Gishrin Zaman Duniya Chapter

Gishirin Zaman Duniya Chapter 5

*GISHIRIN*

       *ZAMAN*

*DUNIYA*

   _Daga Al’kalamin_

_Badi’at Ibrahim_

( Mrs Bukhari Ibrahim B4B)

GAWURTATTU BIYAR 🤚🏻

Labari wanda yai duba kan gwagwarmayar mata a duniya. Da irin gudummawar da ilimin mace ya ke bayarwa  ga al’umma. Da kuma rawar da ilimin mata ke takawa a cikin gidajen Aure.

Kashi na 1

Babi na 9~10

Anas ne ya shigo ‘barayin Sadiya shi da Amadi kafinta.

“Goggo wannan shine kafintan kin ganshi, kusan duk kauyan nan shi ke yin aikin kafinta.” Goggo tace.

“Kaga madafi  na ke so ka buga mun na langa langa ko da ta can bangaren ne.” Ta nuna mai dai dai in da ya dace.

“Asa  k’ofa da abun kullewa a jiki. Amma yau na ke so, ko in ce ma yanzu.” Amadi ya duba ya ce.

“Toh da tsohon langa langa ko da sabo?” Goggo tace.

“Sabon dai zai fi, tunda na Amarya ne.” Shiru ya d’an yi sannan ya ce.

“Nera dubu uku da d’ari biyar za’a biya. Zan buga mata me kyau, kuma na sa har da ku’din abun hawa. Jiya na siyo langa langar, zan yi gyara, amma zan yi muku da shi. Ina gamawa sai in shiga Gusau in siyo wasu.” Goggo ta ciro ku’din a jaka  ta ba shi. A cikin minti talatin ya kammala buga kitchen d’in, har da buga katakai zagayen kitchen d’in. Yanda za’a iya jera  wasu kayan. Goggo Hansatu ta na tsaye a kitchen d’in ta na jera  kaya. Mamaki da al’ajabin irin muguntar  da dangin mijin yarta  su kai ma Sadiya ta ke yi. Domun zaman wannan k’auyan k’ayau tashin hankaline ga wanda yai rayuwar maraya. Ta gama jera  komai da komai, kuma duk da haka akwai sarari  sosai, kitchen ya yi mugun kyau, sai dai k’asan  ba siminti  k’asa ce kawai. Kayayyaki da dama baza su yi ma Sadiya amfanin komai ba domun kayan wuta ne. Sauran kayan da su ka rage, Goggo ta d’aga kar’kashin gado ta zuba mata shi.

******

Khadija ta na tsakar gida sai kuka ta ke ta faman yi. Mahaifinta mai gari ne ya fito tsakar gidan, ganin Khadija na kuka ya sake jagula shi.

“Khadija ke tun jiya wannan kukan bai k’are ba? Na fa’da miki kiyi shiru, dole Aliyu ya za’bi d’aya ko ke, ko ‘yar bokon  da aka Aura mishi, amma bazan bari a ha’da ki kishi da ‘yar duniya masu budadden idanu ba. Ina ganin ki yi hak’uri da Aliyu shi zai fi.Domun anci amanarmu, yarinyar shekara nawa ina mishi rainonta, sai ace kuma yanzu anyi mishi aure. Mai dambu mahaifiya  a wajan Khadija, kuma aminiya ga Goggo Asabe. tace.

” Haba malam ba’a gaggauwar  yanke k’auna, musamman k’auna irin ta Aliyu da Khadija. Yarinyar nan tun tana yarinya Aliyu ke kula da ita, tun sanda aka ce matar shi ce. A  RAQUMA babu wanda bai san son da su ke yi ma juna ba. Kuma ni na tabbatar Aliyu ba zai fifita tsohuwar guxumar da aka ce an aura mishi ba, sama da Khadija. Yana yima khadija wani irin makahon so, kai ka sani malam. Ni gani na ke yi ka bari tukunna Asabe ta dawo in ji meye nufinta, ai  yau za su dawo.” Girgiza kai yayi yace.

“Mai dambu hoo. Toh Allah ya kaimu ta dawo d’in. Ni zan fita. Tace.

” Adawo lafiya malam. Amma za mu je gidan bikin da Khadija inna gama share d’akin tumakai.” Ya ce.

“Gidan watsewa  zai yi yau kenan. Hauwa  da Hajara ma duk sun tambayi anguwa. Toh su kuma tumakan fa?” Mai dambu tace.

“Hamisu  ya na gida, baza shi ko ina ba. Har sai na dawo.”

“Sai kun dawo” ya sa kai ya fice. Mai dambu ta kammala duk aikace aikacen  da ya dace ta yi na gida. Sannan ta yo wanka. Da k’yar ta lallab’a Khadija sannan ta yo wankan. Mai dambu tace.

“Nace ki saki jikinki Khadija, dolen Aliyu ya aureki, kuma dole ki mallakeshi, kamar yanda na mallake ubanki, kema ke ce zaki yi mulki a gidan Aliyu. Kuma ai ke ya ke so kab k’auyannan babu wanda bai sani ba. Ki share hawayenki, in dai nice uwarki, toh hatta Asabe saikin fita iko da Aliyu.

 Sallama mai Dambu tai ma abokan zaman ta akan cewar ta fita. Adawo lafiya su ka yi mata. Ficewa su ka yi a gidan.

Khadija ta na tafe sukuku  babu laka a jikinta, hankali da tunaninta  sam baya tare da ita. Gani ta ke yi, in dai ta rasa Aliyu, tamkar munfashinta  zai iya tsayawa ne. Sai dai kuma maganganun mahaifiyarta na yi mata wani irin yawon da yake shirin farfad’o da kuzaranta. Amma sai gabanta ya tsananta fad’uwa  da su ka iso  k’ofar gidan su Aliyu. Abokan shi ta gani a k’ofar gidan. Wani kallo ta watsa musu, wanda su kan su sai da su ka sha jinin jikin su.Kuma sun yarda ba’a kyauta mata ba, sai dai suna taya abokinsu murnar samun matar birni. Su Goggo Asabe ne su ka iso  a kan Babur.

Sadiya

Tsai  Khadija ta yi ta na kallo na, wasu zafafan hawaye ne su ka zubo mata. Ni ko kaina na k’asa ba ma a iya ganin fuskata. Maman Amina ce ta ke ri’ke da ni. Goggo Mariya ce ta nuna ma maman su Amina gidan da za mu shiga. Ina cikin mayafi na ke jiyo muryar wasu maza su na mun sannu da zuwa.

GOGGO

Goggo Asabe da ta ga mai dambu ta ce.

“Ohh mai dambu yanzu fa kina raina, niyya ta shine, daga nan in wuce gidanki.” Khadija ce ta karaso ta fa’da jikin Goggo Asabe ta saki kukan da ta ke ta ri’kewa. Goggo Asabe ta ce.

‘’ki kwantar da hankalinki khadija. Aliyu dai na ki ne. kuma babu mai raba ku. mai dambu mu je mu daga ciki.

hannun khadija na cikin na Goggo Asabe, su ka kutsa zuwa cikin gidan,

Sadiya

ni kuwa mu na shiga jama,ar biki su ka tarbe ni. Mata an yi cincirindon son ganin Amaryar Aliyu. Nayi mamakin irin taron da aka had’a na mata. kai tsaye  d’akin Goggo Asabe cikin k’uryar d’akinta aka shige da ni. a tabarma na zauna tare da sauke ajjiyar xuchiya na azabar da mu ka sha a hanya. ga zazzab’i da ke ta damuna.Gabaki d’aya babu abunda ke mun dad’i. Hankalina ya k’ara tashi matuk’a da ganin irin k’auyan da aka kawoni zanyi rayuwar Aure a ciki. Rayuwar da ake mata fatan d’orewa har abada. fatima yayar Aliyu ce ta zauna kusa da ni.

“Barka da isowa Amarya ina miki maraba. murmushin yak’e na yi mata, na ce.

nagode Fatima. Ina yaran su ke?

“suna k’war gida, wasa su ke yi. Sallamar su Goggo Asabe ce ta katse mu ni da Fatima.

“shigo mai dambu ki ji kan labari. zama mai dambu ta yi, khadija ma ta zauna.

“mai dambu Bala ne ki na ji ya cuce ni, ya had’a Aurannan. Allah shine shaida ta bana son wannan Auran. kuma yaronnan nawa ne, daya dawo za’ayi bikin a lokacin da yake a tsaye, ai mijin mata hudu ne k’usar yak’i. Sannan Khadija ce surukar da nake so Aliyu ya kawo mun ita cikin gidannan. Ke mai dambu kinsan irin amincin dake tsakanina dake, babu batun yaudara, asalima dan zumuncinmu ya sake yin dank’one muka had’a yarannan namu. Ko ba gaskiya ba? Kuyi hak’uri bisa k’addarar data kunno kai.

 mai dambu tace

“matsalar fa Asabe ita ce. tsakani da Allah ba’ayi mana adalci ba.babu dattaku a cikin wannan lamarin. kuma mahaifin yarinyar nan cewa ya yi dole Aliyu sai dai ya zab’i d’aya. ko ‘yar boko, ko khadija. amma bazai ha’da su ba. kuma ni kai na ina  bayan hakan Asabe. Yarinya dai kun cutar mun da ita. Tunda labarinnan ya isheta take ta faman kuka, hankalinmu ba a kwance yake ba sam.

Goggo Asabe ta ce.

“tunda mu mu ke neman iri, zanje in sami mai garin  zuwa da daddare in na wuta. saura kwana biyar yaronnan ya dawo.”

muk’ut na had’iye wani kakkauran yawu mai d’aci, hawaye sirara su ka surnano mun. na zama abun tausayi. Goggo da kanta ta ke fadama bare cewar cutar ta aka yi da aka aura ma Aliyu ni? yar mahaifina uwa d’aya uba d’aya. Wannan wanne irin k’iyayya Goggo take nuna mini haka?  Fatima ta mi’ke ta fita. ana ta hidimar biki. ni kuwa babu wanda ya sake bi ta kaina. ga zazzab’i ga yunwa, uwa uba k’ishin ruwa na ke ji. amma na kasa ko da motsi mai kyau. A mugun takure nake, gashi duk wanda ya shigo sai Goggo ta bashi labarin, a birni sau uku ana sa bikina, amma sabida boko na kasa auruwa, shine aka cuceta aka aura ma k’usar yak’i ni.

Su Amina ne a cikin kasuwar kanawa me suna samaru ta cikin garin Gusau. sun sai duk wani  abunda Goggo Hansatu ta ba su sallahu. harda ma wanda su ka tabbatar Sadiya za ta buk’ata. hanyar dawowa su ka nufa. sun wahala sosai wujiga wujiga su ka dawo da yamma lis. Goggo Hansatu za ta fito daga b’arayin Sadiya kenan su kuma su na shigowa.

“wayyo yarannan ina ta tunaninku. ga su Sadiya ma sun iso tun tuni. shine zanje in dawo da’ita ta shiga d’akinta. ku shiga ku huta, yanzu ma za’a kira sallah.

fita Goggo ta yi, ta nufi cikin b’arayin su Goggo Asabe. a bakin k’ofa ta tsaya ta bud’e labulen da sallama tace.

“Yaya Asabe kun iso lafiya?” Goggo Asabe tace.

“lafiya” Goggo Safiya tace.

“dama yanzu mu ke shirin za mu kawo ta da kin k’ara hakuri ba cinye ta za mu yi ba. Goggo Asabe ce ta d’agama Goggo Safiya hannu sannan tace.

“dama za’a kawo ta. akwai abunda muke jira ne. tunda kun kasa hak’uri za’a kawota ki je.” juyawa Goggo tayi. Tana mayar musu da martanin cewar ai ta zaci cinyenin za su yi. ni ko ina d’aki a takure, ina jiyo su. sai wajajen bayan isha. A lokacin na gama galabaita da zazzab’i da yunwa. Goggo mariya ta shigo d’akin da na ke.

“ta so mu je Sadiya in kai ki d’akin mijinki.” da sauri na mik’e, ta na gaba. ina biye da ita a baya har zuwa falon Goggo Asabe. wasu mata na gani da gani K’awayen Goggo ne. sune su ka rakani d’akina. a falo su ka zazzauna. nasiha su ka shiga yi mun. sannan su ka yi sallama su ka fice.

da sauri na bud’e mayafina. ina hawaye Goggo Hansatu ce ta matso kusa da ni. da sauri na fad’a kirjinta nai lamo. kau ta ji jikina da zafi rau. nan hankalinta ya tashi.

“Sadiya kin kuwa sha maganinki kuwa, kin ma ci abinci kuwa?

kai kawai na iya girgiza mata dan a mugun galabaice nake. Amina ce ta shiga kitchen ta kunna risho. ruwan zafi ta d’aura mun da zan yi wanka. ina zaune kusa da Goggo. kaina na d’aga na kalli rufin d’akina. lantarki mai yin chaji da hasken rana na gani a manne. kamar kwan wuta ya ke, ya na da haske sosai. kuma ya na rik’e chaji. ajjiyar zuchiya na sauke dan na d’anji sanyi a raina. rufin d’akin na sake kallo inaso in tantance da me aka rufe saman d’akin. naga dai abu bak’i zare zare a jere ras. da kyar na gane igiyar dake cikin video kaset ne wannan bak’in mai d’an fad’i na ciki. Goggo Hansatu ce ta katse mun tunani na da cewar.

“Sadiya mu je in nuna miki toilet ki yi wanka. ga shayi ki sha sai in baki magani.”

mik’ewa na yi. na bita a baya. langa langa ta nuna mun ta ce.

“ga toilet d’innan ki shiga ruwan na ciki.”

to.

kawai na iya ce mata.

na shige toiket d’innan ya sha plasta ya yi kyau. ga shadda irinta gargajiya mai k’aramin baki. cikin nutsuwa na yo wankan tare da d’auro alwala na fito.

bedroom na shiga dukkansu su na ciki. wadrope d’ina wacce ta cika bango guda na bud’e. kaya na su na jere reras. doguwar rigar bacci mai sauk’i na sanya. turare na fesa a jikin rigar. sannan na yi sallah. Hadiza ta mik’amun tea a kofi mai kauri, dan har kayan tea duk sun siyo mun manyan gwangwamaye.

ahankali na ke sha har na shanye. sannan na sha magani. ina jin su suna ta tab’a hirarsu da ban dariyar jama’ar k’auyannan, yanda su kaita tururuwar zuwa ganin d’akina. ganin hakanne yasa har na d’an sake. a lokacinne na samu damar karema d’akin kallo. iya ha’duwa ya tsaru ko a birni d’aki ne na azo a gani.

tabkeken gadone  6 by 7 fararene kayan katakon  sai ratsin gold da ke jiki. wadrope dina babbace mai kofa shida, sannan ga dresing mirror na a gefe harda kujerar zaman kwalliya. labulayen d’akin kuma gold colour ne. haka ma kafet din dake malale a cikin uwar d’akin shima kalar gold ne.

falona kuma kujerune kirar Royal masu kalar gold da ja. manya manya ne sosai daga gefe kuma show glass ce me biyu da abun ‘daura tv a tsakiya. show glass dinnan ta sha roses da kiristal masu kyau sai tv na a tsakiya aka ajjiyeshi da video a k’asan shi. kafet ne ja malala a kasan falon haka labulayen falon jajayene masu kyau. falon ba tarkace sam abun sha’awa.

Goggo Hansatu tace.

“Sadiya hauro ki kwanta kinji. kuma ya kamata mu bar hirar nan haka nan gobe za’a d’auki hanyar gida kuma.

koda na kwanta na kasa bacci sam. sai tunane tunane na ke yi. babu abunda ya fi tsaya mun sai zancan Auran Aliyu bayan dawowarshi da wata guda. idanu na lumshe a raina nace.

“yau ni ce a tsakankanin masoya biyu na shigo rayuwarsu ba tare da sun shirya ba. na rusa musu duk abunda su ka jima su na tsarawa. Haka nima duk wani tanadi da tsara yanda zan gudanar da rayuwar aurena, da yanda zan gigita mijina da soyayyar da saina juya mishi k’wak’walwa, yanxu duk ya kau. Na auri d’an k’auye yaro k’arami.Da wanne idanunma zan iya mishi kallon miji.  Shin yama rayuwar k’auyan zata kasancemun?

haka nai ta tunani. sai jefin asuba bacci yai awon gaba da ni.

WASHE GARI

 tun sassafe na yi wanka. sanye nake da shadda mai ruwan k’asa. dinkin riga da siket yasha surrani da milk colour d’in zare. d’inkin ya zauna a jikina sosai. kwalliya na yi mai tsari, jikina kuma sai tashin kamshi ya ke yi. takalmi ne mai tsini a kafata milk colour, haka ma mayafin jikina ya kasance milk. Goggo Hansatu tace.

” su Hadiza su raka ki ku gaisa da  ayagin surukarki da matan gida. kafin su d’au haramar tafiya kuma. dubanta na yi nace.

Goggo kema yau za ki tafi?

“A’a Sadiya. zan zauna sai nan da kwana hud’u ranar da Aliyu zai dawo sai in tafi. a k’alla zan d’ebe miki kewa.

da’di naji sosai da jin bayanin Goggo.

fita mu ka yi da su Hadiza. mu na tafe ne nace.

Hadiza lallai Bashir yayi kok’ari daya barki ki ka zo bikina tun daga katsina. gaki har kauyenmu. dariya Hadiza ta yi tace.

“Haba Sadiya ai muna tare. abinda na ke so dake shine. karki sake kallon rayuwar da ki ka gudanar ta baya. Sadiya abu guda mace take buk’ata a rayuwarta shine ta samu kulawa da tausayi a gidan mijinta. in gidan aure ya samu wannan toh magana ta k’are. ni shawarar da zan baki shine. ki kawo walwala da farin ciki gidan auranki. ki gaiyato haske da raha a zamanki da.Aliyu. ke wayayyace kinsan meye makamar d’a namiji. idan ki ka yi hakan zaki samu nutsuwar da sai kauyannan ya zame miki tamkar America.

kai na kad’a. maganarta gaskiya ne.

Hakane Hadiza zanyi kokarin hakan. amma wannan sai mun samu fahimtar juna tare da shi. kinsan yaro ne, dole al’amuran ba za su zo mun da sauk’i ba. ni wallahi kunya ma nake ji.

Amina tace

“shi namiji ba ya kad’an. ni mijina sai da na shekara d’aya a hannunshi ba mu’amalar Aure. sai dai mu yi wasa da juna kawai. gaban na shi ashe ya na da matsala. sai da ga baya ne ya samu lafiya. amma ba wanda yasan wannan labarin sai ku da na sanar ma yau. shi namiji ba’a shekaru bane. kar ki yi girman kai ki je ki shiga wuta a banza.”

hirar ta mu ta tsaya ne, a sakamakon isowa b’arayin su Goggo Asabe. da sallama mu ka shiga falon Goggo Asabe. duk yayyan Babana su na ciki, da alama tattaunawa su ke yi. gurfana mu ka yi a gabansu mu ka gaishesu da girmamawa. sun amsa a sake babu laifi. kawu Sulaiman yace.

“Sadiya. sai ki sake hakuri nan da kwana hudu mu ke sa ran Aliyu zai dawo. ki kula dan baza mu yadda da fitsara irin taku ta ‘yan boko ba ma su ido a tsakar ka. Aliyu kuma dole ki mai biyayya domun duk shekarunki da matsayinki kin dawo karkashin ikon shi ne. kar kuma ki ji wani iri. bayan wata guda da dawowarshi za’a d’aura Auranshi. gyatumarki ma ta san da hakan. akwai dokoki da k’a’idoji akan ko wacce surukar gidannan. dan haka za ki iya samun Bilkisu. matar wan Aliyu ta yi miki bayanan daya dace.

A sanyaye na ce.

Toh kawu zan yi hakan in sha Allah.

Su Goggo Asabe a cikinsu ba wacce ta ce da mu uffan. sai daga baya Goggo Asabe tace.

“Toh ki koma d’akin ki. magana mu ke yi.

dole na kalato murmushi na d’aura ma fuskata nace.

Toh Goggo.

jiki a mace mu ka fito. mun d’an zazzaga cikin gidan Bilkisu ce tai mana jagora. tare da gabatar mun da surukan gidan. gaggaisawa mu ka yi da kowa. sai dai da dukkan alama ban samu karb’uwa ba sam a wajansu. Dan sai wani hararata suke yi, su nai mun kallon banza haka.

komawa mu ka yi b’angare na. Sallama muka soma jiyowa ta namiji a k’ofar b’arayina. Hadiza ce ta fita.

“Sannu baiwar Allah, kune k’awayen Amaryar tamu ko? Hadiza da dariya a fuskarta tace.

“Eh mune”

Murmushi yayi yace.

“Sunana Kamilu, nine aminin Aliyu, tun jiya naso in zo dan mu gana da ku, toh sauran abokan namu suna waje, dama a game da sallamar k’ayawyene, bisa ga al’ada.”

Hadiza tace.

“Hakane, sai ku bayar da duk abunda ya sauwak’a, jiya ma baku kawo mana abinci ba” kai Kamilu ya sosa.

“Eh ayi mana afuwa, sai yau na gama harhad’o kan abokan, Amma ga abun kari.” Hannu tasa ta amsa, leda ce mai d’auke da gasassun zabi, sai robar fenti cike da tea, wanda sai da Kamilu ya fita zuwa cikin zamfara ya siyo kayan tean. nera dubu biyar ya mik’ama Hadiza”

“Ga wannan ayi hak’uri, abun yazo mana babu shiri.”

“Ah babu komai mun gode” ciki Hadiza ta dawo ta kawo mana kayan kari, tare da yi mana bayanin yanda su ka yi da Kamilu. bayan sun gama karyawa, sun yi wanka. sai kuma su ka fito dan tafiya.

ina kuka mu ka rabu da su. tare da mun al’kawarin za su kewayo ni.

Goggo ce ta ri’ke hannuna mu ka koma ciki. kan gado na fad’a ina ta kuka amma mara sauti.

wai wanne irin matsalolin zan fuskanta ne a wannan zaman Auran?

mrs Bukhari ce

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *