bai Saka mata shaawan soyayyar da sukeyiba kwata kwata batama ganin kanta a wadda ta Isa fara soyayya.

Akwai masu Sonta da yawa sbd kyau da haskenta tareda gatanta da kyan jikinta Amma suna shakkar tinkararta da maganar soyayya sbd kullum tana tafe da babanta ko yannanta hakama gata kaman Me rariya a Baki koka zagaya kaje makaranta kace kana Sonta tana Isa gida take fadawa yayunta ko Babbah azo ana rantse rantse a gaban me gari ace kana bibiyanta shiyasa kowa ya kama kansa da ita duk da akwai Yan nacin da duk masifar Babbah suna Nan kan bakansu.

Tinda dadewa Yaya Hafiz ya daukota daga makarantar boko ya biya da ita site gurin Hafiz yace tinda lokacin tashinsu yayi ya wuce da ita gida shi gurin aikinsa ana nemansa.

A ranar idanuwanta suka ganar mata kyakkyawar halittar da Bata taba ganin me kyansaba tinda take.

Da farko kasa yadda tayi da mutum ne seda ya tinkaro inda suke sanye da baqaqen kayan dasuka fidda farinsa sosai ga Rana tana haskasa sai wani daukan ido yakeyi duk sai Taga su Yaya Hafiz da sauran ma’aikatan gurin sun koma mata kaman wasu halittun daban ba mutane ba.

Bakinta ta sake tana kallan fuskarsa dake sanye da black sunglasses me shegiyar kyau da fcap akansa Yana magana kaman ranar zata kashesa Dan kuwa alamunsa sun nuna Hakan.

Fitowa tayi daga inda take ta nufi inda yake Kai tsaye Dan kuwa idan ba gabansa ta tsaya tayi masa kallan kurulla ba bazata tantance abinda idanuwanta suka ganiba.

Hafiz ne yayi saurin riqeta daidai tana gap da Isa gabansa Yana cewa

“Ke Ina zakije?

Kwacewa tayi tana cewa

“Yaya Hafiz wannan baturen shine oganku?
Kullum ze Riqa zuwa ne??

Tunkuda keyarta yayi ya maidata inda yace ta jirasa tayi wani Dan qaramin ihun Jin zafi tana cewa

“Tambaya fa nayi Kuma baka ban amsaba ai”

Jin maganar mace a gurin ya Sanya JAMAAL juyowa ya Kalli gurin daidai Hafiz na rufeta da bayansa Yana fuskewa.

Ganin Babu kowa yasashi juyawa Yana ci gaba da sauransu bayanin da ake masa ita kuma ta fito tana cewa

“Bazanyi magana ba kallansa kawai zan riqa yi” ta Dora hannunta Daya a bakinta tana zubawa Jamaal din idanuwanta masu haske da kyau tareda yin shiru.

Sautin muryansa me tsananin nutsuwa da kamewa acikine Taji Yana magana Rabi duk turanci Wanda ita bama irinsa malamansu keyiba dasu kansu Dan Wanda suka iya.

Tinda tafara kallansa tana Jin muryansa Yana magana Bata qara motsi ba har Saida ya gama ya juya yabar gurin Bata motsaba sai murmushi takeyi.

Hafiz Daya gama aka sallamesu sbd maigidan nasu Daya wuce kama hannunta yayi yaja suka bar gurin Saida sukai Nisa ta kwace hannunta tana matsowa kusa dashi sosai tace

“Yaya Hafiz Yaya sunansa?
Bature ne ko balarabe?

Suna Isa gida ta bawa babba da dadah labarin Taga irin Wanda zasu Nemo mata a matsayin miji idan zasu mata aure.

Tin daga wannan ranar Ameenatou Babu ranar da Bata maganar baturen ogansu Yaya Hafiz,
Kaf gidan saida suka gaji da Jin kalan kyansa datake fadan kaman Rana zata konasa yanata kyalli.

Haka zalika tin daga lokacin Yaya Abdul ko Babbah suna daukota daga makaranta gurin Hafiz suke ajiyeta shikuma daga Nan yaje da ita gida duk Dan sbd tagansa Amma kuma abin mamaki tin daga ranar Bai sake zuwa ba bare ma ta gansa daga qarshema sai gashi anrufe site din gaba Daya tareda aikin dole suka koma Neman wasu ayyukan kafin idan Allah yasa zaa dawo da aikin sai gashi kuwa kwatsam ance su shirya su koma bakin aikinsu Kuma me gidanma yananan tafe da kansa.

MAMUH

AMEENATOU

THE SEELAHS

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!

30
Washe gari Tin 7 na safe Yaya Abdul ya shirya fita aiki ya tsaya jiran Budurwar babban Amma dai lokacin ma dadah ke tadata bacci cikin lallabawa da tausayinta akan tashin safen Wanda yake kular da Hafiz Dake tsakar gidan Yana wankin kayansa Dana Ameenatou din.

Brush tafara kafin Tayo wanka ta fito ta nufi daki Dadah haryanxu data girma tayata shiri takeyi.

Sai kusan takwas saura ta gama shiryawa ta fito tsakar gidan ta zauna gefen Babbah dake zaune kan tabarma.

Farin Koko me kyau da aka zuba mata zuma aciki ta dauka a cup da fanke manya manya da zafinsu sun soyu tafara Sha tana fadawa Babbah gobe bazata je makaranta ba duk idanuwanta rage girma sukeyi Bata samun bacci gashi da Rana ma Bata samu.

Cikin kulawa da yadda da abinda ta fada din Babbah ya gyada Kai Yana cewa

“Na lura da Hakan sarai ‘yar budurwata magana ce kawai banba sbd Yan Saka idon gidan Nan Amma gobe Babu inda Zaki ai ana son Rai da hutawa”

Juyowa Hafiz yayi sbd ya Dena mamakin lamarin babbah da budurwan tasa Amma takaici Baya barinsa yin shiru Dan haka Baki sake yace

“Wlh duk ranar da kika sake tsallaken zuwa makaranta bazaki sake zuwa site ba ko oga yafara zuwa aiki kuwa,
Sai naga karshen rashin bacci.”

Kallan babbah ta dago tayi da idanuwanta da suka narke tana masa alaman yayi magana.

Inda yake babbah ya juya ya kalla Yana jifansa da wani mugun kallo yace

“Nine nace bazata goben ba sai naga abinda zakayi”

Yaya Abdul da hakurinsa ya fara karewa sbd yayi masifan lattin Danma Babu ranar da Baya latti sbd ita cikin kulewa yace

“Zan tafiyata idan Baki nutsu kin gama abinda yake gabanki ba Kokuma ki tashi mu tafi hakanan Baki gama cin abincin ba.”

Dadah Daketa Kaida kawon hada mata jakarta da ruwanta a sabuwar roban ruwa me tsafta sosai da Yaya Abdul ya sake siyo mata miqawa Abdul din dayake tsaye Yana harare harare tayi tana cewa

“Dan taimaka riqe mata kafin ku Isa”

Baida lokacin batawa na musu Dan haka ya karba kawai zai sake magana Dadah ta rigasa da cewa

“Yi hkr saura kadan fa ta gama karta qware duk Kuna Neman rikitata”

Hafiz ajiye wankinsa yayi Yana nufota Babbah ya jefesa da wani kallan daya sakashi tsayawa Yana cewa

“Babbah wai meyasa kakemun hakane duk lokacinda naso gyarawa wannan yarinyar zama duk ta renani ko abokaina fa sunsan ta renani a gabansu Babu kalan sakarcin da batamin gudun nakeyi wataran na harzika na babbalata jinin mutane yayita Hawa”

“Karka wani Sakaya fito fili kace jinina Dana uwarku ya hau,
Zaka koma aikin gabanka kokuwa saina ce Abdul din ya tafiyarsa ka aje wankin ka Kaita”

Ball yayi da takarmanta Dake gabansa Yana juyawa ya koma aikinsa Dan ba qaramin aikinsu Babbah dinne ba ace ya aje wankinsa ko wanka beyiba ya Rakata makarantar.

Miqewa tsaye tayi bayan ta gama tana goge bakinta da tsaftacciyar kyallen sabuwar atampa da Dadah ta miqo mata ta Saka takarmanta masu kyau Wanda suka Hafiz dinne ya siyo mata Dan komai nata Hafiz da Yaya Abdul ne ke Siya
Babba kuwa a siya mata kayan ciye ciye da kwalama Yan canjinsa suke karewa sai fura da asalin Madaran fulani me kyau dayake siyo mata duk dare Wanda yawanci ita take Sha Bata cika cin abinci ba sai idan Yaya Abdul ya siyo mata kwai zuwa makaranta take ci da dare.

Suna fita tana gefensa tana masa surutu suka kama hanyar makarantar Yana amsata sama sama sbd hankalinsa na kan gurin aikinsa dayayi latti gashi Basu yadda da kowaba akanta da tini mashin zai ringa Bata kudi tana Hawa Amma kwata kwata Basu yadda da kowaba akanta shiyasa duk tsananin latti da rashin jinta basa iya barinta taje ita kadai makaranta kuma itama kanta sbd sabo da Hakan Bata iya tafiya koina batareda dayansu ya Kaita ba tsoro ma takeji na bin hanya ita kadai.

Suna Isa gate din makarantar ya miqa mata kayan ciye ciyen Daya Siya mata na break Dan basa Bata kudi kwata kwata.

Karba tayi tana masa Godia da fuska a cakude sbd lattin datai tasan Kuma Yaya Abdul din Babu rokon dazaije yayi mata Dan haka ta juya ta shige tana ciko idanuwa da hawaye Dan a tausaya mata.

Cikin babbar sa’arta malamin data tarar Yana Taron lattin Baya ko kallan inda take kwata kwata sbd tashin hankalin Daya taba Sha shida Babbah da Hafiz akan dukanta Daya taba yi
Babbah yazo makarantar ya rufe ido ya zuba musu tsiya rigima har gaban shugaban makarantar kawu yayi mirsisi ya nuna Yar budewarsa Bata da laifi shine Babu lafiya shiyasa batazo da wuri ba.

Dayake sunsan ba yadda zeyiba daga Nan har hukuma Dan haka suka basa hakuri aka rufe maganar,

Tin daga lokacin da yawa malamai basa taba Ameenatoun sbd Babu me buqatan rigima kowa na fama da kansa.

Simi Simi kaman munafuka ta wuce ciki tana Jin dadi a zuciyarta Dan idan akwai abinda ta tsana a duniya shine a taba lafiyar jikinta,
Bata kaunar abinda ya taba jikinta shiyasa Sam batason duka ko faduwa bare Jin ciwo.

Idan kuwa taji ciwo a gidan jinya zata kwanta a ringa fama,kafin ta warke zuciyar Hafiz saita kumbura ta huce yafi so a kirga sbd yanafin kowa Shan wuya da takaici Dan a kansa sakarcin yake karewa.

Farin jini datake dashine ya Saka yakeda kawaye masu tsananin son binta koina Amma da Aminiyarta Daya Khadija.

Karfe biyu saura Yaya Abdul yazo ya dauketa Kai tsaye gida suka nufa ko shiga beyiba ya juya ya koma gurin aikinsa ita Kuma ta shige a gajiye duk da Yaya Abdul din ya Siya mata yoghurt me sanyi sosai yazo mata dashi Amma dai batasha ba tana shigowa ta miqawa Dadah hadda Jakarta da komai ta tube a tsakar gidan ta daura zani ta nufi bandaki Tayo wanka tana fitowa abinci kawai taci Tayi sallah ta share dakinta dana Dadah duk da fes suke Dan Dadah akwai tsafta.

Tana gamawa bacci kawai ta kwanta abinta.
Sai kusan hudu ta tashi tayi Shirin makaranta dayake Hafiz yasan lokacin gama shirinta tana gamawa Yana dawowa yace ta fito su tafi yakaita sauri yakeyi akwai inda zashi.

Tin a cikin gidan suka fara rigima har suka Isa ta shige ya juya ya wuce inda zashi.

Da yamma kuwa babbah ne ya biya mata suka dawo gida tare Yana Bata labarin inda yaje da abinda ya Gani tanata Jin dadi.

Da daddare yau kusan kowa Yana gida lokaci Daya sukaci abinci su a tsakar gidan tanata zuba shagwabarta yanda takeso a cikin iyayenta da yannanta.


Zaune yake a gaban Dad dinsa jikinsa gabaki Daya a mace,
Daga shi har Dad da Dad Lameenu dasuke palon su a zaune Babu me walwala ko farin ciki ko kadan a zuciya da fuskokinsu,

Tarin bacin Rai da baqin ciki ne yake sake tirnike zuciyar kowannensu Yana Kona jininsu.

Dad Lameenu dayake Jin kwata kwata baiga amfanin Haroon a rayuwarsu ba sbd Babu inda suka Kara gaba kullum sai Baya sukeyi suna Neman durkushewa ba shiri,

Rashin JAMAAL a rayuwarsu wani babbar balai da masifa ne Dan kuwa sun sheda Hakan Kuma suna kan shedawa tin daga ranar Daya barsu komai sai rushe musu yakeyi,

Shi baimaga dalilin wani Yanke yanken alaqa ba da Mam yayi da Jamaal din dan kuwa da Haroon din ya miqawa Dr Aleena can taje dashi tayita kayan rashin amfanin dashi.

Mam kasa cewa komai yayi sbd yanason ya kasawa ransa iya danne tsananin rashin ‘dansa JAMAAL a taredashi,
Yanason ya Hana abinda yake cin zuciyarsa gameda rashin Dansa,

A tsawon shekarun Nan da suka diba basa tare Babu ranar da Baya kwana ya tashi da tsananin son kasancewa da JAMAAL,
Babu ranar da Baya kewansa,
Babu ranar da Baya baqin cikin faduwa da rushewan da sukeyi sbd rashinsa.

Kallan Haroon ya sake yi Yana ajiye takardun hannunsa Daya gama karantawa y
Zuciyarsa na quna yace

“Se yaushe ne zaka zama me amfanin dazanyi alfahari dakai amatsayin Dana?
Kasan irin millions din da muke rasawa akowace safiya tindaga ranar da Jamaal ya tafi kuwa??

Zaka iya lissafa asara da faduwan da muketa yi kullum?

Menene yake faruwa acikin kanka ne da kwata kwata Babu Abu Daya a cikin lamuranmu dayake tafiya daidai?

Aikin site dincan a yanzu shi kadai ne abinda ya rage a tayar shine abinda zai hanamu karasa rugujewa sbd ka lalata komai,
Ka rusa abinda mukai aiki tukuru da jini da majina muka hada,
Ka rusa abinda Dan uwanka yayi aiki dare da Rana ya hada duk kana Neman lalata komai a cikin shekaru kalilan.”

Dad Lameenu kuwa kasa magana yayi sbd Jan da idanuwansa sukai zuciyarsa na quna cikin baqin ciki da tashin hankali.

Har abada bazasu hada Haroon da Jamaal ba sbd Jamaal zakin namiji ne da kosu suke shakkarsa,

Ga Haroon yau ya Sakasu a tsaka me wuya sbd Bai iya komaiba sai rusasu yakeyi da rashin amfaninsa.

Cikin zafin zuciyar Dad yace

“Ka tafi ka fara Shirin tafiya wancan babban project din,
Abu Daya nakeso ka sani,
Wannan aikin shine aikin dana Saka dukkanin burina akansa yanzu
Samun matsala akan wannan aikin shine rugujewanmu gaba Daya Dan haka ko rayuwa nawa zaa ci a aikin Nan banason ka tinkaroni da matsala duk tsanani duk rintsi,

Ka nutsu dakyau ka fahimci mahimmanci wannan aikin a gurinmu,
Ka tafi kasan abinda kakeyi idanma haryanxu rabuwarka da Dan uwankane ta kasa sakinka to ka sani wannan Karan a shirye nake da kawar da matsalata kowace iri ce.”

Wani abu me dacin gaske Haroon ya hadiye kansa da kirjinsa na wani irin nauyi da radadin dayake cikinsa na tsawon shekarun Nan,

Tinda Jamaal ya rabu da Dad Bai sake sanin farin ciki ko samun kauna daga mahaifinsa ba Kona Rana Daya ne,

Shi kansa ya sani baida jarumta ko ilimin aiki irin wanna da Kuma izzar gudanar da manyan huldodin kasuwanciba irin Jamaal,

Baida sa’a kaman Jamaal,
Baida cika ido da kwarjinin kasuwanci acikin manyan mutane na gida Dana waje kamar Jamaal

Rayuwarsa gaba dayanta akan abinda ya karanta ya kwallafa ta sedai Kuma babbar jarabansa itace kauna da son kyautatawa mahaifinsa Daya rufe masa zuciya da ido Amma duk yanda yake kokari Dan zama hasken idaniyar Dad din Hakan Bai taba samuwa ba saima lalacewa da komai yakeyi.
Baya tareda mahaifiyarsa,Baya tareda Dan uwansa Baya da kowa sai mahaifinsa da sauran dangin seelahs da duk Babu Wanda yake appreciating nasa ta koina da komai sai Hakan yafara tabasa ahankali ahankali har depression na shigarsa batareda kowa ya sani ba bare fahimta.

A yanzu da shine komai na Seelahs yadawo hannunsa shine yake juyata Babu abinda Bai saniba na sirrinsu Dad sedai bazai taba iya fadawa Dan uwansa Hakan ba,

Bai iya illegal huldodinsu ba,
Bai iya juya business na Seelahs ba na bayyane Dan haka gaba Daya rayuwarsa ta tashi daga Haroon seelahs Takoma wani mutumin daban dabai San kowanne farin ciki ba bare walwala sbd haryanxu Babu abinda yakeso kaman burge mahaifinsa ya samu yabo da alfahari daga garesa.

Wannan aikin na site a yanzu shine abinda zai basa Daman samun yabo da kauna daga Dad dinsa yanda yake buri Dan haka yayi alkawari tareda sakawa ransa zaiyi aiki tuquri akan wannan project din.
Shiri ya fara na tafiya Nasarawa tareda sakawa Akai masa booking na hotel da komai.

MAMUH

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!

31
Bayan ficewan Haroon daga palon kallan Mam Dad Lameenu yayi cikin nauyin zuciya da rashin Jin dadin komai na duniya yace

“Dole muna buqatan tsananta binciken abinda àka haifawa Omar duk inda yake sbd sanin inda suke zai Saka Omar din dawowa daga inda yake ya dawo cikinmu sbd sanin munsan yanada ‘da a duniya,

Idan ba Hakan mukaiba cikin gaggawa wlh muna gap da rasa komai munaji muna Gani Dan haka yanzu Kam dole mu tashi tsaye dakyau mu samo ‘dan Omar”

Mam da zuciyarsa tafi ta lameenu tsananta a cikin baqin ciki da tafasa tareda bacin Rai baice komaiba sbd Daman ya hangowa kansu Hakan daga ranar da suka Dora Haroon akan komai nasu,
Sam baida jarumta ko amfanin da zai musu yanda ya kamata.

Ta bangare Daya yasan duk Wanda zasu Saka a magajin nasu me gudanar da komai bazasu taba samun Jamaal ba Dan kuwa shi din zakinsu ne.

Numfashi ya sauke ahankali Yana kallan takardun gabansa da idanuwansa da sukai jajir Yana kokarin daidaita tafasar da zuciyarsa keyi,
A yanzu shima Babu abinda ruhi da zuciyarsa suke tsananin buqata kaman dukiyar Omar Dan ita kadaice zasu mallaka suyi tsayuwarda Babu ranar rushewansu a kusa sbd koba komai a tsaftace take Babu jinin kowa aciki Dan haka zeyi wuya ta shiga hannunsu ta lalace kaman yanda tasu ta dauko hanyar lalacewa duk Dan sbd Allah ya basa sakaran ‘da mara amfani sosai duk da Yana son dansa sosai Amma Sam Baya kaunar rashin amfaninsa har ransa yake Jin baqin ciki da tsanar Hakan.

Wayarsa ya miqa hannunsa Daya ya dauka cikin nutsuwa ya Nemo numbern BB ya Saka kira Yana dauka yace

“Ina buqatan ganinka yanzu”

“Yes Sir” ya fada Yana zare sigarin Dake bakinsa Yana zuqa cikin palon gidansa.

Cikin mintinan da Basu wuce hamsin da Yan Kai ba saigashi ya iso gidan Kai tsaye motarsa yayi parking ya nufi hanyar office dinsu Yana zare baqin glass dinsa Dake rufawa jajayen idanuwansa masu Bada tsoro asiri.

Yana shigowa ya rufe kofar tareda qarasawa ya tsaya gabansu cikin girmamawa da kulawa ya gaidasu Yana kallan fuskokinsu ya sheda akwai sabon bacin Rai da sabuwar matsala wadda kwanan wani zai qare Kila a kwanakin Dan kuwa Kai tsaye yake gane girman bacin ran uwayen gidan nasa.

Kallansa lameenu yayi cikin tashin hankali da son danne tafasar zuciyarsa yace

“Yaya ake ciki a bincikenmu??

Gyara tsayuwa yayi Yana dagowa yace

“Ranka ya Dade tsawon shekarun Nan wlh bamu taba dakatawa daga binciken inda suke ba,
Babu kalar yawon da bamuyiba state state da kauyuka gurin nemansu,
Acan Asalin kauyen na iyayen matar sir Omar din muntashi kauyen gaba Daya Dan kunasa mukayi da gidajen Dake cikinsa dayawansu ma Babu sun mutu,
Hakama itama me aikin munyi nasarar sanin inda aka daukota aiki daga Jos Amma bamu gama sanin a inane take a jos din…….

Cikin daga murya da bacin ran da suke jimawa Basu ganiba a gun Mam ya katsesa idanuwansa na qara yin jajir yace

“Ko nawa zaa kashe a kashe a Nemo mana matarnan Ina buqatan Jin komai daga bakinta zuwa kunnuwana,
A yanzu wannan aikin shine tabbatuwar arzikinmu da tsayuwarmu,
Samun wannan matar shine duk wani abu damuke buqata da ranmu da zuciyarmu,
Omar jeden Yana kallanmu daga nesa amatsayin matsiyata wainda ya take ya wuce nesa ba kusa Dan haka nakeson nuna masa Munfi karfinsa da gaske shi din a tafin hannunmu yake Dan kuwa idan ban zubar da jinin ‘dansa ba bazan taba Ji ko samun nutsuwan zuciya ba..”

Lameenu dakejin zuciyarsa har wani rawa da tsallen tashin hankali takeyi sbd Jin inama zasu samu ganin matar da Gano komai a ranar da hannunsa zai cike aikinsa dabai qarasa ba Dan kuwa barin ‘dan Omar a duniya kaman aikine da Basu samu cikawaba Wanda bazai taba samun nutsuwa ba idan ba cike aikin yayi ba daidai.

Cikin sauti me tattareda radadi da son samun abinda zuciya keso Dad Lameenu yace

“Ko nawa zaa kashe a kashe acika wannan aikin Daya gagara cikuwa shekara da shekaru,
Duk Wanda yasan wani abu gameda me aikin gidan Omar a nemesa aji nasa bayanin a Kuma kawar dashi bayan karban bayanan Dan basason barin sheda ko Daya datasan meyake faruwa Da abinda ma zai farun.

BB da Shima daya kawar da rayuka sunkai nawa akan wannan binciken Jin yayi zuciyarsa ta sake daukan zafi Dan rashin sauki ko kadan Dan haka Koda zasu tada kauyuka da rayuka nawa wannan Karan Se sun Nemo inda matar Nan take sunji me aka haifawa Omar din da inda abinda aka haifa din yake.

Kudi masu yawan gaske Dad Lameenu ya kira Haroon ya bawa BB da yaransa akan aikin Nemo matar wadda Shima Haroon yake tsananin so da buqatan a Gani din duk da Yana Jin shakkar abinda zai iya biyowa bayan samun me aikin da Kuma samun Abinda Dad Omar ya Haifa, duk da haka Shima Yana Nan Yana bincikensa sosai a boye sbd zaiso yasamo information da zai taimaki Dad dinsa Dan ya yaba masa Koda so Daya ne Kuma yayi alkawarin Yana samun Information koman kankantarsa zai sanarwa Dad din.

Bayan bawa lameenu kudin sanar dashi yayi duk information da zaa samu Shima ya sanar dashi ko yayane.

“Angama Barrister” BB ya fada Yana ficewa daga palon Haroon din zuciyarsa cikeda rashin Imani da Jin ya dauki sabon caji Baji ba Gani yayiwa kansa alkawarin Nemo matar Nan duk inda take a cikin Jos da zagayenta.

***Anyi Hakan da kwana biyu Haroon ya tattara ya tafi Nasarawa sbd gaba Daya Dad ko kallan daraja Baya masa sbd tsananin bacin Ran dasuke ciki akansa Dan haka ya sake shiga damuwa sosai da rashin walwala duk da Bai bari Mum dinsa da Dan uwansa dashi kadai suke communicating a Nigeria sai siddeeq da duk motsin Haroon Yana sane dashi Yana sanarwa Jamaal Dan kuwa kwata kwata Jamaal Bai yadda dasu Dad din akan Dan uwansa ba.

Duk tsananin damuwa da kadaici da rashin mutuntawa ko daraja da Haroon din yake cikinsu Jamaal Yana sane da komai sbd Yana sane ya saka Haroon daukan siddeeq Aiki ya zama Dan hannun damarsa batareda su Dad sunsan asalin waye Siddeeq dinba hakama Haroon kansa baisan ma siddeeq din yanada alaqa haryanxu da Jamaal ba sbd kwata kwata abinda ya sani dashi kadai Jamaal ke magana a Nigeria Dan ko mum Atee duk nacinta ta gaji ta barsa Dan ko kwana zatayi tana kiransa Bata samunsa.

Koda ya karbi aikin project dinnan zuciyarsa cikin shakku da fargaba take sosai tareda tsananin tsoro Dan baisanma ta inda zai fara gudanar da wannan aikin da Dad ya basa damar karshe akansa ba,
Baisan Yaya zai fara ba gashi baisan ta Ina zai fara rokon taimakawan Jamaal ba Dan yasan Jamaal din bazai taba Saka hannu a aikinsu Dad ba Dan haka yake cikin damuwanda tini tafara taba ayyukansa da rayuwarsa Dan kuwa komaima kaman ya Dena ganewa daidai.

Tareda siddeeq suka sauka Nasarawa har babban hotel din da Aka kama masa motar data daukesa ta Kaisa.

Siddeeq ne yakai masa kayansa har dakinsa ya jere masa kafin ya fito ya nufi nasa dakin dayake kusa da nasa Shima ya jere kayansa ya fada toilet sbd zasuyi kwanakin da basusan yaushe ne ranar tafiyansu ba tukuna.

Shi kansa Haroon wankan yayi Yana fitowa ya shirya cikin kaya marasa nauyi yayi Sallah kafin ya kunna wayarsa sai alokacin ya kira Dad ya sanar masa sun iso.

Babu wani yabawa Dad din ya sake maimaita masa mahimmanci da tsananin buri dasuke dashi Akan aikin Nan tareda tabbatar masa da idan aka samu matsala to babusa Babu shi.

Wannan kalman itace kalma mafi Munin data girgiza zuciyarsa ta qarasa tarwatsa duk wani Dan sauran dubaru Dan kokarin Daya rage masa Dan haka ya sake shiga damuwa da tashin hankali me tsananin gaske gashi bayajin zai iya ajiye aikin Dan kaman nauyi ne Daya rataya akansa hakama bayajin Dad din ze barsa ya ajiye din Dan.

Jin yayi ciwonsa na tsananin ciwon Kai da depression na dawo masa sosai Dan kuwa take yafara Jin kaman kansa ze juye Baya gane komai,

Wayarsa ya kashe tareda wurgi da ita Yana silalewa qasa hannuwansa riqe da kansa Dake Neman bugawa tareda bugun zuciyarsa.

Maganinsa yafara rarrafawa Dan nemowa yasha amma kwata kwata Baya Gani daidai saima juyawa dayaji kaman anayi dashi,
Hannuwansa Dake wani Irin rawa sosai suna kakkarwa ya dago Yana kalla sunai masa bibbiyu.

Sake rarrafawa yakeyi Yana faduwa Yana tashi harya Isa gaban mirror inda siddeeq ya ajiye masa maganinsa kafin yakai hannunsa ya dauka ya Fadi akan mirror din kayan Dake Kai suka zube qasa Wanda sautin ya Isa har dakin siddeeq Dake maqale da nasa da sauri ya fito ya shigo dakin Yana ganin Halinda yake ciki da sauri ya qaraso Yana daukan maganin ya Bude roban ya Ciro Daya ya Saka masa a Baki tareda dauko ruwan Roba a fridge ya basa.

Yana shanye magana ko mintina uku beyiba sai gashi ya fara dawowa daidai Yana hada zufa idanuwansa nayin jajir.

Boyayyar ajiyan zuciya me zafi siddeeq ya sauke Yana kallan Haroon dan kuwa da Baya kusa wani abin ya samesa baisan me zaicewa JEEY ba.

Miqewa Haroon din yayi da kansa Yana kasa kallan siddeeq ya Bude Baki ahankali ya furta

“Thank you”

Kujera ya nufa ya zauna ahankali har lokacin zufa yake tsiyayowa ya dauki tissue Dake gabansa aje Yana Dan gogewa kadan.

MAMUH

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!

32
Abinci siddeeq yayi order tareda abubuwan dayasan Haroon zai buqata kafin ya fice ya koma dakinsa Dan sanarda JEEY ciwon Haroon gaba yakeyi sosai.

Bai samu wayar JEEY a lokacin ba Dan haka Shima abincin yaci kafin ya kira manyan ma’aikatansu da zasuyi Aiki dasu Dan Yana buqatan fara zuwa site din yaga komai ya gana da tarin ma’aikatansu masu yawan gaske kusan shine zai karbi Ragamar Aikin sbd Haroon Babu abinda zai iya.

Su Hafiz da suka shirya tsaf washe gari tinda safe suka halarci site cikin farin cikin dawowansu bakin aikinsu Dan suna samu sosai a aikin.

Kusan ma’aikata sama da hamsin Dana garin da wainda da yawansu daga wasu garin suke zuwa, manyan kuwa daga Lagos wasu suka taho wasu Kuma daga Abuja Dan haka tini site ya rayu ya cika da leburorinsu da masu kulawa dasu da masu tsari da Zanen.

Lafiyayyar tanti aka kafawa oga kwata kwata Haroon seelah da kujeran zamansa da table da duk abubuwan da zai Dan buqata a zaman da zai ringa yi idan yazo site din.

Siddeeq dayake sosai yakeda nasa ilimin da qwazon aiki tareda dubaru irin wainda duk ya koya a karkashin maigidansa na Amana JEEY Dan haka tinda suka taho shine yake fitowa site din ya gana da ma’aikata da abokan aikinsu na project din suka sake Bude sabon bayani tareda gabatar da kansu da ayyukansu tini aka fara aiki Babu wasa sbd kowa da gaskensa yake.

Saida aka kwana biyu Haroon ya koma daidai kafin ya fara fitowa site aiki zuciyarsa cikeda fatan samun nasarar abinda sukeso
Ta bangare Daya Kuma ya tsananta bincikensa akan Abinda su Dad suka Hana kansu zama da tsayi gurin nema sbd ya samo information me amfani dazai Hana Dad yafesa idan aka samu matsala a wannan aikin.

***Yar Budurwan Babbah kuwa kusan tafi su Hafiz shiga farin cikin komawansu aiki Dan kuwa tasan baturenta zata sake Gani Wanda kamanninsa suke Zane daram a idanuwa da zuciyarta Dan haka ta daga hankalin babbah da Dadah Saida suka Saka Abdul ya Dinka mata sabon uniform duk da a shekarar zata kammala Amma sbd rigima Saida aka Dinka mata sabbin uniform din.

Shi kansa Babbah da Dadah akan dole suka ringa farin cikin komawansu Hafiz aikin site sbd Ameenatoun data sakasu nuna murnan dolen.

Da daddare bayan Yaya Abdul ya shigo mata da sabbin uniform din a leda me kyau ya miqa mata Yana cewa

“Wlh safar banza ma bazan Kara Siya Miki ba sbd bansan uban me zakiyi dasu ba keda duka duka baifi wata uku ba zuwa hudu ki kammala karatun Amma shine tsaban an renamun da wayo zaa sakani dinko sabon uniform.”

Hafiz Daya fito wanka Ya gama shafa Mai Yana gyara kansa da brush na brushing Kai yace

“Kafin ma aje can ka fada mata yanda ka dinko sabon uniform dinnan tana faduwa jarabawa da su zataci bikin sallah Dan Babu uban dazai mata Dinkin sallah da f9 duk cikeda takarda….”

Babbah Dake shigowa ne ya katsesa da cewa

“Ubanta ne zai Dinka mata basai kaja da Nisa ba,
Kuma faduwa jarabawan ma ai rabo ne tinda yafi Babu…

Cikin narke fuska tana kokarin ciko idanuwanta da Hawaye tace

“Babbah to ai na Maka alkawarin bazan Fadi bafa ka gaya masa,
Kuma ni Allah wanna sallan shi kadai ma nakeso yamun komai tinda ya koma aikin site…

Wurgi yayi da Brush din hannunsa Yana yowa kanta yace

“Bazaki Dena renani ba ko?
Na rantse a gidan Nan kika kawo faduwan jarabawa silipas bazan Siyaba na sallanki sedai duk me Shure…..

Katsesa dadah tayi da cewa

“Babu me shurewa Dan bakayiba.”

“Ai da kin bari ya qarasa da bakinsa Muji waye ze Shure din” inji Babbah Yana karban ledan hannun Ameenatou datake nuna masa kayan babu guga.

Miqawa Hafiz kayan yayi Yana cewa Maza gama shiryawa ka goge mata ko a shagon abokincan naka me dinki ne.

Kallan ledan kayan yayi Yana sake Jin takaici na siqesa ya juya ya kalli inda Yaya Abdul yake zaune Yafara cin abincinsa hankali kwance yace

“Dena kallona Dan kasan Babu inda zani guga yanzu Kaine me abokai masu shagunan dinki”

Kanta ya dawo da kallansa zeyi magana Dadah ta bisa da rarrashinda yasan anriga an cucesa ne ake toshe masa Baki.

Jinjina Kai yayi Dan zata shiga hannunsa ne gobe tinda shine zai daukota makaranta.

Wucewa yayi daki ya qarasa shiryawa ya fito baicewa kowa komaiba ya fice Yana jinta tana masa a dawo lafiya itada Dadah yayi musu shiru ya fice Dan wankan dayayi fita zashi aka sakashi zuwa guga duk yaje ya sake hado gumi duk da Daman shine mai yi mata guga Amma dai yau din ba lokacin yinsa bane.

Bayan fitarsa Abdul ne ya fara yiwa Ameenatou din fada Babbah ya dakatar dashi da cewa yabar zancen Nan tinda dai ba fandarewa yarinyar Nan tayi na.

Da daddaren kafin ta kwanta Saida ta Jira Hafiz din ya dawo sukai karatu dayake sake nuna mata abubuwan da Bata ganeba
Anan dai ya shiririce firar da Bai tafi ba kenan.

Washe gari Abdul ne yakaita makaranta ya wuce aikinsa daga can.

Karfe biyu saura Hafiz ya iso makarantar cikin sauri sbd aikinsa Daya baro ya taho yakaita gida ya koma.

Tana ganin sun kama hanyar gida ta riqe hannunsa tana narkewa tana rokonsa suje site tinda zeyi latti kafin ya dawo kuma ai uku suke tashi Dan haka bama wani Jira zataiba zai gama su wuce gida.

Yana Jin Hakan yasan wa takeson Gani Kuma cikin sa’arta maigidan nasu Yana Nan kaman yanda ta Saka masa suna bature Suma gurin tinda dadewa suka Saka masa suna baturen.

Kaman bazaije da itaba sbd ba gurin zuwan mata bane idan ba irin masu tallan nan ba duk da an dauki nauyin abincinsu acan ake basu abinci tin farkon aikinsu Amma dai yanzu tinda aka dawo dinnan baa fara Basu ba hakanan suke siyan na masu Siya shi Kam dai iyakacinsa ruwa Basa cin abincin siyarwa waje.

Kallanta Yayi Yanajin kaman bazai tafi da ita ba Amma mum matsalarsu shine Bata iya rokon Abu su kasa Bata shi Dan haka yace

“Muje Amma tattara aikina zanyi na ajiye mu dawo gida sai gobe na Dora.”

Wani kyakkyawar murmushin daya lotsa simple dinta sosai ta sake tana Jin dadi tace “Eh na yadda Yaya Hafiz dina Rabin Raina”

Harararta yayi Yana yin gaba tana biyosa tareda miqa masa Jakarta ya karba Yana kallan fuskanta kafin ya kalli ranar da ake qwalawa yasan zeyi wuya batai zazzabi ba idan ta Dade a cikin Rana Dan haka kudin aljihunsa ya taba ya ciro yaga nawa ne.
Wani shago ya tsaya ya shirya umbrella ya Bude mata yana miqa mata.

Karba tayi murmushin tsananin kaunar yayan nata datakejin sonsu fiyeda yanda suke jinta kawai dai Bata iya zama basuyi rigima ne ba Amma tasan kaunarta a zuciyoyin iyayenta da yannanta bame misaltuwa bace.

Bata tafiyan sauri Dan haka a natse suka iso site din ya Kaita inda ya Saba cewa ta zauna ta jirasa yace ta zauna ta jirasa din.

Tinda suka iso gurin taji zuciyarta tayi wani irin sanyi da farin ciki Mai nutsuwa lokaci Daya ta rasa wane irin yanayi ne ma takeji akan wannan kyakkyawan baturen Daya fita idanuwa da zuciyarta.

Zaunawa take kokarin yi a inda Hafiz ya goge mata ya wuce idanuwanta sukai kyakkyawar sauka akan Haroon Daya tinkaro inda take Kai tsaye siddeeq na gefensa Yana duba wasu takardu hakama wasu ma’aikatan na biye dashi.

Sanye yake Dan kananun kaya Ash Shima da fcap a kansa sedai Babu sunglasses a fuskansa.

Kasa zama tayi ta tsaya cak tareda zuba masa fararen idanuwansa tana Jin farin ciki na dabaibaiyeta sedai Kuma idanuwanta sai suke ganin sauye sauye a tattareda shi duk da ta Dade sosai Bata gansaba.

Kyakkyawar fuskarsa da batai hasken ta Jamaal ba ta zubawa dukkanin fararen idanuwanta tana kallan mamakinta na qaruwa zuciyarta na sake hasko kamanninsa na Baya da suka tsaya tsaf a cikin idanuwanta.

Wayar dake hannunsa ce tayi ringing Yana gap da isowa inda take ya dakata tareda dago wayar Yana ganin sunan Wanda yake Kai ya daga Kai tsaye Yana ambatar sunansa cikin sautin nutsuwa da turancinsa me dadi Shima.

Lumshe fararen idanuwanta tayi ahankali lokacinda take Jin sauyin a sautin muryansa ma,

Bude idanuwanta tayi tana sake Dorasu akansa muryansa na sake ratsa jinta,

Idanuwanta da kunnuwanta sun tabbatar mata da sauyin abubuwa akansa sedai a zuciyarta shi din daine takeson Gani da Kuma ji Dan haka sai alokacin ta saki wani kyakkyawar murmushin daya sakata Jin kunyar kanta tana rufe fuskanta da tafukan hannuwanta tana Jin tin ganin datai masa farko shine Gani mafi farin ciki dataiwa Abu.

Haroon Daya gama wayarsa ya qaraso Yana kallan abinda sukazo dubawa gurin baima lura da mutum ba saida ya qaraso daf da ita yaganta ciki mamaki ya tsaya zai kalleta daidai Nan ta janye hannuwanta daga fuskanta kyakkyawar fuskanta daukeda murmushi sedai batasan da isowansa a gurin ba Dan haka ganinsa ya Sakata yin Baya da sauri sbd firgita da mamakin data shiga me qarfin gaske.

Shi kansa bayan yayi ahankali sbd kusancin da suka samu gashi murmushin dayake fuskanta wani faduwan gaba ya sakar masa Dan baitaba samun kusanci da mace ba haka a rayuwarsaba bayan Ayesha da yayan Dad Lameenu wainda su kannensa ne ba maganar Jin komai akansu.

MAMUH

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!

33
Hafiz dayake nesa dasu da sauri ya qaraso gurin Yana bawa Sir Haroon din hakuri tareda sanar dashi Kanwarsace ya dauko makaranta yanzu wucewa zasuyi gida tabar gurin.

Ahankali Haroon ya mayar da Idanuwansa akan Ameenatou din ya kalleta Yana mamakin kalman daukota makarantar da Hafiz din ya ambata.

Ita kuwa bayan Hafiz din ya matsa ta batareda ta iya furta kalma ko Daya ba Dan samun bakinta datai da mutuwa ‘dokin zuciyarta na ragewa batareda tasan dalili ba Kila Kuma zuciyarta tafi sonsa idan Yana daga nesa da ita ne.

Magana Jafar yayi mata a hankali wadda ta Sakata Dan fitowa kadan batareda ta kallesaba ta gaidasa cikin nutsuwa batareda tayi tinanin Yana Jin hausar ba.

Shi dariya ma ta basa Dan haka Saida ya saki Dan murmushi kadan kafin ya amsa Yana kallan Hafiz yace ya tafi da ita gida kawai yabar aikinsa zuwa gobe.

Ita kanta kaman tana jiran ya fada Hakan Dan haka ta wuce gaba batareda ta waiwayoba Hafiz kuwa wanke hannuwansa yayi tareda daukan Jakarta data barmasa yayiwa Haroon din godiya yabi bayanta Yana Bude mata umbrella data manta Yana cewa

“Salon ta ishesu da kukan zazzabi zai kashewa Babbah yar budewa ne yasakata biyosa cikin wanna uwar ranar gashi duk ta ruda masa aiki”

Shiru tayi masa Saida sukai Nisa ta waiwayo tana sake kallan Haroon Dake tsaye har lokacin Yana magana akan abinda sukazo dubawa.

Tin a hanya bakinta ya mutu har suka Isa gida Bata wani ishesa da magana ba Dan haka suna shiga gidan wanka kawai tayi taci abinci tafara kokarin kwantawa yasata gaba suka wuce islamiya Badan tayi niyar zuwa lolacinba Amma sbd tanason ringa biyawa ta gurinsa site hakanan ta shirya suke tafi.
Su kansu malaman sunyi mamakin zuwanta batareda latti ba yau din Amma dai dayake batajin hayaniyar Babu Wanda ya takurata da tambaya haka ta wuni makarantar ba hayaniya har suka tashi ta dawo gida tareda Yaya Abdul.

Washe gari ma haka suka biya site ya qarasa aikinsa ta zauna tana bin duk inda Haroon yayi da idanuwanta masu haske da kyau tana Jin kaman tace ya zauna ya Dena shiga rana duk da duk motsinsa biye ake dashi da umbrella sbd Rana karta tabasa.

Tinda take zuwa Bata sake bari ya ganta ba harta gama binsa da kallo tana murmushin su koma gida.

Abinda Bata saniba tinda kwanakin suka fara ja Yana sane da duk zuwanta da tafiyarta kuma ahankali ahankali ya fahimci sbd shine yake zuwan ta dauka bature ne shi da gasken.

Da farko lamarin mamaki da dariya yake basa sbd Bai taba Ganin inda asalin gata da tattalin ‘yaya yake ba sai akanta hakama baitaba ganin kauna da kulawa me tsananin gaske ba da yanne kewa kanwa irin Wanda ahankali yaga anaiwa yarinyar.

Tinda tafara zuwa Bata taba tsallaken zuwa ba Saida exams dinsu ta karato sosai suna farawa shikenan ta Dena zuwa kwata kwata sbd karatu sosai da Yaya Abdul ya sakota gaba dashi
Shi kansa Hafiz sosai yake Bata lokacinsa suyi karatun exams din tare.

Barin zuwanta ya Saka Haroon tambayar Hafiz ko lafiyanta kalau ya sanar masa axams takeyi Kuma dai Bata jin dadi sosai sbd wahalan karatun.

A nata bangaren ahankali ta dawo hayyacinta akan zuwa ganinsa Dan haka Koda suka gama exam kwata kwata Dena zuwa tayi ga rashin lafiya sosai Daya kwantar da ita na kusan kwanaki Dan haka suketa fama da ita anata lallabawa da ita kaman kwai.

Shi kansa Haroon duk tsananin damuwa da quncin zuciyar dayake ciki Saida yazo har gida ya dubata Wanda Hakan ya Sakata Jin dadi sosai Suma su Babbah haka suka nuna masa Jin dadinsa sosai sbd Ameenatoun.

A nasa bangaren yanda ya samu iyayenta da karamci dakuma sake ganin irin so da tsananin gatan da ake nuna mata ya sakashi fara jinta a zuciyarsa sbd kallan datake masa lokuta da dama idan ta zuba masa kyawawan idanuwanta sai yakejin damuwar datake lullube da rayuwarsa kaman tana ragewa Dan haka ya Dan saki jiki da gidansu Ameenatou din musamman Hafiz dayake qarqashinsa.

A bangaren siddeeq kuwa komai na Haroon shine yake basa kulawa da tsaro yanda ya kamata Dan haka Koda yaga Haroon din yafara samun walwala da yar sakewa a cikin Iyalin Babbah sai Shima yaji ya samu nutsuwa da Hakan take Shima ya sake suka fara samun sabo da mutunci dasu din.

A bangare Daya rayuwar Haroon din na cikin matsanancin daci da damuwa tareda rashin farin ciki ko Daya sbd Dad dinsa da suka Saka ido sosai a lamarinsa hakama Babu alaman aikin Nan nasu zai samu karbuwa a inda zasu gabatar dashi Dan haka kowace dakika ta rayuwarsa cikin damuwa da ‘daci me tsanani take Dan haka ciwonsa ma keyin gaba gaba koyaushe batareda sanin kowaba sai siddeeq Wanda ko numfashinsa Baya boyewa JEEY.

Shigarsa cikin Iyalin Babbah ya Saka Dan haske da farin ciki shigowa rayuwarsa a duk lokacinda yake cikinsu Dan takai kusan abinci ma wasu lokutan a gidan yake ci na dadah.

Ameenatou Kam zuwa yanzu tagama shiga zuciyarsa fiyeda yanda yake tinani duk da shagwabarta yayi yawa Amma shi Hakan ne ya kashe zuciyarsa ta mutu gabaki Daya akanta ita Kuma a nata bangaren a yanzu dayake tareda su sai ta aje maganan son datake masa ta jefasu a layinsu Hafiz duk da haryanxu kallansa takeyi a Wanda yafi kowa kyau da tsari Bata taba Ganin kamansa ba.

****Su Dad sun dukafa ba ji ba Gani sai barin kudi sukeyi hankali tashe gurin Neman Maryama Dan kuwa suna gap da zubewa gaba Daya Dan haka suka fice hayyacinsu.

BB ma sun haukace Baki ba ganin sunata tsananta bincike da zufafasa akan Maryama wadda daga karshe suka gano kauyensu.

Bayan barin dukiya me yawan gaske su BB Saida suka gano Maryama saigasu da ita har cikin Lagos sedai ko kwana batai a lagos ba Su Mam suka taho har inda su BB suka boyeta da daddare.

Mam ne ya fara tsayuwa akanta kafin Lameenu ya shigo bayan ya kashe wayarsa gabaki Daya daga wayar dayayi ya tsaya Shima yayi mata kallo Daya Yana komawa ya zauna kujeran alfarma dasu BB suka kawo musu na zama.

Shima Mam zama yayi Yana kallan BB batareda Bata lokaci ba Dan baida time na batawan yace

“Tatso mana bayanin komai daga bakinta banason rasa kalma ko Daya komai nakeson Jin a yanda yake dinsa.”

Qwayar datake bakin BB ya qarasa hadiyewa idanuwansa na sake rinewa jajir ya miqawa yaronsa Daya hannu ya Saka masa wata mahaukaciyar wuqa da shape dinta kadai abin tsoro ne.
Nufar Maryama din da idanuwanta suke a daure yayi tareda tsayuwa a kanta ya kamo kanta ya Bude idanuwanta ya Saka mata wuqar gaban idanuwanta da sukasha mugun dauri cikin muryansa me kauri da karajin rashin Imani yace

“Ki kalla Menene a gaban idanunki”

Kafin ma taja numfashin tsoro da tashin hankali bare taga wainda ke zaune a gurin ya mayar mata da daurin idanuwan ya rufe.

Mayar da kaifin wuqar yayi akan jijiyan maqoshin wuyanya Kai tsaye yace

“Meya faru a Daren ranar da matar sir Omar ya ta rasu?
Akwai ciki a jikinta koda ranar tazo?
Wata nawa?
Ta haihu?
Me ya Haifa?
Ina abinda ta Haifa yake?
Waye taredaku a Daren ranar?
Ya Akai kika tsira a Daren????

Cikakken bayani zakiyi sbd rashin kalma Daya daidai take da ficewan ruhinki daga gangar jikinki.”

Wasu Hawaye masu tsananin zafi ne suka gangaro daga idanuwanta dasuke a rufe zuciyarta na wani irin rawar tashin hankali da tsoro Dan kuwa tasan shikenan nata karshen yazo abinda taketa yiwa gudu sbd tasan Hakan zai iya faruwa wata ran sbd akwai tabbacin asan data tsira.

Sake daga wuyanta BB yayi Yana qarawa wuqar seti har seda ta Dan fasa wuyan jini ya Dan fito.

Zufa take fitarwa sosai kirjinta na wani irin mugun bugawar da kusan Suma su mam din kirjin nasu harbawa yakeyi sosai Dan kuwa a Baya duk zance ne sukeyi Basu tabbatarba sai yau din zasu tabbatarda masifar Dake gabansu tana can tana yawo a duniya batareda sunsan a Ina ba.

Lameenu kuwa har wani zufa yake tsiyayowa hannuwansa na rawa Da matsuwan Jin Abinda zata fadan,

Allah yasa Omar din Bai haihuba zance ne kawai,
Allah yasa suji abinda zai kawo karshen matsalar tasu idan ba Hakan ba akwai babbar matsala da kura a gaba.

MAMUH

ZAFAFA BIYAR

1 Ameenatou!!
Mamuhgee

2 Tsutsar Nama!!
Billyn Abdull

3 Gudun Kaddara!!
Safiya huguma

4 Kwankwason Jimina!!
Miss xoxo

karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!

Series Navigation<< Ameenatou Part 1Ameenatou Part 3 >>
Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *