Rikon Kaka Chapter 6

Riqqon Kaka Chapter 3

RIKON KAKA

CHAPTER3

Kaka tace”Ba kowa, zaluncine kawai da kuma ba

ya qaunar . ki” Rukayyah tace “Ai nima shi yasa

bana Raunar sa, dama ya mutu

~ Kaka tace”Idan ya mutu ai muma da mun

mutu, don da Allah muka dogara da shi muka

dogara, idan ya mum jika ai sai munyi bara“

‘Rukayya ta diro daga kan gadoh ta , dauko kofi

ta zuba furar da kaka ta gama damawa, sannan

ta koma bakin gado ta soma sha. *

_ Kaka ta mike ta kuskure bakinta saboda kiran

sallar la’asar da aka fara a masallaci.

Misalin karfe biyar dai-dai taiwa Abubakar a Kofar

gida, a gajiye liqis ya dawo gidan tamkar Wanda

aka bawa kashi. Ya cire kayan jikinsa ya fito ya

:nufi kewayrn gidan ya watsa ruwa ya dawo

ya‘saka ‘yan Kananan kaya mararsa nauyi,

sannan ya fito tsakar gidan ya

nufi dakin kaka.

Tana kwance tana hutawar ta sai jika ce keta

faman * ‘ wasan kyallaye, tana ganin Abubakar

gabanta ya fadi, ta shiga faman raba idanuwa.

Abubakar ya tsaya bakin kofar dakin ya watsa

mata harara, kafin yace

“Naga ranar da zakiyu hankali, qatuwa dake kin

tile kina wasan kyalle. Mtsw! Allah wadaran naka

ya lalace’. .

Kaka tai saurin tashi zaune, “Ah! Ka dawo kcnan

k0, sarkin mita uban ‘yan iyayi?”

Ya cc, ”Ni ba mita nazo ki min ba’“.

Ya wurgawa Rukayya Naira hamsin, yace

“Tashi maza kiyo min cefane wurin Haladu in

dora sanwa, kuma saura idan kin tafi kije ki ta

neme-nemen fitina”.

Ya juya ya barsu ya nufi wurin murhu ya hada

itatuwa ya dora sanwar wake, sannan ya koma

dakinsa ya kunna kallo a wayar sa

Rukayya ta tafi siycn cefanen tanata faman

dirc~dircn ta a hanya, tana shawo kwanar

Rukayya ta rinqa krta musu dariya har tana

dukawa ta zub da sauran duwatsun ta nufi gida

tana tsallen murna.

Ta kawo masa cefanen dakinsa, a lokacin ta

tsaya daga bakin kofa.

“Ga cefanen”.

Yai kamar bai ji ta ba, sai da ta mai maita wurin

sau uku sannan ya mike yazo ya amsa tamkar

wanda ya rike wani abin kyama, yana binta da

kallon kyama

Duk tai dagaje-dagaje da ita, kayan nan duk

sunyi dauda, ita kanta fatar jikinta taji jiki. Har

zata wuce yace.

“Ke, zo nan.

Ta dawo, “Gani“.

Kamar ba zai tanka ba. can kuma ya dame ya ce

”Yaushe rabon da kiyi wanka?” Shiru ba amsa, ya

daka mata tsawa koba dake nake bane

Tace; “Nima na manta

Abubakar ya girgixa kai wuce kije ki ciro kayan

jikin da sauran

daudar ki kawo min a bakin maguji, kije ki debi

ruwa kiyi wanka, sakarya, qazamar Wofi. Wuce ki

tafi

Da hanzarintata wuce, .ya rufa mata baya. Haka

kawaiyake jin tsanar yarinyar a. ransa saboda

qazantar ta da kuma‘ kin jinta kamar _ wadda

aka kadawa da ruwan sanyi. ., ’

Ya wanke cefanen ya zuba a turmi yana

jajjagawa, Rukayya ta debo kayan ta kai masa a

bakin maguji ta ajiye masa tuli guda, sannanta

debi ruwa a bokiti ta nufi kewaye tai wanka, ta

wuce daki. ‘

Kaka ta cc, “Da yake shi ne ai gashi nan kinyi

wankan,anfi sati ina matsa miki da kiyi wankan

amman kin kiya sbd kin rainani

Rukayya ta xumBuro baki, ta janyo jakar kayanta

ta fito da wata cukurkudaddiyar

doguwar riga ta saka, bata shafa mai ba balle

hoda, tai zamanta abinta.

‘ K0 kadan Rukayya bata son kwalliya,

Bata ma damu da tsaftar jikinta ba ballantana

wata kwalliya. .

Kaka tace, “Ki dauko k0 mai :neki murza Jika, kin

zauna da jiki haka furu-furu”.

Ta zumBuro baki tai kwanciyar ta hankalin ta a

kwance

Abubakar yai jalof din shinkafa da wake,

yana kammala sallar magariba ya filo ya ,dibi

nashi ‘abincin ya kwashe masu sauran ya kai

masu sannan ya wuce dakinsa. Washe gari .

tunda sanyin safiya Abubakar ya gama jidar ruwa

sannan ya ta da Rukayya ta nemo masa tsari, ta

zunguro baki‘ alamar bata so ba, ta dauki bokitin.

Abubakar na kallonta cike da takaici, ya. danne

zuciyar sa ya kyale ta. “

Gida biyu ta shiga ta samo tsarin ta nufo ~gida,

tana cikin tafiya ta hadu da Zulai da Rakiya, bata

kula su ba saboda tsarin da ta debo. Abokanen

fadanta ne sosai suma ‘yan neman rigima ne

Zulai ta bangaje ta har bukitin tsarin ya fado

daga kanta ya zube bokitin ya fashe.

Rukayya ta ce, “Kaikai! Ni ku ka fasawa bokiti?

Wallahi ba zan yarda ba

Sukace “An zubar, k0 akwai abinda za kiyi?“

Ba ta tsaya mai da masu magana ba ta cakumi

Zulai da kokawa, ta yarbar da ita a cikin tsarin

tana duka, ganin haka yasa Rakiya ta shiga

dukan Rukayya, suka tararmata su biyu, sai da

Allah Ya kawo wani mutum sannan ya raba su.

‘ Rukayya ta dauki fashasshen bokitin tsarin ta

nufi gida tana kuka, Abukabar na ‘shara a tsakar

gida yaji kukan ta, ya mike da tsinsiya a hannun

sa yana jiran shigowar ta.

Bai ,yi mamakin ganinta da fashasshen bokiti ba,

jikinta duk tsari da qasa. Wani irin bakin ciki ya

turnike mashi zuciya, yai tsaye yana kallonta. Ta

kasa motsawa daga inda take,

tai tsaye tana rera masa kuka. Kaka tai saurin

hankado labule

tana fadan ‘ ”Mugu, dukan nata din kake k0?

Indai ka

kashe ta Habu ka huta

Ganinta da tayi tsaye da tsari duk jikinta yasa tai

saurin nufarta tana fadar. ‘

Jika, wane la’anannen ne yai miki haka? Lahaula

wala quwata, kashe ki ake so ayi ne Jika? Wai

me ki kaiwa mutane ne yasa basa kaunar ki?”

Sai tasa kuka har da hawayen ta, cikin kuka tace

Waye yai miki haka Jika?” Rukayya ta ce, ”Su

Rakiya ne da Zulai’. * Kaka ta ce, ”Ai ko yau sai

na rama miki, don wallahi basu bugi banza ba”.

Abubakar ya qaraso yana fadar, ”Allah Yasa kije

su hada da ke ai ni zuciyata fari ta Allah Ya qara,

ai da ana miki haka da kin rage wani iskancin da

kike wa jama’a”. Kaka ta ce ”Tunda dama ba

tausayine dakaiba Ai idan sun kashcta baka da

asara, ai ni nasan ba qaunar mu kakc ba”dama.

Ta juya ta janyo zani ta yafa ta nufi hanyar fita,

Abubakar ya ce ‘ ‘ “Ina zaki kuma?”

“Zuwa zanyi in ramo mata tunda

Kai baka da amfani. Na lura ai na lura matsoracin

, banza nekai, baka da fushi sai cikin gida”,

Tayi waje tana mita ganin, bai ce mata Kala ba

har ta fice. Ya dubi Rukayya dake kokarin binta,

ya daka mata tsawa

“Karki kuskura , munafukar banza, duk wata

masifa ke ke haddasa ta, kinja ana ta zagar

mana kaka, kuma duk saboda ke. In bacin keda

kr debo mana rigima da wa ma yasan damu?

Masifaffiyar yarinya kawai.

Sai ki wuce kije ki cire kayan kiyi wanka ki canza

wasu, aike ne tunda baki so daga yau an gama

aikcn ki, sai ki zauna”, Ya watsa mata harara ya

wuce abinsa. .

Ta wuce simi-simi ta dauko zani ta debi ruwa ta

nufi krwaye tai wanka, ta dauro zanin ’ ta ajiye

mashi masu tsarin a bakin maguji, ta wuce daki

ta canza‘ wasu kayan. Sai dai babu mai ba

kwalli, haka aka sa kayan ta kama tai kwanciyar

ta saman gudo.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *