Gishrin Zaman Duniya Chapter

Gishirin Zaman Duniya Chapter 5

*GISHIRIN*

Ā Ā Ā Ā Ā Ā  *ZAMAN*

*DUNIYA*

Ā Ā  _Daga Alā€™kalamin_

_Badiā€™at Ibrahim_

( Mrs Bukhari Ibrahim B4B)

GAWURTATTU BIYAR šŸ¤ššŸ»

Labari wanda yai duba kan gwagwarmayar mata a duniya. Da irin gudummawar da ilimin mace ya ke bayarwaĀ  ga alā€™umma. Da kuma rawar da ilimin mata ke takawa a cikin gidajen Aure.

Kashi na 1

Babi na 9~10

Anas ne ya shigo ā€˜barayin Sadiya shi da Amadi kafinta.

ā€œGoggo wannan shine kafintan kin ganshi, kusan duk kauyan nan shi ke yin aikin kafinta.ā€ Goggo tace.

ā€œKaga madafiĀ  na ke so ka buga mun na langa langa ko da ta can bangaren ne.ā€ Ta nuna mai dai dai in da ya dace.

ā€œAsaĀ  kā€™ofa da abun kullewa a jiki. Amma yau na ke so, ko in ce ma yanzu.ā€ Amadi ya duba ya ce.

ā€œToh da tsohon langa langa ko da sabo?ā€ Goggo tace.

ā€œSabon dai zai fi, tunda na Amarya ne.ā€ Shiru ya dā€™an yi sannan ya ce.

ā€œNera dubu uku da dā€™ari biyar zaā€™a biya. Zan buga mata me kyau, kuma na sa har da kuā€™din abun hawa. Jiya na siyo langa langar, zan yi gyara, amma zan yi muku da shi. Ina gamawa sai in shiga Gusau in siyo wasu.ā€ Goggo ta ciro kuā€™din a jakaĀ  ta ba shi. A cikin minti talatin ya kammala buga kitchen dā€™in, har da buga katakai zagayen kitchen dā€™in. Yanda zaā€™a iya jeraĀ  wasu kayan. Goggo Hansatu ta na tsaye a kitchen dā€™in ta na jera Ā kaya. Mamaki da alā€™ajabin irin muguntarĀ  da dangin mijin yartaĀ  su kai ma Sadiya ta ke yi. Domun zaman wannan kā€™auyan kā€™ayau tashin hankaline ga wanda yai rayuwar maraya. Ta gama jeraĀ  komai da komai, kuma duk da haka akwai sarariĀ  sosai, kitchen ya yi mugun kyau, sai dai kā€™asanĀ  ba simintiĀ  kā€™asa ce kawai. Kayayyaki da dama baza su yi ma Sadiya amfanin komai ba domun kayan wuta ne. Sauran kayan da su ka rage, Goggo ta dā€™aga karā€™kashin gado ta zuba mata shi.

******

Khadija ta na tsakar gida sai kuka ta ke ta faman yi. Mahaifinta mai gari ne ya fito tsakar gidan, ganin Khadija na kuka ya sake jagula shi.

ā€œKhadija ke tun jiya wannan kukan bai kā€™are ba? Na faā€™da miki kiyi shiru, dole Aliyu ya zaā€™bi dā€™aya ko ke, ko ā€˜yar bokonĀ  da aka Aura mishi, amma bazan bari a haā€™da ki kishi da ā€˜yar duniya masu budadden idanu ba. Ina ganin ki yi hakā€™uri da Aliyu shi zai fi.Domun anci amanarmu, yarinyar shekara nawa ina mishi rainonta, sai ace kuma yanzu anyi mishi aure. Mai dambu mahaifiyaĀ  a wajan Khadija, kuma aminiya ga Goggo Asabe. tace.

ā€ Haba malam baā€™a gaggauwarĀ  yanke kā€™auna, musamman kā€™auna irin ta Aliyu da Khadija. Yarinyar nan tun tana yarinya Aliyu ke kula da ita, tun sanda aka ce matar shi ce. AĀ  RAQUMA babu wanda bai san son da su ke yi ma juna ba. Kuma ni na tabbatar Aliyu ba zai fifita tsohuwar guxumar da aka ce an aura mishi ba, sama da Khadija. Yana yima khadija wani irin makahon so, kai ka sani malam. Ni gani na ke yi ka bari tukunna Asabe ta dawo in ji meye nufinta, aiĀ  yau za su dawo.ā€ Girgiza kai yayi yace.

ā€œMai dambu hoo. Toh Allah ya kaimu ta dawo dā€™in. Ni zan fita. Tace.

ā€ Adawo lafiya malam. Amma za mu je gidan bikin da Khadija inna gama share dā€™akin tumakai.ā€ Ya ce.

ā€œGidan watsewaĀ  zai yi yau kenan. HauwaĀ  da Hajara ma duk sun tambayi anguwa. Toh su kuma tumakan fa?ā€ Mai dambu tace.

ā€œHamisuĀ  ya na gida, baza shi ko ina ba. Har sai na dawo.ā€

ā€œSai kun dawoā€ ya sa kai ya fice. Mai dambu ta kammala duk aikace aikacenĀ  da ya dace ta yi na gida. Sannan ta yo wanka. Da kā€™yar ta lallabā€™a Khadija sannan ta yo wankan. Mai dambu tace.

ā€œNace ki saki jikinki Khadija, dolen Aliyu ya aureki, kuma dole ki mallakeshi, kamar yanda na mallake ubanki, kema ke ce zaki yi mulki a gidan Aliyu. Kuma ai ke ya ke so kab kā€™auyannan babu wanda bai sani ba. Ki share hawayenki, in dai nice uwarki, toh hatta Asabe saikin fita iko da Aliyu.

Ā Sallama mai Dambu tai ma abokan zaman ta akan cewar ta fita. Adawo lafiya su ka yi mata. Ficewa su ka yi a gidan.

Khadija ta na tafe sukukuĀ  babu laka a jikinta, hankali da tunanintaĀ  sam baya tare da ita. Gani ta ke yi, in dai ta rasa Aliyu, tamkar munfashintaĀ  zai iya tsayawa ne. Sai dai kuma maganganun mahaifiyarta na yi mata wani irin yawon da yake shirin farfadā€™o da kuzaranta. Amma sai gabanta ya tsananta fadā€™uwaĀ  da su ka isoĀ  kā€™ofar gidan su Aliyu. Abokan shi ta gani a kā€™ofar gidan. Wani kallo ta watsa musu, wanda su kan su sai da su ka sha jinin jikin su.Kuma sun yarda baā€™a kyauta mata ba, sai dai suna taya abokinsu murnar samun matar birni. Su Goggo Asabe ne su ka isoĀ  a kan Babur.

Sadiya

TsaiĀ  Khadija ta yi ta na kallo na, wasu zafafan hawaye ne su ka zubo mata. Ni ko kaina na kā€™asa ba ma a iya ganin fuskata. Maman Amina ce ta ke riā€™ke da ni. Goggo Mariya ce ta nuna ma maman su Amina gidan da za mu shiga. Ina cikin mayafi na ke jiyo muryar wasu maza su na mun sannu da zuwa.

GOGGO

Goggo Asabe da ta ga mai dambu ta ce.

ā€œOhh mai dambu yanzu fa kina raina, niyya ta shine, daga nan in wuce gidanki.ā€ Khadija ce ta karaso ta faā€™da jikin Goggo Asabe ta saki kukan da ta ke ta riā€™kewa. Goggo Asabe ta ce.

ā€˜ā€™ki kwantar da hankalinki khadija. Aliyu dai na ki ne. kuma babu mai raba ku. mai dambu mu je mu daga ciki.

hannun khadija na cikin na Goggo Asabe, su ka kutsa zuwa cikin gidan,

Sadiya

ni kuwa mu na shiga jama,ar biki su ka tarbe ni. Mata an yi cincirindon son ganin Amaryar Aliyu. Nayi mamakin irin taron da aka hadā€™a na mata. kai tsayeĀ  dā€™akin Goggo Asabe cikin kā€™uryar dā€™akinta aka shige da ni. a tabarma na zauna tare da sauke ajjiyar xuchiya na azabar da mu ka sha a hanya. ga zazzabā€™i da ke ta damuna.Gabaki dā€™aya babu abunda ke mun dadā€™i. Hankalina ya kā€™ara tashi matukā€™a da ganin irin kā€™auyan da aka kawoni zanyi rayuwar Aure a ciki. Rayuwar da ake mata fatan dā€™orewa har abada. fatima yayar Aliyu ce ta zauna kusa da ni.

ā€œBarka da isowa Amarya ina miki maraba. murmushin yakā€™e na yi mata, na ce.

nagode Fatima. Ina yaran su ke?

ā€œsuna kā€™war gida, wasa su ke yi. Sallamar su Goggo Asabe ce ta katse mu ni da Fatima.

ā€œshigo mai dambu ki ji kan labari. zama mai dambu ta yi, khadija ma ta zauna.

ā€œmai dambu Bala ne ki na ji ya cuce ni, ya hadā€™a Aurannan. Allah shine shaida ta bana son wannan Auran. kuma yaronnan nawa ne, daya dawo zaā€™ayi bikin a lokacin da yake a tsaye, ai mijin mata hudu ne kā€™usar yakā€™i. Sannan Khadija ce surukar da nake so Aliyu ya kawo mun ita cikin gidannan. Ke mai dambu kinsan irin amincin dake tsakanina dake, babu batun yaudara, asalima dan zumuncinmu ya sake yin dankā€™one muka hadā€™a yarannan namu. Ko ba gaskiya ba? Kuyi hakā€™uri bisa kā€™addarar data kunno kai.

Ā mai dambu tace

ā€œmatsalar fa Asabe ita ce. tsakani da Allah baā€™ayi mana adalci ba.babu dattaku a cikin wannan lamarin. kuma mahaifin yarinyar nan cewa ya yi dole Aliyu sai dai ya zabā€™i dā€™aya. ko ā€˜yar boko, ko khadija. amma bazai haā€™da su ba. kuma ni kai na inaĀ  bayan hakan Asabe. Yarinya dai kun cutar mun da ita. Tunda labarinnan ya isheta take ta faman kuka, hankalinmu ba a kwance yake ba sam.

Goggo Asabe ta ce.

ā€œtunda mu mu ke neman iri, zanje in sami mai garinĀ  zuwa da daddare in na wuta. saura kwana biyar yaronnan ya dawo.ā€

mukā€™ut na hadā€™iye wani kakkauran yawu mai dā€™aci, hawaye sirara su ka surnano mun. na zama abun tausayi. Goggo da kanta ta ke fadama bare cewar cutar ta aka yi da aka aura ma Aliyu ni? yar mahaifina uwa dā€™aya uba dā€™aya. Wannan wanne irin kā€™iyayya Goggo take nuna mini haka?Ā  Fatima ta miā€™ke ta fita. ana ta hidimar biki. ni kuwa babu wanda ya sake bi ta kaina. ga zazzabā€™i ga yunwa, uwa uba kā€™ishin ruwa na ke ji. amma na kasa ko da motsi mai kyau. A mugun takure nake, gashi duk wanda ya shigo sai Goggo ta bashi labarin, a birni sau uku ana sa bikina, amma sabida boko na kasa auruwa, shine aka cuceta aka aura ma kā€™usar yakā€™i ni.

Su Amina ne a cikin kasuwar kanawa me suna samaru ta cikin garin Gusau. sun sai duk waniĀ  abunda Goggo Hansatu ta ba su sallahu. harda ma wanda su ka tabbatar Sadiya za ta bukā€™ata. hanyar dawowa su ka nufa. sun wahala sosai wujiga wujiga su ka dawo da yamma lis. Goggo Hansatu za ta fito daga bā€™arayin Sadiya kenan su kuma su na shigowa.

ā€œwayyo yarannan ina ta tunaninku. ga su Sadiya ma sun iso tun tuni. shine zanje in dawo daā€™ita ta shiga dā€™akinta. ku shiga ku huta, yanzu ma zaā€™a kira sallah.

fita Goggo ta yi, ta nufi cikin bā€™arayin su Goggo Asabe. a bakin kā€™ofa ta tsaya ta budā€™e labulen da sallama tace.

ā€œYaya Asabe kun iso lafiya?ā€ Goggo Asabe tace.

ā€œlafiyaā€ Goggo Safiya tace.

ā€œdama yanzu mu ke shirin za mu kawo ta da kin kā€™ara hakuri ba cinye ta za mu yi ba. Goggo Asabe ce ta dā€™agama Goggo Safiya hannu sannan tace.

ā€œdama zaā€™a kawo ta. akwai abunda muke jira ne. tunda kun kasa hakā€™uri zaā€™a kawota ki je.ā€ juyawa Goggo tayi. Tana mayar musu da martanin cewar ai ta zaci cinyenin za su yi. ni ko ina dā€™aki a takure, ina jiyo su. sai wajajen bayan isha. A lokacin na gama galabaita da zazzabā€™i da yunwa. Goggo mariya ta shigo dā€™akin da na ke.

ā€œta so mu je Sadiya in kai ki dā€™akin mijinki.ā€ da sauri na mikā€™e, ta na gaba. ina biye da ita a baya har zuwa falon Goggo Asabe. wasu mata na gani da gani Kā€™awayen Goggo ne. sune su ka rakani dā€™akina. a falo su ka zazzauna. nasiha su ka shiga yi mun. sannan su ka yi sallama su ka fice.

da sauri na budā€™e mayafina. ina hawaye Goggo Hansatu ce ta matso kusa da ni. da sauri na fadā€™a kirjinta nai lamo. kau ta ji jikina da zafi rau. nan hankalinta ya tashi.

ā€œSadiya kin kuwa sha maganinki kuwa, kin ma ci abinci kuwa?

kai kawai na iya girgiza mata dan a mugun galabaice nake. Amina ce ta shiga kitchen ta kunna risho. ruwan zafi ta dā€™aura mun da zan yi wanka. ina zaune kusa da Goggo. kaina na dā€™aga na kalli rufin dā€™akina. lantarki mai yin chaji da hasken rana na gani a manne. kamar kwan wuta ya ke, ya na da haske sosai. kuma ya na rikā€™e chaji. ajjiyar zuchiya na sauke dan na dā€™anji sanyi a raina. rufin dā€™akin na sake kallo inaso in tantance da me aka rufe saman dā€™akin. naga dai abu bakā€™i zare zare a jere ras. da kyar na gane igiyar dake cikin video kaset ne wannan bakā€™in mai dā€™an fadā€™i na ciki. Goggo Hansatu ce ta katse mun tunani na da cewar.

ā€œSadiya mu je in nuna miki toilet ki yi wanka. ga shayi ki sha sai in baki magani.ā€

mikā€™ewa na yi. na bita a baya. langa langa ta nuna mun ta ce.

ā€œga toilet dā€™innan ki shiga ruwan na ciki.ā€

to.

kawai na iya ce mata.

na shige toiket dā€™innan ya sha plasta ya yi kyau. ga shadda irinta gargajiya mai kā€™aramin baki. cikin nutsuwa na yo wankan tare da dā€™auro alwala na fito.

bedroom na shiga dukkansu su na ciki. wadrope dā€™ina wacce ta cika bango guda na budā€™e. kaya na su na jere reras. doguwar rigar bacci mai saukā€™i na sanya. turare na fesa a jikin rigar. sannan na yi sallah. Hadiza ta mikā€™amun tea a kofi mai kauri, dan har kayan tea duk sun siyo mun manyan gwangwamaye.

ahankali na ke sha har na shanye. sannan na sha magani. ina jin su suna ta tabā€™a hirarsu da ban dariyar jamaā€™ar kā€™auyannan, yanda su kaita tururuwar zuwa ganin dā€™akina. ganin hakanne yasa har na dā€™an sake. a lokacinne na samu damar karema dā€™akin kallo. iya haā€™duwa ya tsaru ko a birni dā€™aki ne na azo a gani.

tabkeken gadoneĀ  6 by 7 fararene kayan katakonĀ  sai ratsin gold da ke jiki. wadrope dina babbace mai kofa shida, sannan ga dresing mirror na a gefe harda kujerar zaman kwalliya. labulayen dā€™akin kuma gold colour ne. haka ma kafet din dake malale a cikin uwar dā€™akin shima kalar gold ne.

falona kuma kujerune kirar Royal masu kalar gold da ja. manya manya ne sosai daga gefe kuma show glass ce me biyu da abun ā€˜daura tv a tsakiya. show glass dinnan ta sha roses da kiristal masu kyau sai tv na a tsakiya aka ajjiyeshi da video a kā€™asan shi. kafet ne ja malala a kasan falon haka labulayen falon jajayene masu kyau. falon ba tarkace sam abun shaā€™awa.

Goggo Hansatu tace.

ā€œSadiya hauro ki kwanta kinji. kuma ya kamata mu bar hirar nan haka nan gobe zaā€™a dā€™auki hanyar gida kuma.

koda na kwanta na kasa bacci sam. sai tunane tunane na ke yi. babu abunda ya fi tsaya mun sai zancan Auran Aliyu bayan dawowarshi da wata guda. idanu na lumshe a raina nace.

ā€œyau ni ce a tsakankanin masoya biyu na shigo rayuwarsu ba tare da sun shirya ba. na rusa musu duk abunda su ka jima su na tsarawa. Haka nima duk wani tanadi da tsara yanda zan gudanar da rayuwar aurena, da yanda zan gigita mijina da soyayyar da saina juya mishi kā€™wakā€™walwa, yanxu duk ya kau. Na auri dā€™an kā€™auye yaro kā€™arami.Da wanne idanunma zan iya mishi kallon miji.Ā  Shin yama rayuwar kā€™auyan zata kasancemun?

haka nai ta tunani. sai jefin asuba bacci yai awon gaba da ni.

WASHE GARI

Ā tun sassafe na yi wanka. sanye nake da shadda mai ruwan kā€™asa. dinkin riga da siket yasha surrani da milk colour dā€™in zare. dā€™inkin ya zauna a jikina sosai. kwalliya na yi mai tsari, jikina kuma sai tashin kamshi ya ke yi. takalmi ne mai tsini a kafata milk colour, haka ma mayafin jikina ya kasance milk. Goggo Hansatu tace.

ā€ su Hadiza su raka ki ku gaisa daĀ  ayagin surukarki da matan gida. kafin su dā€™au haramar tafiya kuma. dubanta na yi nace.

Goggo kema yau za ki tafi?

ā€œAā€™a Sadiya. zan zauna sai nan da kwana hudā€™u ranar da Aliyu zai dawo sai in tafi. a kā€™alla zan dā€™ebe miki kewa.

daā€™di naji sosai da jin bayanin Goggo.

fita mu ka yi da su Hadiza. mu na tafe ne nace.

Hadiza lallai Bashir yayi kokā€™ari daya barki ki ka zo bikina tun daga katsina. gaki har kauyenmu. dariya Hadiza ta yi tace.

ā€œHaba Sadiya ai muna tare. abinda na ke so dake shine. karki sake kallon rayuwar da ki ka gudanar ta baya. Sadiya abu guda mace take bukā€™ata a rayuwarta shine ta samu kulawa da tausayi a gidan mijinta. in gidan aure ya samu wannan toh magana ta kā€™are. ni shawarar da zan baki shine. ki kawo walwala da farin ciki gidan auranki. ki gaiyato haske da raha a zamanki da.Aliyu. ke wayayyace kinsan meye makamar dā€™a namiji. idan ki ka yi hakan zaki samu nutsuwar da sai kauyannan ya zame miki tamkar America.

kai na kadā€™a. maganarta gaskiya ne.

Hakane Hadiza zanyi kokarin hakan. amma wannan sai mun samu fahimtar juna tare da shi. kinsan yaro ne, dole alā€™amuran ba za su zo mun da saukā€™i ba. ni wallahi kunya ma nake ji.

Amina tace

ā€œshi namiji ba ya kadā€™an. ni mijina sai da na shekara dā€™aya a hannunshi ba muā€™amalar Aure. sai dai mu yi wasa da juna kawai. gaban na shi ashe ya na da matsala. sai da ga baya ne ya samu lafiya. amma ba wanda yasan wannan labarin sai ku da na sanar ma yau. shi namiji baā€™a shekaru bane. kar ki yi girman kai ki je ki shiga wuta a banza.ā€

hirar ta mu ta tsaya ne, a sakamakon isowa bā€™arayin su Goggo Asabe. da sallama mu ka shiga falon Goggo Asabe. duk yayyan Babana su na ciki, da alama tattaunawa su ke yi. gurfana mu ka yi a gabansu mu ka gaishesu da girmamawa. sun amsa a sake babu laifi. kawu Sulaiman yace.

ā€œSadiya. sai ki sake hakuri nan da kwana hudu mu ke sa ran Aliyu zai dawo. ki kula dan baza mu yadda da fitsara irin taku ta ā€˜yan boko ba ma su ido a tsakar ka. Aliyu kuma dole ki mai biyayya domun duk shekarunki da matsayinki kin dawo karkashin ikon shi ne. kar kuma ki ji wani iri. bayan wata guda da dawowarshi zaā€™a dā€™aura Auranshi. gyatumarki ma ta san da hakan. akwai dokoki da kā€™aā€™idoji akan ko wacce surukar gidannan. dan haka za ki iya samun Bilkisu. matar wan Aliyu ta yi miki bayanan daya dace.

A sanyaye na ce.

Toh kawu zan yi hakan in sha Allah.

Su Goggo Asabe a cikinsu ba wacce ta ce da mu uffan. sai daga baya Goggo Asabe tace.

ā€œToh ki koma dā€™akin ki. magana mu ke yi.

dole na kalato murmushi na dā€™aura ma fuskata nace.

Toh Goggo.

jiki a mace mu ka fito. mun dā€™an zazzaga cikin gidan Bilkisu ce tai mana jagora. tare da gabatar mun da surukan gidan. gaggaisawa mu ka yi da kowa. sai dai da dukkan alama ban samu karbā€™uwa ba sam a wajansu. Dan sai wani hararata suke yi, su nai mun kallon banza haka.

komawa mu ka yi bā€™angare na. Sallama muka soma jiyowa ta namiji a kā€™ofar bā€™arayina. Hadiza ce ta fita.

ā€œSannu baiwar Allah, kune kā€™awayen Amaryar tamu ko? Hadiza da dariya a fuskarta tace.

ā€œEh muneā€

Murmushi yayi yace.

ā€œSunana Kamilu, nine aminin Aliyu, tun jiya naso in zo dan mu gana da ku, toh sauran abokan namu suna waje, dama a game da sallamar kā€™ayawyene, bisa ga alā€™ada.ā€

Hadiza tace.

ā€œHakane, sai ku bayar da duk abunda ya sauwakā€™a, jiya ma baku kawo mana abinci baā€ kai Kamilu ya sosa.

ā€œEh ayi mana afuwa, sai yau na gama harhadā€™o kan abokan, Amma ga abun kari.ā€ Hannu tasa ta amsa, leda ce mai dā€™auke da gasassun zabi, sai robar fenti cike da tea, wanda sai da Kamilu ya fita zuwa cikin zamfara ya siyo kayan tean. nera dubu biyar ya mikā€™ama Hadizaā€

ā€œGa wannan ayi hakā€™uri, abun yazo mana babu shiri.ā€

ā€œAh babu komai mun godeā€ ciki Hadiza ta dawo ta kawo mana kayan kari, tare da yi mana bayanin yanda su ka yi da Kamilu. bayan sun gama karyawa, sun yi wanka. sai kuma su ka fito dan tafiya.

ina kuka mu ka rabu da su. tare da mun alā€™kawarin za su kewayo ni.

Goggo ce ta riā€™ke hannuna mu ka koma ciki. kan gado na fadā€™a ina ta kuka amma mara sauti.

wai wanne irin matsalolin zan fuskanta ne a wannan zaman Auran?

mrs Bukhari ce

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *